1

1 Urushalima wadda take cike da mutane a dā, Yanzu tana zaman kaɗaici! Tana zama kamar mace wadda mijinta ya rasu, Ita wadda dā ta zama babba a cikin sauran al'ummai! Ita wadda take a dā sarauniya a cikin larduna, Ta zama mai biyan gandu!

2 Da dare tana kuka mai zafi, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf a kumatunta. Dukan masoyanta ba wanda yake ta'azantar da ita. Dukan abokanta sun ci amanarta, sun zama maƙiyanta.

3 Yahuza ta tafi bauta tana shan azaba, Da bauta mai tsanani. Tana zaune a tsakiyar sauran al'umma, Amma ba ta sami hutawa ba, Gama masu runtumarta sun ci mata, ba hanyar tsira.

4 Hanyoyin Sihiyona suna baƙin ciki Domin ba mai halartar ƙayyadaddun idodi. Dukan ƙofofinta sun zama kufai, Firistocinta suna nishi, Budurwanta kuma suna wahala, Ita kanta ma tana shan wuya ƙwarai.

5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta, Abokan gābanta kuma sun zama iyayengijinta. Gama Ubangiji ne ya sa ta sha wahala Saboda yawan zunubanta. 'Ya'yanta sun tafi bauta wurin maƙiyanta.

6 Dukan darajar Sihiyona ta rabu da ita, Shugabanninta sun zama kamar bareyin Da ba su sami wurin kiwo ba, Suna gudu ba ƙarfi a gaban wanda yake korarsu.

7 A kwanakin wahalarta na rashin wurin zama, Urushalima ta tuna da dukan abubuwanta masu daraja a dā. A lokacin da mutanenta suka fāɗa a hannun maƙiyi, Ba wanda ya taimake ta, Maƙiyanta sun gan ta, Sun yi mata ba'a saboda fāɗuwarta.

8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai da gaske, Saboda haka ta ƙazantu, Dukan waɗanda suka girmama ta sun raina ta Domin sun ga tsiraicinta, Ita kanta ma tana nishi, ta ba da baya.

9 Ƙazantarta tana cikin tufafinta, Ba ta tuna da ƙarshenta ba, Domin haka faɗuwarta abar tsoro ce, Ba ta da mai yi mata ta'aziyya. “Ya Ubangiji, ka dubi wahalata, Gama maƙiyi ya ɗaukaka kansa!”

10 Maƙiyi ya miƙa hannunsa A kan dukan kayanta masu daraja, Gama ta ga al'ummai sun shiga Haikali, Su waɗanda ka hana su shiga cikin jama'arka.

11 Dukan jama'arta suna nishi don neman abinci, Sun ba da kayansu masu daraja saboda abinci Don su rayu. “Ya Ubangiji ka duba, ka gani, Gama an raina ni.”

12 “Dukanku masu wucewa, ba wani abu ba ne a gare ku? Ku duba, ku gani, ko akwai baƙin ciki irin nawa, Wanda Ubangiji ya ɗora mini, A ranar fushinsa mai zafi.

13 “Daga sama ya aukar da wuta a cikin ƙasusuwana. Ya kuma kafa wa ƙafafuna ashibta, Ya komar da ni baya, Ya bar ni a yashe, sumamme dukan yini.

14 “Ubangiji ya tattara laifofina Ya yi karkiya da su, Ya ɗaura su a wuyana, Ya sa ƙarfina ya kāsa. Ya kuma bashe ni a hannun Waɗanda ban iya kome da su ba.

15 “Ubangiji ya yi watsi da majiya ƙarfina, Ya kirawo taron jama'a a kaina Don su murƙushe samarina. Ya kuma tattake Urushalima, zaɓaɓɓiyarsa, Kamar 'ya'yan inabi a wurin matsewa.

16 “Ina kuka saboda waɗannan abubuwa, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf daga idanuna. Gama mai ta'azantar da ni, Wanda zai sa in murmure yana nesa da ni. 'Ya'yana sun lalace, Gama maƙiyi ya yi nasara!”

17 Sihiyona tana miƙa hannuwanta, Amma ba wanda zai ta'azantar da ita. Gama Ubangiji ya umarci maƙwabtan Yakubu su zama maƙiyansa. Urushalima kuma ta zama ƙazantacciya a tsakaninsu.

18 “Abin da Ubangiji ya yi daidai ne, Gama ni na ƙi bin maganarsa, Ku ji, ya ku jama'a duka, Ku dubi wahalata, 'Yan matana da samarina, An kai su bauta!

19 “Na kira masoyana, amma suka yaudare ni, Firistocina da dattawana a cikin birni sun hallaka Saboda neman abincin da za su ci su rayu.

20 “Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala, Raina yana cikin damuwa, Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata. A titi takobi yana karkashewa, A gida kuma ga mutuwa.

21 “Sun ji yadda nake nishi, Ba mai ta'azantar da ni. Dukan maƙiyana sun ji labarin wahalar da nake ciki, Suna kuwa murna da ka yi haka. Ka kawo ranan nan da ka ambata, Domin su ma su zama kamar yadda nake.

22 “Ka sa mugayen ayyukansu su bayyana a gabanka, Sa'an nan ka hukunta su kamar yadda ka hukunta ni saboda dukan laifofina. Gama nishe-nishena sun yi yawa. Zuciyata kuma ta karai.”

2

1 Ubangiji ya duhunta Sihiyona saboda fushinsa! Daga Sama kuma ya jefar da darajar Isra'ila a ƙasa. Bai kuma tuna da matashin sawayensa ba A ranar fushinsa.

2 Dukan wuraren zaman Yakubu, Ubangiji ya hallakar ba tausayi, Da fushinsa kuma ya rurrushe kagaran Sihiyona. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulkin.

3 Da zafin fushinsa, ya karya ƙarfin Isra'ila, Ya kuma bar yi musu taimako A lokacin da abokan gāba suka zo. Kamar harshen wuta, ya ƙone dukan abin da yake na Yakubu.

4 Ya ja bakansa kamar abokan gāba, Ya kuma nuna ikonsa kamar maƙiyi. Ya hallaka dukan abin da yake da bansha'awa. A alfarwar Sihiyona, ya zubo da hasalarsa kamar wuta.

5 Ubangiji ya zama kamar maƙiyi, ya hallaka Isra'ila. Ya hallaka fādodinta duka, Ya mai da kagaranta kango. Ya aukar wa Yahuza da makoki da baƙin ciki mai yawa.

6 Ya rushe Haikalinsa kamar bukka cikin gona, Ya mai da wurin yin ƙayyadaddun idodinsa kufai. Ubangiji ya sa ƙayyadadden idi da kiyaye Asabar Su ƙare a Sihiyona, Da zafin fushinsa kuma ya wofinta sarki da firist.

7 Ubangiji ya wulakanta bagadensa, Ya kuma wofinta tsattsarkan Haikalinsa. Ya ba da garun fādodinta a hannun abokan gāba, Suka yi sowa a Haikalin Ubangiji Kamar a ranar idi.

8 Ubangiji ya yi niyya Ya mai da garun Sihiyona kufai, Ya auna ta da igiyar awo, Bai janye dantsensa daga hallaka ta ba. Ya sa kagara da garu su zozaye, su lalace tare.

9 Ƙofofinta sun nutse ƙasa, Ya lalatar, ya kakkarya ƙyamarenta, An kai sarkinta da mahukuntanta cikin al'ummai, Inda ba a bin dokokin annabawanta, Ba su kuma samun wahayi daga wurin Ubangiji.

10 Dattawan Sihiyona suna zaune a ƙasa shiru, Sun yi hurwa, suna saye da tufafin makoki. 'Yan matan Urushalima kuma sun sunkuyar da kansu ƙasa.

11 Idanuna sun dushe saboda kuka, Raina yana cikin damuwa. Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena, Gama 'yan yara da masu shan mama Sun suma a titunan birnin.

12 Suna yi wa uwayensu kuka, suna cewa, “Ina abinci da ruwan inabi?” Suna suma kamar mutanen da aka yi wa rauni A titunan birnin, Suna mutuwa a ƙirjin uwayensu.

13 Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ya Urushalima? Da me zan misalta wahalarki Don in ta'azantar da ke, ya Sihiyona? Masifar da ta same ki tana da fāɗi kamar teku, Wa zai iya warkar da ke?

14 Annabawanki sun gano miki wahayan ƙarya, Ba su tone asirin muguntarki, Har da za a komo da ke daga bauta ba. Amma suka yi miki annabcin ƙarya na banza.

15 Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini. Suna yi wa Urushalima tsāki, Suna kaɗa mata kai, suna cewa, “Ai, Urushalima ke nan, Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali, Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”

16 Maƙiyanki duka sun wage bakinsu gāba da ke, Suna tsāki, suna cizon bakinsu, Suna ihu, suna cewa, “Mun hallaka ta! Ai, wannan ita ce ranar da muke fata! Ga shi kuwa, ta zo, mun gan ta!”

17 Ubangiji ya aikata abin da ya yi niyya, Ya cika maganarsa wadda ya faɗa tun dā, Ya hallakar, ba tausayi, Ya sa maƙiyi ya yi murna a kanki, Ya ƙarfafa ƙarfin maƙiyanki.

18 Ya Sihiyona, ki yi kuka ga Ubangiji, Bari hawayenki su gudana dare da rana kamar ruwan rafi, Kada ki huta, kada kuma idanunki su huta!

19 Ki tashi, ki ya ta kuka dukan dare, Ki bulbule abin da yake cikin zuciyarki Kamar ruwa gaban Ubangiji. Ki miƙa hannuwanki zuwa gare shi, Saboda rayukan 'ya'yanki, Waɗanda suke suma da yunwa A magamin kowane titi!

20 Ya Ubangiji, ka duba, ka gani! Wane ne ka yi wa haka? Mata za su cinye 'ya'yansu da suke reno? Ko kuwa za a kashe firist da annabi A cikin Haikalin Ubangiji?

21 Yara da tsofaffi suna kwance cikin ƙurar tituna, An kashe 'ya'yana, 'yan mata da samari, da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka, ba tausayi.

22 Ka gayyato mini tsoro Kamar yadda akan gayyato taro a ranar idi. A ranar fushin Ubangiji Ba wanda ya tsere, ko wanda ya tsira. 'Ya'yan da na yi renonsu, na goye su, Maƙiyina ya hallaka su.

3

1 Ni ne mutumin da ya sha wuyar horon Ubangiji.

2 Ya kore ni zuwa cikin duhu baƙi ƙirin.

3 Hakika ikonsa ya yi ta gāba da ni dukan yini.

4 Ya sa naman jikina da fatar jikina su lalace, Ya kuma kakkarya ƙasusuwana.

5 Ya kewaye ni da yaƙi, Ya rufe ni da baƙin ciki mai tsanani da wahala.

6 Ya zaunar da ni cikin duhu, Kamar waɗanda suka daɗe da mutuwa.

7 Ya kewaye ni da garu don kada in tsere, Ya ɗaure ni da sarƙa mai nauyi.

8 Ko da yake ina kira, ina kukan neman taimako, Ya yi watsi da addu'ata.

9 Ya toshe hanyata da sassaƙaƙƙun duwatsu, Ya karkatar da hanyoyina.

10 Ya zamar mini kamar beyar wanda yake fako, Kamar zaki a ɓoye cikin ruƙuƙi.

11 Ya bauɗar da ni daga hanyata, ya yayyage ni, Ya maishe ni, ba ni a kowa.

12 Ya ja bakansa, ya sa in zama abin baratarsa.

13 Ya harbe zuciyata da kiban kwarinsa.

14 Na zama abin dariya ga dukan mutane, Dukan yini suna yi mini waƙar zambo.

15 Ya shayar da ni da ruwan ɗaci, Ya ƙosar da ni da abinci mai ɗaci.

16 Ya sa in tauna tsakuwa da haƙorana, Ya zaunar da ni cikin ƙura.

17 An raba ni da salama, Na manta da abar da ake ce da ita wadata.

18 Sai na ce, “Darajata ta ƙare, Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.”

19 Ka tuna da azabata, da galabaitata, Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi.

20 Kullum raina yana tunanin azabaina, Raina kuwa ya karai.

21 Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba.

22 Ƙaunar Ubangiji ba ta ƙarewa, Haka kuma jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.

23 Su sababbi ne kowace safiya, Amincinka kuma mai girma ne.

24 Na ce, “Ubangiji shi ne nawa, Saboda haka zan sa zuciya gare shi.”

25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke sauraronsa, Da wanda suke nemansa kuma.

26 Yana da kyau a jira ceton Ubangiji da natsuwa,

27 Yana da kyau mutum ya hori kansa tun yana yaro.

28 Bari ya zauna a kaɗaice, ya yi shiru Sa'ad da yake da damuwa.

29 Bari ya kwanta cikin ƙura, Watakila akwai sauran sa zuciya.

30 Bari ya yarda a mari kumatunsa, Ya haƙura da cin mutunci.

31 Gama Ubangiji ba zai yashe mu har abada ba.

32 Ko da ya sa ɓacin rai, Zai ji tausayi kuma, Saboda tabbatacciyar ƙaunarsa mai yawa.

33 Gama ba da gangan ba ne yakan wahalar da 'yan adam Ko ya sa su baƙin ciki.

34 Ubangiji bai yarda a danne 'Yan kurkuku na duniya ba.

35 Bai kuma yarda a hana wa mutum hakkinsa A gaban Maɗaukaki ba,

36 Ko kuwa a karkatar wa mutum da shari'arsa.

37 Wa ya umarta, abin kuwa ya faru, In ba Ubangiji ne ya umarta ba?

38 Ba daga bakin Maɗaukaki Alheri da mugunta suke fitowa ne ba?

39 Don me ɗan adam Zai yi gunaguni a kan hukuncin zunubansa?

40 Bari mu jarraba, mu bincika hanyoyinmu, Sa'an nan mu komo wurin Ubangiji.

41 Bari mu roƙi Allah na Sama, Muna miƙa hannuwanmu sama, mu ce,

42 “Mun yi zunubi, mun tayar, Kai kuwa ba ka gafarta ba.

43 “Ka yafa fushi, ka runtume mu, Kana karkashe mu ba tausayi.

44 Ka kuma rufe kanka da gajimare Don kada addu'a ta kai wurinka.

45 Ka maishe mu shara da juji a cikin mutane.

46 “Dukan maƙiyanmu suna yi mana ba'a.

47 Tsoro, da wushefe, Da lalatarwa, da hallakarwa sun auka mana.

48 Hawaye suna gangarawa daga idanuna kamar ruwan koguna, Saboda an hallaka mutanena.

49 “Hawayena suna ta gangarawa, ba tsayawa, ba hutawa,

50 Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani.

51 Ganin azabar 'yan matan birnina Ya sa ni baƙin ciki.

52 “Waɗanda suke maƙiyana ba dalili Sun farauce ni kamar tsuntsu.

53 Sun jefa ni da rai a cikin rami, Suka rufe ni da duwatsu.

54 Ruwa ya sha kaina, Sai na ce, ‘Na halaka.’

55 “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunanka Daga cikin rami mai zurfi.

56 Ka kuwa ji muryata. Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.

57 Sa'ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa. Sa'an nan ka ce mini kada in ji tsoro.

58 “Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji, Ka kuwa fanshi raina.

59 Ka ga laifin da aka yi mini, Sai ka shara'anta da'awata, ya Ubangiji.

60 Ka ga dukan irin sakayyarsu, Da dukan dabarun da suke yi mini.

61 “Ya Ubangiji, ka ji zargi Da dukan dabarun da suke yi mini.

62 Leɓunan maƙiyana da tunaninsu Suna gāba da ni dukan yini.

63 Suna raira mini waƙar zambo sa'ad da suke zaune, Da lokacin da suka tashi.

64 “Ya Ubangiji, za ka sāka musu bisa ga ayyukansu,

65 Za ka ba su tattaurar zuciya, La'anarka kuwa za ta zauna a kansu!

66 Da fushi za ka runtume su Har ka hallaka su a duniya, ya Ubangiji!”

4

1 Ƙaƙa zinariya ta zama duhu! Ƙaƙa zinariya tsantsa ta sāke! Tsarkakakkun duwatsu kuma suna zube A kowane magamin titi.

2 Darajar samarin Sihiyona Ta kai tamanin zinariya tsantsa. To, ƙaƙa ake lissafinsu kamar tukwanen ƙasa, Aikin hannun maginin tukwane?

3 Ko diloli ma sukan ba 'ya'yansu mama, Su shayar da su. Amma mutanena sun zama kamar jiminai cikin jeji.

4 Harshen jinjiri ya liƙe a dasashinsa saboda ƙishi, 'Yan yara suna roƙon abinci, Amma ba wanda ya ba su.

5 Su waɗanda suka ci abubuwa masu daɗi, Sun halaka a titi. Su waɗanda aka goye su da alharini, Yanzu suna kwance a kan tsibin toka.

6 Gama zunubin mutanena Ya fi zunubin Saduma, Wadda Ubangiji ya hallakar da ita nan da nan.

7 Keɓaɓɓunta sun fi dusar ƙanƙara tsabta, Sun kuma fi madara fari. Jikunansu sun fi murjani ja. Kyan tsarinsu yana kama da shuɗin yakutu.

8 Yanzu fuskokinsu sun fi kukunniya baƙi, Ba a iya fisshe su a titi ba, Fatar jikinsu ta liƙe wa ƙasusuwansu, Sun bushe kamar itace.

9 Gara ma waɗanda takobi ya kashe Da waɗanda yunwa ta kashe, Gama sun rame sarai saboda rashin abinci.

10 Mata masu juyayi, da hannuwansu Suka ɗauki 'ya'yansu, suka dafa, Suka zama musu abinci a lokacin halakar mutanena.

11 Ubangiji ya saki fushinsa, Ya zuba fushinsa mai zafi. Ya kunna wa Sihiyona wuta Wadda ta cinye harsashin gininta.

12 Sarakunan duniya da mazaunanta ba su gaskata, Cewa abokan gaba ko maƙiya Za su iya shiga ƙofofin Urushalima ba.

13 Dalili kuwa saboda zunuban annabawa ne, Da muguntar firistoci, Waɗanda suka kashe adalai.

14 Sun yi ta kai da kawowa a titi kamar makafi, Sun ƙazantu da jini Har ba wanda zai taɓa rigunansu.

15 Mutane suka yi ta yi musu ihu, Suna cewa, “Ku tafi, ku ƙazamai, Ku tafi, ku tafi, kada ku taɓa mu!” Don haka suka zama korarru, masu kai da kawowa. A cikin sauran al'umma mutane suna cewa, “Ba za su ƙara zama tare da mu ba.”

16 Ubangiji kansa ya watsar da su, Ba zai ƙara kulawa da su ba. Ba su darajanta firistoci ba, Ba su kuma kula da dattawa ba.

17 Idanunmu sun gaji Da zuba ido a banza don samun taimako, Mun zuba ido Ga al'ummar da ba za ta iya cetonmu ba.

18 Ana bin sawayenmu, Don haka ba mu iya tafiya a titunanmu ba. Ƙarshenmu ya yi kusa, Kwanakinmu sun ƙare, Gama ƙarshenmu ya zo.

19 Masu runtumarmu sun fi gaggafar da take tashi sama sauri. Sun fafare mu a kan duwatsu, Suna fakonmu a cikin jeji.

20 Shi wanda muke dogara gare shi, Wato zaɓaɓɓe na Ubangiji, ya auka cikin raminsu, Shi wanda muka ce, “A ƙarƙashin inuwarsa ne za mu zauna a cikin sauran al'umma.”

21 Ki yi farin ciki, ki yi murna, ke Edom, Wadda kike zaune cikin ƙasar Uz. Amma fa za a ba ki ƙoƙo ki sha, Ki bugu har ki yi tsiraici.

22 Ya Sihiyona, hukunci a kan muguntarki ya ƙare, Ba zai ƙara barinki a ƙasar bauta ba. Amma zai hukunta ki saboda muguntarki, ya Edom, Zai tone zunubanki.

5

1 Ya Ubangiji, ka tuna da abin da ya same mu. Ka duba, ka ga yadda muka zama abin kunya!

2 An ba baƙi gādonmu, Gidajenmu kuwa an ba bare.

3 Mun zama marayu, marasa ubanni, Uwayenmu sun zama kamar matan da mazajensu sun mutu.

4 Dole ne mu biya ruwan da za mu sha, Dole ne kuma mu sayi itace.

5 Masu binmu a ƙyeyarmu suke, suna korarmu da zafi, Mun gaji, ba a yarda mu huta.

6 Mun miƙa hannu ga Masar da Assuriya Don mu sami abinci.

7 Ubanninmu sun yi zunubi, ga shi kuwa, ba su, Mu kuwa muna ɗaukar alhakin muguntarsu.

8 Bayi suke mulkinmu, Ba kuwa wanda zai cece mu daga hannunsu.

9 Sai mun yi kasai da ranmu kafin mu sami abinci, Domin akwai masu kisa a jeji.

10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, Saboda tsananin yunwa.

11 An yi wa mata faɗe a cikin Sihiyona, Haka kuma aka yi wa budurwai a garuruwan Yahuza.

12 An rataye shugabanni da hannuwansu, Ba a kuma girmama dattawa ba.

13 An tilasta wa samari su yi niƙa, Yara kuma suna tagataga da kayan itace.

14 Tsofaffi sun daina zama a dandalin ƙofar birni, Samari kuma sun daina bushe-bushe.

15 Farin cikinmu ya ƙare, Raye-rayenmu sun zama makoki.

16 Rawani ya fāɗi daga kanmu, Tamu tu ƙare, gama mun yi zunubi!

17 Saboda wannan zuciyarmu ta ɓaci, Idanunmu kuma suka duhunta.

18 Gama Dutsen Sihiyona ya zama kufai, Wurin yawon diloli.

19 Amma ya Ubangiji, kai ne kake mulki har abada, Kursiyinka ya dawwama har dukan zamanai.

20 Don me ka manta da mu har abada? Don me ka yashe mu da daɗewa haka?

21 Ya Ubangiji, ka komo da mu zuwa gare ka! Mu kuwa za mu koma. Ka sabunta kwanakinmu su zama kamar na dā.

22 Ko ka ƙi mu ne, sam sam? Ko kuwa ka husata da mu?