1 Albarka ta tabbata ga mutumin da Ba ya karɓar shawarar mugaye, Wanda ba ya bin al'amuran masu zunubi, Ko ya haɗa kai da masu wasa da Allah.
2 Maimakon haka, yana jin daɗin karanta shari'ar Allah, Yana ta nazarinta dare da rana.
3 Yana kama da itacen da yake a gefen ƙorama, Yakan ba da 'ya'ya a kan kari, Ganyayensa ba sa yin yaushi, Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi.
4 Amma mugaye ba haka suke ba, Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa.
5 Allah kuwa zai hukunta mugaye, Masu zunubi kuwa za a ware su daga adalai.
6 Gama Ubangiji yana lura da al'amuran adalai, Amma al'amuran mugaye za su watse.
1 Don me al'ummai suke shirin tayarwa? Don me waɗannan mutane suke ƙulla shawarwarin banza?
2 Sarakunan duniya sun yi tayarwa, Masu mulkinsu suna shirya maƙarƙashiya tare, Gāba da Ubangiji da zaɓaɓɓen sarkinsa.
3 Suna cewa, “Bari mu 'yantar da kanmu daga mulkinsu, Bari mu fice daga ƙarƙashinsu!”
4 Ubangiji ya yi dariya daga kan kursiyinsa can Sama, Ya mai da su abin dariya.
5 Ya yi musu magana da fushi, Ya razanar da su da hasalarsa,
6 Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka, Na naɗa sarkina.”
7 Sarkin ya ce, “Zan yi shelar abin da Ubangiji ya hurta. Ubangiji ya ce mini, ‘Kai ɗana ne, Yau ne na zama mahaifinka.
8 Ka yi roƙo, zan kuwa ba ka dukan al'ummai, Dukan duniya kuma za ta zama taka.
9 Za ka mallake su da sandan ƙarfe, Za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu.’ ”
10 Yanzu ku kasa kunne gare ni, ku sarakuna, Ku mai da hankali, ku mahukunta!
11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro, Ku yi rawar jiki, ku rusuna masa,
12 Ku yi mubaya'a da Ɗan, Idan kuwa ba haka ba zai yi fushi da ku, za ku kuwa mutu, Gama yakan yi fushi da sauri. Albarka ta tabbata ga dukan masu zuwa gare shi neman mafaka!
1 Ina da maƙiya da yawa, ya Ubangiji, Da yawa kuma sun juya, suna gāba da ni!
2 Suna magana a kaina, suna cewa, “Allah ba zai taimake shi ba!”
3 Amma kai, ya Ubangiji, kullum kana kiyaye ni daga hatsari, Kana ba ni nasara, Kana kuma maido mini da ƙarfin halina.
4 Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako, Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa.
5 Na kwanta na yi barci, Na kuwa tashi lafiya lau, Gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 Ba na jin tsoron dubban abokan gāba Waɗanda suka kewaye ni ta kowane gefe.
7 Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana, Ka hallakar da dukan mugaye.
8 Ceto yana zuwa daga wurin Ubangiji, Bari yă sa wa jama'arsa albarka!
1 Ka amsa mini sa'ad da na yi kira, Ya Allah, madogarata! Lokacin da nake shan wahala, ka zama mai taimakona. Ka yi mini alheri, ka kuma saurari addu'ata!
2 Ku mutanen nan, sai yaushe za ku daina zagina? Sai yaushe za ku daina ƙaunar abubuwan banza, Da bin abin da yake na ƙarya?
3 Ku tuna fa, Ubangiji ne ya zaɓe ni domin in zama nasa, Ya kuma ji ni lokacin da na yi kira gare shi.
4 Ku ji tsoro, ku daina aikata zunubinku, Ku yi tunani da gaske a kan wannan A kaɗaice, shiru, a ɗakunanku.
5 Ku miƙa wa Ubangiji hadayun da suka dace, Ku kuma dogara gare shi.
6 Akwai mutane da yawa da suke cewa, “Da ma a sa mana albarka!” Ka dube mu da alheri, ya Ubangiji!
7 Farin cikin da ka ba ni mai yawa ne, Fiye da na waɗanda suke da wadataccen hatsi da ruwan inabi.
8 Da zarar na kwanta, sai barci ya kwashe ni, Kai kaɗai kake kiyaye ni sosai, ya Ubangiji.
1 Ka kasa kunne ga kalmomina, ya Ubangiji, Ka kuma ji ajiyar zuciyata.
2 Ya Sarkina, Allahna, Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako.
3 A gare ka zan yi addu'a, ya Ubangiji, Da safe za ka ji muryata, Da hantsi zan yi addu'ata, In kuma jira amsa.
4 Kai ba Allah mai yarda da aikin kuskure ba ne, Ba ka yarda da mugunta a gabanka.
5 Ba ka jurewa da ganin mutane masu fāriya, Kana ƙin mugaye.
6 Kakan hallakar da duk maƙaryata, Kakan raina masu ta da hankali da masu ruɗi.
7 Amma ni, ina iya zuwa wurinka, Saboda ƙaunarka mai girma, In yi sujada a tsattsarkan Haikalinka, In kuma rusuna maka da bangirma.
8 Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji, Ka bi da ni in aikata nufinka, Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta!
9 Abin da maƙiyana ke faɗa, Ba abin da za a yarda da shi ba ne, Su dai, so suke su hallakar kawai, Bakinsu kamar buɗaɗɗen kabari yake, Maganganunsu kuwa suna da taushi da kuma yaudara.
10 Ka kāshe su, ka hukunta su, ya Allah Ka watsar da mugayen shirye-shiryensu, Ka kore su daga gabanka sabili da yawan zunubansu, Da kuma tayarwar da suke yi maka.
11 Duk waɗanda suka fake gare ka za su yi farin ciki, Kullum za su yi ta raira waƙa domin murna. Kana kiyaye waɗanda suke ƙaunarka, Suna kuwa matuƙar murna saboda kai.
12 Ka sa wa masu yi maka biyayya albarka, ya Ubangiji, Alherinka yana kāre su kamar gārkuwa.
1 Ya Ubangiji, kada ka yi fushi, ka kuma tsauta mini! Kada ka hukunta ni da fushinka!
2 Ka ji tausayina, gama na gaji tiƙis, Ka wartsarkar da ni, gama na tafke sarai.
3 Duk na damu ƙwarai da gaske. Sai yaushe wannan zai ƙare, ya Ubangiji?
4 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni, Gama kana ƙaunata, ka kuɓutar da ni daga mutuwa.
5 Ba za a tuna da kai a lahira ba, Ba wanda zai yabe ka a can!
6 Na gaji tiƙis saboda baƙin ciki, Kowane dare gadona yakan jiƙe saboda kukana. Matashin kaina ya yi sharkaf da hawaye.
7 Idanuna sun yi kumburi saboda yawan kuka, Har da ƙyar nake iya gani, Duk kuwa saboda abokan gābana!
8 Ku tafi daga nan, ku masu aikin mugunta! Ubangiji yana jin kukana.
9 Yana kasa kunne ga kukana na neman taimako, Yana kuwa amsa addu'o'ina.
10 Abokan gābana duka za su sha kunyar fāɗuwarsu, Suna cikin matsanancin ruɗami, Za a kwashe su farat ɗaya.
1 Ya Ubangiji, Allahna, na sami mafaka a wurinka, Ka cece ni, ka tserar da ni daga dukan masu fafarata,
2 Idan ba haka ba kuwa, za su ɗauke ni, Su tafi da ni zuwa wurin da ba wanda zai cece ni, A can za su yayyage ni kamar zaki.
3 Ya Ubangiji, Allahna, idan na aikata ɗaya daga cikin waɗannan, Wato idan na yi wa wani laifi,
4 Idan na ci amanar abokina, Ko kuwa in na gwada wa maƙiyi fin ƙarfi ba dalili,
5 To, bari abokan gābana su fafare ni, su kama ni, Bari su datse ni har ƙasa, su kuma kashe ni, Su bar ni ƙasa, matacce!
6 Ka tashi da fushinka, ya Ubangiji, Ka kuma tashi ka yi gāba da hasalar abokan gābana! Ka tashi, ka taimake ni, gama adalci kake so a yi.
7 Ka tattaro dukan kabilun da suke kewaye da kai, Ka yi mulki a kansu daga Sama.
8 Ya Ubangiji, kai ne alƙalin dukan mutane. Ka shara'anta mini bisa ga adalcina, Gama ba ni da laifi, ina kuma da kirki.
9 Ka tsai da muguntar mugaye, Ina roƙonka, ka sāka wa mutanen kirki. Kai Allah mai adalci ne, Kana kuwa auna tunanin mutane, da marmarinsu.
10 Allah ne mai kiyaye ni, Yakan ceci waɗanda suke yi masa biyayya.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Kullum kuwa yana kā da mugaye.
12 Idan mutane ba su tuba ba, Allah zai wasa takobinsa,
13 Zai ɗana bakansa ya shirya shi, Zai ɗauki makamansa masu dafi, Ya kuma auna kibansa masu wuta.
14 Ka duba, yadda mugu yake tunanin mugunta a ransa, Yana shisshirya wahala, yana kuma aikata ruɗi.
15 Yana haƙa rami mai zurfi a ƙasa, Sa'an nan yă fāɗa ramin da ya haƙa!
16 Saboda haka muguntarsa ta hukunta shi ke nan, Rikicin kansa ya yi masa lahani.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa, Zan raira yabbai ga Ubangiji, Maɗaukaki.
1 Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya. Yabonka ya kai har sammai,
2 Yara da jarirai suna raira shi, Ka gina kagara saboda magabtanka, Domin ka tsai da maƙiyanka da abokan gābanka.
3 Sa'ad da na duba sararin sama, wanda ka yi, Da wata da taurari waɗanda ka sa a wuraren zamansu,
4 Wane ne mutum, har da kake tunawa da shi, Mutum kurum, har da kake lura da shi?
5 Duk da haka in banda kai ba wanda ya fi shi, Ka naɗa shi da daraja da girma!
6 Ka sa shi ya yi mulkin dukan abin da ka halitta, Ka ɗora shi a kan dukan abubuwa,
7 Tumaki da shanu, har ma da namomin jeji,
8 Da tsuntsaye da kifaye, Da dukan halittar da suke cikin tekuna.
9 Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya!
1 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji, Zan hurta dukan abubuwa masu banmamaki da ka yi.
2 Zan raira waƙa da farin ciki sabili da kai, Zan raira yabo gare ka, ya Maɗaukaki!
3 Magabtana sun jā da baya da suka gan ka, Suka faɗi, suka mutu.
4 Kai da kake alƙali mai adalci Ka zauna a kursiyinka, Ka kuwa yi shari'ar da ta yi mini daidai.
5 Ka kā da arna, Ka kuma hallakar da mugaye, Ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba.
6 An hallaka abokan gābanmu har abada, Ka lalatar da biranensu, An kuma manta da su sarai.
7 Amma Ubangiji sarki ne har abada, Ya kafa kursiyinsa domin yin shari'a.
8 Yana mulkin duniya da adalci, Yana yi wa mutane shari'a da gaskiya.
9 Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta, Wurin ɓuya a lokatan wahala.
10 Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji, Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba.
11 Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona! Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!
12 Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya, Ba ya mantawa da kukansu, Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.
13 Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai! Ka dubi irin wulakancin da maƙiya suka yi mini! Ka kuɓutar da ni daga mutuwa, ya Ubangiji,
14 Domin in iya tsayawa a gaban jama'ar Urushalima, In faɗa musu dukan abin da ya sa nake yabonka. Zan yi farin ciki saboda ka cece ni.
15 Arna sun haƙa rami sun kuwa fāɗa ciki, Sun ɗana tarko, ya kuwa kama su.
16 Ubangiji ya bayyana kansa ta wurin shari'arsa mai adalci, Mugaye sun kama kansu da abubuwan da suka aikata.
17 Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye, Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.
18 Ba kullum ne ake ƙyale masu bukata ba, Ba za a danne sa zuciyar waɗanda ake zalunta ba har abada.
19 Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka! Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su.
20 Ka sa su ji tsoro, ya Ubangiji, Ka sa su sani su mutane ne kawai.
1 Ya Ubangiji, me ya sa kake can nesa? Me ya sa ka ɓoye kanka a lokacin wahala?
2 Mugaye suna fāriya, suna kuma tsananta wa matalauta, Ɗana tarkon da suka yi yă kama su.
3 Mugun mutum yana fāriya da mugayen manufofinsa, Mai haɗama yakan zagi Ubangiji ya kuma ƙi shi.
4 Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!” Wannan ne abin da mugu yake tunani.
5 Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi. Ba zai fahimci hukuncin Allah ba, Yana yi wa abokan gābansa duban raini.
6 Yana ce wa kansa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba, Ba zan taɓa shan wahala ba.”
7 Maganganunsa suna cike da zage-zage, da ƙarairayi, da barazana, Yana da saurin faɗar maganganun ƙiyayya da na mugunta.
8 Yakan ɓuya cikin ƙauyuka, Yă jira a can har yă kashe marasa laifi. Yakan yi sanɗa, ya kama kāsassu,
9 Yakan jira a inda ya ɓuya kamar zaki. Yakan kwanta yana fakon wanda zai kama, Har ya kama shi da tarkonsa ya tafi da shi!
10 Yakan ragargaza kāsasshe, Yă gwada masa ƙarfi, yă ci nasara a kansa.
11 Mugun mutum yakan ce wa kansa, “Allah bai kula ba! Ya rufe idonsa, ba zai taɓa ganina ba.”
12 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni! Kada ka manta da waɗanda ake zaluntarsu, ya Allah!
13 Yaya mugun zai riƙa raina Allah, Har yă riƙa ce wa kansa, “Ba zai hukunta ni ba”?
14 Amma kana gani, kana kuma lura da masu shan wuya, da masu ɓacin rai, Koyaushe kuma a shirye kake ka yi taimako. Mutum wanda ba shi da mai taimako yakan danka kansa gare ka, Gama kullum kakan taimaki masu bukata.
15 Ka karya ikon mugaye, masu mugunta, Ka hukunta su saboda muguntarsu, Har hukuncinsu ya cika sarai.
16 Ubangiji sarki ne har abada abadin, Arna kuma za su ɓace daga ƙasarsa.
17 Za ka saurara ga addu'o'in masu kaɗaici, ya Ubangiji, Za ka ba su ƙarfin hali.
18 Za ka ji koke-koken waɗanda ake zalunta da na marayu, Ka yi shari'ar da za su ji daɗi, Domin kada 'yan adam su ƙara haddasa wata razana.
1 Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya, Wauta ce idan kun ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,
2 Domin mugaye sun ja bakkunansu, Sun kuma ɗana kibansu Domin su harbi mutanen kirki a duhu.
3 Ba abin da mutumin kirki zai iya yi Sa'ad da kome ya lalace.”
4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Yana da kursiyinsa a Sama. Yana kallon dukan mutane Yana sane da abin da suke yi.
5 Yana auna masu kirki da mugaye dukka, Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya.
6 Yakan aukar da garwashin wuta Da kibritu mai cin wuta a kan mugaye, Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna.
7 Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar kyawawan ayyuka, Masu yi masa biyayya za su zauna a gabansa.
1 Ka cece ni, ya Ubangiji, Ba sauran mutanen kirki, Ba kuma za a sami amintattun mutane ba.
2 Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya, Suna ruɗin junansu da yaudara.
3 Ka sa harsunan nan masu yaudara su yi shiru, Ya Ubangiji, ka rufe bakunan nan masu fāriya!
4 Sukan ce, “Za mu yi magana yadda muka ga dama, Ba kuwa wanda zai hana mu. Wane ne yake da ikon faɗa mana abin da za mu faɗa?”
5 Ubangiji ya ce, “Amma zan zo yanzu, Domin ana zaluntar masu bukata, Waɗanda aka tsananta musu kuma, suna nishi don zafi. Zan ba su zaman lafiya da suke nema!”
6 Alkawaran Ubangiji abin dogara ne, Alkawarai ne na ainihi kamar azurfa Da aka tace har sau bakwai cikin matoya.
7 Ka kiyaye lafiyarmu, ya Ubangiji, Ka kiyaye mu daga irin waɗannan mutane.
8 Akwai mugaye ko'ina, suna ta yanga, Suna ta yabon abin da yake mugunta.
1 Har yaushe za ka manta da ni, ya Ubangiji? Har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye mini fuskarka?
2 Har yaushe raina zai jure da shan wahala? Har yaushe zan yi ta ɓacin rai dare da rana? Har yaushe maƙiyana za su riƙa cin nasara a kaina?
3 Ka dube ni, ya Ubangiji Allahna, ka amsa mini, Ka mayar mini da ƙarfina, don kada in mutu.
4 Sa'an nan maƙiyana ba za su ce, “Ai, mun yi nasara da shi” ba! Ba za su iya yin murna saboda fāɗuwata ba.
5 Amma ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarka, Zan yi murna gama za ka cece ni.
6 Zan raira waƙa ga Ubangiji, Gama ya kyautata mini.
1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah!” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.
2 Daga Sama Ubangiji ya dubi mutane, Yă ga ko da akwai masu hikima Waɗanda suke yi masa sujada.
3 Amma dukansu sun koma baya, Su duka mugaye ne, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai, Babu ko ɗaya.
4 Ubangiji ya ce, “Ba su sani ba? Duk waɗannan masu aikin mugunta jahilai ne? Ta wurin yi wa jama'ata fashi suke zaman gari, Ba su yin addu'a gare ni.”
5 Amma za su razana, Gama Allah yana tare da masu yi masa biyayya.
6 Suna yi wa shirye-shiryen kāsasshe dariya, Saboda yana dogara ga Ubangiji.
7 Ina addu'a matuƙa domin ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona! Sa'ad da Ubangiji ya sāke arzuta jama'arsa, Zuriyar Yakubu za su yi farin ciki, Jama'ar Isra'ila za su yi murna.
1 Wane ne zai iya zama cikin Haikalinka? Wa zai iya tsayawa a Sihiyona, wato tudunka tsattsarka?
2 Sai dai mutumin da yake biyayya ga Allah da kowane abu, Yana kuwa aikata abin da yake daidai, Wanda yake faɗar gaskiya da zuciya ɗaya,
3 Wanda kuma ba ya ɓāta sunan waɗansu. Ba ya zargin abokansa, Ba ya kuwa baza jita-jita a kan maƙwabtansa.
4 Yakan raina waɗanda Allah ya ƙi su, Amma yana girmama waɗanda suke yi wa Ubangiji biyayya, Kullum yana cika alkawaran da ya yi ko ta halin ƙaƙa,
5 Yana ba da rance ba ruwa, Ba ya karɓar hanci don ya yi shaidar zur a kan marar laifi. Wanda ya aikata waɗannan abubuwa ba zai taɓa fāɗuwa ba.
1 Ya Allah, ka kiyaye ni, gama na zo gare ka neman mafaka.
2 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Ubangijina, Dukan kyawawan abubuwan da nake da su Daga gare ka suke.”
3 Dubi irin martabar da amintattun jama'ar Ubangiji suke da ita! Ba abin da raina ya fi so, Sai in zauna tare da su.
4 Waɗanda suke hanzari zuwa ga gumaka, Za su jawo wa kansu wahala. Ba zan yi tarayya da su da hadayarsu ba. Ba zan yi sujada ga gumakansu ba.
5 Kai ne kaɗai, nake da shi, ya Ubangiji, Kai ne kake biyan dukan bukatata, Raina yana hannunka.
6 Kyautanka zuwa gare ni da bansha'awa suke, Kyawawa ne kuwa ƙwarai!
7 Na yabi Ubangiji saboda yana bi da ni, Da dare kuma lamirina yana yi mini fadaka.
8 A kullum ina jin Ubangiji yana tare da ni, Yana nan kusa, ba abin da zai girgiza ni.
9 Don haka cike nake da murna da farin ciki, Kullum kuwa ina jin kome lafiya yake,
10 Saboda ba za ka yarda in shiga lahira ba, Ba za ka bar wanda kake ƙauna a zurfafa daga ƙarƙas ba.
11 Za ka nuna mini hanyar rai, Kasancewarka takan sa in cika da farin ciki, Taimakonka kuwa yana kawo jin daɗi har abada.
1 Ka kasa kunne ga roƙona, ni adalin mutum, Ka lura da kukana na neman taimako! Ka kasa kunne ga addu'ata, Gama ni ba mayaudari ba ne.
2 Za ka shara'anta shari'ar da za ta gamshe ni, Saboda ka san abin da yake daidai.
3 Ka san zuciyata, Kakan zo gare ni da dare, Ka riga ka jarraba ni sarai, Ba ka kuwa sami mugun nufi a cikina ba. Na ƙudurta kuma bakina ba zai yi saɓo ba.
4 Zancen aikin sauran mutane, Na yi biyayya ga umarninka Ban bi hanyar rashin hankali ba.
5 Ina tafiya a kan tafarkinka kullum, Ban kuwa kauce ba.
6 Ina addu'a gare ka, ya Allah, Domin kakan amsa mini, Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata.
7 Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki, Ya Mai Ceto, Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu.
8 Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu, Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka,
9 Daga hare-hare na mugaye. Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni.
10 Ba su jin tausayi, suna magana da girmankai,
11 Yanzu suna kewaye da ni duk inda na juya, Suna jira su sami dama su fyaɗa ni ƙasa.
12 Kamar zakoki suke nema su yayyage ni kaca-kaca, Kamar sagarun zakoki suna fakona a wurin ɓuyarsu.
13 Ka zo, ya Ubangiji, Ka yi yaƙi da maƙiyana, ka yi nasara da su! Ka cece ni da takobinka daga mugaye,
14 Ka cece ni daga gare su da ikonka, Ka cece ni daga waɗanda suke da duk abin da suke so a duniyan nan, Ka hukunta su da wahalar da ka shirya musu, Ka sa har 'ya'yansu, su ma, ta ishe su, Wahalar da ta ragu kuma, ta sami jikokinsu!
15 Zan gan ka domin ni adali ne, Sa'ad da na farka, kasancewarka tana cika ni da farin ciki.
1 Ina ƙaunarka ƙwarai, ya Ubangiji! Kai ne mai kāre ni.
2 Ubangiji ne Mai Cetona, Shi ne garkuwata mai ƙarfi. Allahna, shi ne yake kiyaye ni, Lafiya nake sa'ad da nake tare da shi, Yana kiyaye ni kamar garkuwa, Yana kāre ni, ya ba ni lafiya.
3 Na yi kira ga Ubangiji, Yakan cece ni daga magabtana, Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
4 Mutuwa ta ɗaure ni kam da igiyoyinta, Halaka ta auko mini a kai a kai.
5 Mutuwa ta ɗaure ni kam da igiyoyinta, Kabari kuma ya ɗana mini tarko.
6 A shan wahalata na kira ga Ubangiji, Na yi kira ga Allahna domin neman taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Sai duniya ta raurawa ta girgiza, Harsashin duwatsu suka jijjigu, suka girgiza Saboda Allah ya husata!
8 Hayaƙi ya yi ta tuƙaƙowa daga hancinsa, Harshen wuta da garwashi suna fitowa daga bakinsa.
9 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, Tare da girgije mai duhu a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Ya sauko ta bisa bayan kerubobi, Yana tafe da sauri a kan fikafikan iska.
11 Ya rufe kansa da duhu, Gizagizai masu duhu cike da ruwa, suna kewaye da shi.
12 Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko Daga cikin walƙiya da take gabansa, Suka keto ta cikin gizagizai masu duhu.
13 Sa'an nan Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama, Aka ji muryar Maɗaukaki. Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko.
14 Ya harba kibansa, ya watsa magabtana, Da walƙatawar walƙiya ya kore su.
15 Kashiyar teku ta bayyana, Tussan duniya sun bayyana, Sa'ad da ka tsauta wa magabtana, ya Ubangiji, Sa'ad da kuma ka yi musu tsawa da fushi.
16 Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni, Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.
17 Ya cece ni daga magabtana masu ƙarfi, Daga kuma dukan masu ƙina, Gama sun fi ƙarfina!
18 Sa'ad da nake shan wahala suka auka mini, Amma Ubangiji ya kiyaye ni.
19 Ya fisshe ni daga cikin hatsari, Ya cece ni, don yana jin daɗina.
20 Ubangiji yakan sāka mini, saboda ni adali ne, Yakan sa mini albarka, don ni marar laifi ne.
21 Na yi biyayya da umarnan Ubangiji, Ban yi wa Ubangiji Allahna tawaye ba.
22 Na kiyaye dukan dokokinsa, Ban yi rashin biyayya da umarnansa ba.
23 Ya sani ba ni da laifi, Domin na kiyaye kaina daga mugunta.
24 Don haka ya sāka mini, domin ni adali ne, Gama ya sani ni marar laifi ne.
25 Kai, ya Ubangiji, mai aminci ne ga masu aminci, Kai nagari ne, cikakke ga kamilai.
26 Kai Mai Tsarki ne ga waɗanda suke tsarkaka, Amma kana gāba da mugaye.
27 Kakan ceci masu tawali'u, Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai.
28 Ubangiji yakan ba ni haske, Allah yakan kawar da duhuna.
29 Yakan ba ni ƙarfin da zan fāɗa wa magabtana, Da ikon rinjayar kagararsu.
30 Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai, Maganarsa abar dogara ce! Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.
31 Ubangiji shi kaɗai ne Allah, Allah ne kaɗai kāriyamu.
32 Shi ne Allahn da yake ƙarfafa ni, Yana kiyaye lafiyata a kan hanya.
33 Yana sa in tabbata lafiya nake tafiya, kamar barewa. Yana kiyaye ni lafiya a kan duwatsu.
34 Yakan horar da ni don yaƙi, Domin in iya amfani da baka mafi ƙarfi.
35 Ya Ubangiji ka kiyaye ni, ka cece ni, Na zama babban mutum saboda kana lura da ni, Ikonka kuma ya kiyaye lafiyata.
36 Ka tsare ni, ba a kama ni ba, Ban kuwa taɓa fāɗuwa ba.
37 Na kori magabtana, har na kama su, Ba zan tsaya ba, sai na yi nasara da su.
38 Zan buge su har ƙasa, ba kuwa za su tashi ba, Za su fāɗi ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Kakan ba ni ƙarfin yin yaƙi, Kakan ba ni nasara a kan magabtana.
40 Ka kori magabtana daga gare ni, Zan hallaka waɗanda suke ƙina.
41 Suna kukan neman taimako, amma ba wanda zai iya cetonsu, Za su yi kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa ba.
42 Zan murƙushe su har su zama ƙura Wadda iska take kwashewa, Zan tattake su kamar caɓi a titi.
43 Ka cece ni daga mutane masu tawaye, Ka naɗa ni in yi mulkin sauran al'umma, Jama'ar da ban san ta ba, ta zama abin mulkina.
44 Za su yi biyayya sa'ad da suka ji ni, Baƙi za su rusuna mini,
45 Za su karai, Su fita, suna rawar jiki daga kagaransu.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai kāre ni! Allah ne, Mai Cetona! A yi shelar girmansa!
47 Yakan ba ni nasara a kan magabtana, Yakan sa jama'a a ƙarƙashina,
48 Yakan cece ni daga maƙiyana. Ka ba ni nasara a kan magabtana, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga mutane masu kama-karya,
49 Don haka zan yabe ka a cikin al'ummai, Zan raira maka yabo.
50 Kullayaumi Allah yakan ba sarkin da ya naɗa babbar nasara. Yakan nuna madawwamiyar ƙauna ga wanda ya zaɓa, Wato Dawuda da zuriyarsa har abada.
1 Dubi yadda sararin sama yake bayyana ɗaukakar Allah! Dubi yadda suke bayyana a fili ayyukansa da ya yi!
2 Kowace rana tana shelar ɗaukakarsa ga ranar da take biye, Kowane dare yana nanata ɗaukakarsa ga daren da take biye.
3 Ba magana ko kalma da aka hurta, Ba wani amon da aka ji,
4 Duk da haka muryarsu ta game duniya duka, Saƙonsu ya kai ko'ina a duniya. Allah ya kafa wa rana alfarwa a sararin sama,
5 Tana fitowa kamar ango yana taƙama daga gidansa, Kamar ɗan wasan da ya ƙosa ya yi tsere.
6 Takan fara daga wannan ƙarshen sararin sama, ta kewaye zuwa wancan. Ba abin da zai iya ɓuya daga zafinta.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, Tana wartsakar da rai. Umarnan Ubangiji abin dogara ne, Sukan ba da hikima ga wanda ba shi da ita.
8 Ka'idodin Ubangiji daidai suke, Waɗanda suke biyayya da su sun ji daɗi. Umarnan Ubangiji daidai suke, Sukan ba da fahimi ga zuciya.
9 Daidai ne a bauta wa Ubangiji, A ci gaba da yi har abada. Duk abin da Ubangiji ya hukunta daidai ne, A kullum hukuntan Ubangiji daidai suke.
10 Abin da ake so ne fiye da zinariya, I, fiye da tatacciyar zinariya ma, Sun fi zuma zaƙi, I, fiye da tatacciyar zuma ma.
11 Suna ba ni ilimi, ni baranka, Ina samun ladan yin biyayya da su.
12 Ba mai iya ganin kuskuren kansa, Ka cece ni daga ɓoyayyun laifofi!
13 Ka tsare ni kuma daga laifofi na fili, Kada ka bari su mallake ni. Sa'an nan zan zama kamili, In kuɓuta daga mugun zunubi.
14 Ka sa maganata da tunanina su zama abin karɓa a gare ka, Ya Ubangiji, Mafakata da Mai Fansata!
1 Ubangiji ya amsa maka a ranar wahala! Allah na Yakubu ya kiyaye ka!
2 Ya aiko maka da taimako daga Haikalinsa, Ya kawo maka gudunmawa daga Sihiyona.
3 Ya karɓi hadayunka, Ya kuma ji daɗin dukan sadakokinka.
4 Ya ba ka abin da kake bukata, Ya sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
5 Mu kuma, sai mu yi sowa ta farin ciki saboda ka ci nasara, Mu yi bikin cin nasara da ka yi, Da yabon Ubangiji Allahnmu. Allah ya amsa dukan roƙe-roƙenka!
6 Yanzu dai na sani Ubangiji yakan ba da nasara ga zaɓaɓɓen sarkinsa, Yakan amsa masa daga samaniyarsa mai tsarki, Da ikonsa mai girma yakan sa shi yă yi nasara.
7 Waɗansu ga karusan yaƙinsu suke dogara, Waɗansu kuwa ga dawakansu, Amma mu, ga ikon Ubangiji Allahnmu muke dogara!
8 Za su yi tuntuɓe su fāɗi, Amma mu za mu tashi mu tsaya daram!
9 Ka ba sarki nasara, ya Ubangiji, Ubangiji zai amsa mana sa'ad da muka yi kira.
1 Sarki yana murna, ya Ubangiji, Domin ka ba shi ƙarfi, Yana cike da farin ciki, Don ka sa ya ci nasara.
2 Ka biya masa bukatarsa, Ka amsa roƙonsa.
3 Ka zo gare shi da albarka mai yawa, Ka sa kambin zinariya a kansa.
4 Ya roƙi rai, ka kuwa ba shi mai tsawo, Da yawan kwanaki.
5 Darajarsa tana da girma saboda taimakonka, Ka sa ya yi suna da martaba.
6 Albarkarka tana a kansa har abada, Kasancewarka tare da shi, takan cika shi da murna.
7 Sarki yana dogara ga Maɗaukaki, Saboda madawwamiyar ƙaunar Ubangiji Zai zama sarki har abada.
8 Sarki zai kakkama dukan magabtansa, Zai kakkama duk waɗanda suke ƙinsa.
9 Ubangiji zai hallaka su kamar harshen wuta, sa'ad da ya bayyana. Ubangiji zai cinye su a cikin fushinsa, Wuta kuma za ta cinye su ƙurmus.
10 Sarki zai karkashe 'ya'yansu duka, Zai yanyanke dukan zuriyarsu.
11 Sun ƙulla mugayen dabaru, suna fakonsa, Amma ba za su yi nasara ba.
12 Zai harba kibansa a kansu, Ya sa su juya su gudu.
13 Ya Ubangiji, ka zo da ƙarfinka! Za mu raira waƙa mu yabi ikonka.
1 Ya Allahna, ya Allahna, Don me ka yashe ni? Na yi kuka mai tsanani, ina neman taimako, Amma har yanzu ba ka zo ba!
2 Da rana na yi kira a gare ka, ya Allahna, Amma ba ka amsa ba. Da dare kuma na yi kira, Duk da haka ban sami hutawa ba.
3 Amma an naɗa ka Mai Tsarki, Wanda Isra'ila suke yabonsa.
4 Kakanninmu suka dogara gare ka, Sun dogara gare ka, ka kuwa cece su.
5 Suka yi kira gare ka, suka tsira daga hatsari, Suka dogara gare ka, ba su kuwa kunyata ba.
6 A yanzu dai ni ba mutum ba ne, tsutsa ne kawai, Rainanne, abin ba'a ga kowa da kowa!
7 Duk wanda ya gan ni Sai yă maishe ni abin dariya, Suna zunɗena da harshensu suna kaɗa kai.
8 Suka ce, “Ka dogara ga Ubangiji, Me ya sa bai cece ka ba? Idan Ubangiji na sonka, Don me bai taimake ka ba?”
9 Kai ne ka fito da ni lafiya a lokacin da aka haife ni, A lokacin da nake jariri ka kiyaye ni.
10 Tun daga lokacin da aka haife ni nake dogara gare ka, Kai ne Allahna tun daga ran da aka haife ni.
11 Kada ka yi nisa da ni! Wahala ta gabato, Ba kuwa mai taimako.
12 Magabta da yawa sun kewaye ni kamar bijimai, Dukansu suna kewaye da ni, Kamar bijimai masu faɗa na ƙasar Bashan.
13 Sun buɗe bakinsu kamar zakoki, Suna ruri, suna ta bina a guje.
14 Ƙarfina ya ƙare, Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa. Dukan gaɓoɓina sun guggulle, Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.
15 Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura.
16 Ƙungiyar mugaye na kewaye da ni, Suka taso mini kamar garken karnuka, Suka soke hannuwana da ƙafafuna.
17 Ana iya ganin ƙasusuwana duka. Magabtana suka dube ni, suka zura mini ido.
18 Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, Suka jefa kuri'a a kan babbar rigata.
19 Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji! Ka gaggauta ka cece ni, ya Mai Cetona!
20 Ka cece ni daga takobi, Ka ceci raina daga waɗannan karnuka.
21 Ka kuɓutar da ni daga waɗancan zakoki, Ba ni da mataimaki a gaban bijimai masu mugun hali.
22 Zan faɗa wa mutanena abin da ka yi, Zan yabe ka cikin taronsu.
23 “Ku yabe shi, ku bayin Ubangiji! Ku girmama shi, ku zuriyar Yakubu! Ku yi masa sujada, ku jama'ar Isra'ila!
24 Ba ya ƙyale matalauta, Ko ya ƙi kulawa da wahalarsu, Ba ya rabuwa da su, Amma yakan amsa lokacin da suka nemi taimako.”
25 Zan yabe ka a gaban babban taron jama'a Saboda abin da ka yi, A gaban dukan masu yi maka biyayya, Zan miƙa sadakokin da na alkawarta.
26 Matalauta za su ci yadda suke so, Masu zuwa wurin Ubangiji za su yabe shi, Su arzuta har abada!
27 Dukan al'ummai za su tuna da Ubangiji, Za su zo gare shi daga ko'ina a duniya, Dukan kabilai za su yi masa sujada.
28 Ubangiji Sarki ne, Yana mulki a kan al'ummai.
29 Masu girmankai duka za su rusuna masa, 'Yan adam duka za su rusuna masa, Dukan waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa.
30 Zuriya masu zuwa za su bauta masa, Mutane za su ambaci Ubangiji ga zuriya mai zuwa.
31 Mutanen da ba a haifa ba tukuna, za a faɗa musu, “Ubangiji ya ceci jama'arsa!”
1 Ubangiji makiyayina ne, Ba zan rasa kome ba.
2 Yana sa ni in huta a saura mai ɗanyar ciyawa, Yana bi da ni a tafkuna masu daɗin ruwa, suna kwance lif.
3 Yana ba ni sabon ƙarfi. Yana bi da ni a hanyar da suke daidai kamar yadda ya alkawarta.
4 Ko da hanyan nan ta bi ta tsakiyar duhu na mutuwa, Ba zan ji tsoro ba, ya Ubangiji, Gama kana tare da ni! Sandanka na makiyayi da kerenka Suna kiyaye lafiyata.
5 Ka shirya mini liyafa Inda maƙiyana duk za su iya ganina, Ka marabce ni, ka shafe kaina da mai, Ka cika tanduna fal da mai.
6 Hakika, alherinka da ƙaunarka Za su kasance tare da ni muddin raina. Haikalinka zai zama gidana har abada.
1 Duniya da dukan abin da yake cikinta na Ubangiji ne, Duniya da dukan mazaunanta nasa ne.
2 Ya gina ta a bisa ruwa mai zurfi na ƙarƙashin ƙasa, Ya kuma kafa harsashinta a zurfin teku.
3 Wa yake da iko yă hau tudun Ubangiji? Wa yake da iko ya shiga Haikalinsa tsattsarka?
4 Sai wanda yake da tsarki cikin aiki, da tunani, Wanda ba ya yi wa gumaka sujada, Ko kuma yă yi alkawarin ƙarya.
5 Ubangiji zai sa masa albarka, Allah Mai Cetonsa zai kuɓutar da shi.
6 Su ne irin mutanen da suke zuwa wurin Allah, Waɗanda suke zuwa a gaban Allah na Yakubu.
7 A buɗe ƙofofi sosai, A buɗe daɗaɗɗun ƙofofi, Babban Sarki kuwa zai shigo!
8 Wane ne wannan babban Sarki? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai nasara cikin yaƙi!
9 A buɗe ƙofofi sosai, A buɗe daɗaɗɗun ƙofofi, Babban Sarki kuwa zai shigo!
10 Wane ne wannan babban Sarki? Ubangiji Mai Runduna, shi ne babban Sarki!
1 A gare ka nake yin addu'a, ya Ubangiji,
2 A gare ka nake dogara, ya Allah. Ka cece ni daga shan kunyar fāɗuwa, Kada ka bar magabtana su yi mini duban wulakanci!
3 Waɗanda suke dogara gare ka, Ba za su kasa yin nasara ba, Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa.
4 Ka koya mini al'amuranka, ya Ubangiji, Ka sa su zama sanannu a gare ni.
5 Ka koya mini in yi zamana bisa ga gaskiyarka, Gama kai Mai Cetona ne. Dukan yini ina dogara a gare ka.
6 Ya Ubangiji, ka tuna da alherinka da madawwamiyar ƙaunarka, Waɗanda ka nuna tun a dā.
7 Ka gafarta zunubaina da kurakuraina masu yawa na ƙuruciyata. Saboda madawwamiyar ƙaunarka da alherinka, Ka tuna da ni, ya Ubangiji!
8 Ubangiji mai adalci ne, mai alheri, Yana koya wa masu zunubi tafarkin da za su bi.
9 Yana bi da masu tawali'u a tafarkin da suke daidai, Yana koya musu nufinsa.
10 Da ƙauna da aminci yana bi da dukan waɗanda suke biyayya da alkawarinsa da umarnansa.
11 Ka cika alkawarinka, ya Ubangiji, ka gafarta zunubaina, gama suna da yawa.
12 Waɗanda suke biyayya da Ubangiji Za su koyi hanyar da za su bi daga gare shi.
13 Kullayaumi za su arzuta, 'Ya'yansu kuma za su zauna lafiya a ƙasar.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke biyayya da shi, Yakan koya musu alkawarinsa.
15 A koyaushe ga Ubangiji nake neman taimako, Yakan kuɓutar da ni daga hatsari.
16 Ka juyo wajena, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, Gama ina zaman kaɗaici da rashin ƙarfi.
17 Damuwar zuciyata ta yi yawa, Ka raba ni da dukan damuwa, Ka cece ni daga dukan wahalata.
18 Ka kula da wahalata da azabata, Ka gafarta dukan zunubaina.
19 Ka duba yawan magabtan da nake da su, Dubi irin ƙiyayyar da suke yi mini!
20 Ka yi mini kāriya, ka cece ni, Gama na zo wurinka neman kāriya.
21 Ka sa nagartata da amincina su kiyaye ni, Gama na dogara gare ka.
22 Ka fanshi jama'arka daga dukan wahalarsu, ya Allah!
1 Ka hurta rashin laifina, ya Ubangiji, Gama na yi abin da suke daidai, Na dogara gare ka gaba ɗaya.
2 Ka jarraba ni ka auna ni, ya Ubangiji, Ka gwada muradina da tunanina.
3 Madawwamiyar ƙaunarka tana bi da ni, Amincinka yake yi mini jagora kullayaumin.
4 Ba na tarayya da mutanen banza, Ba abin da ya gama ni da masu riya.
5 Ina ƙin tarayya da masu mugunta, Nakan kauce wa mugaye.
6 Ya Ubangiji, na wanke hannuwana Don in nuna ba ni da laifi, Da ibada nakan taka, ina kewaya bagadenka.
7 Na raira waƙar godiya, Na faɗi dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 Ya Ubangiji, ina ƙaunar Haikali inda zatinka yake, Inda ɗaukakarka yake zaune.
9 Kada ka hallaka ni tare da masu zunubi, Ka cece ni daga ƙaddarar masu kisankai,
10 Mutanen da suke aikata mugunta a dukan lokaci, A koyaushe suna shirye don su ba da rashawa.
11 Amma ni, ina yin abin da yake daidai, Ka yi mini jinƙai ka fanshe ni!
12 Na kuɓuta daga dukan hatsarori, A taron sujada na yabi Ubangiji!
1 Ubangiji ne haskena da cetona, Ba zan ji tsoron kowa ba. Ubangiji yana kiyaye ni daga dukan hatsari, Ba zan ji tsoro ba.
2 Sa'ad da mugaye suka tasar mini, Suna ƙoƙari su kashe ni, Za su yi tuntuɓe su fāɗi.
3 Ko da rundunar mayaƙa ta kewaye ni, Ba zan ji tsoro ba. Ko da magabtana sun tasar mini, Zan dogara ga Allah.
4 Abu guda nake roƙo a wurin Ubangiji, Abu ɗaya kaɗai nake bukata, Shi ne in zauna a masujadar Ubangiji, In yi ta al'ajabin alherinsa Dukan kwanakin raina, In roƙi biyarwarsa a can.
5 A lokatan wahala zai kiyaye ni a inuwarsa, Zai kiyaye ni lafiya a Haikalinsa, Zai ɗora ni a kan dutse mai tsayi, ya kiyaye ni.
6 Ta haka zan ci nasara a kan magabtana da suke kewaye da ni. Da sowar farin ciki mai yawa zan miƙa sadakoki a Haikalinsa! Zan raira waƙa, in yabi Ubangiji!
7 Ka ji ni, ya Ubangiji, sa'ad da na ya yi kira gare ka! Ka yi mini jinƙai ka amsa mini!
8 Ka ce, “Zo wurina,” Zan kuwa zo gare ka, ya Ubangiji,
9 Kada ka ɓoye mini fuskarka, ya Ubangiji! Kada ka yi fushi da ni, Kada kuwa ka kori bawanka. Kai ne kake taimakona, tun dā ma, Kada ka bar ni, kada ka yashe ni, Ya Allahna, Mai Cetona!
10 Mai yiwuwa ne ubana da uwata su yashe ni, Amma Ubangiji zai lura da ni.
11 Ka koya mini abin da ya kamata in yi, ya Ubangiji, Ka bi da ni kan lafiyyiyar hanya, Domin ina da magabta da yawa.
12 Kada ka bar ni a hannun magabtana, Waɗanda suke fāɗa mini da ƙarairayi da kurari.
13 Hakika zan rayu domin in ga alherin Ubangiji Da zai yi wa jama'arsa.
14 Ka dogara ga Ubangiji! Ka yi imani, kada ka karai. Ka dogara ga Ubangiji!
1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji mai kāre ni, Ka ji kukana! In kuwa ba ka amsa mini ba, Zan zama ɗaya daga cikin waɗanda suka gangara zuwa lahira.
2 Ka ji ni lokacin da na yi kuka gare ka neman taimako, Ina ɗaga hannuwana wajen tsattsarkan Haikalinka.
3 Kada ka kāshe ni tare da mugaye, Tare da masu aikata mugunta, Mutane waɗanda maganarsu kamar ta zumunci ce, Amma zukatansu cike suke da ƙiyayya.
4 Ka hukunta su saboda abin da suka aikata. Ka hukunta su saboda dukan ayyukansu, Ka ba su abin da ya cancance su!
5 Ba su kula da abin da Ubangiji ya yi ba, Ko kuma abin da ya halitta, Don haka zai hukunta su, ya hallaka su har abada.
6 A yabi Ubangiji, Gama ya ji kukana na neman taimako!
7 Ubangiji yakan kiyaye ni, yă tsare ni. Na dogara gare shi. Ya taimake ni, don haka ina murna, Ina raira masa waƙoƙin yabo.
8 Ubangiji yana kiyaye jama'arsa, Yakan kiyaye sarkinsa da ya zaɓa, ya kuma cece shi.
9 Ka ceci jama'arka, ya Ubangiji, Ka sa wa waɗanda suke naka albarka! Ka zama makiyayinsu, Ka lura da su har abada.
1 Ku yabi Ubangiji, ku alloli, Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa.
2 Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja, Ku rusuna a gaban Mai Tsarki sa'ad da ya bayyana.
3 An ji muryar Ubangiji a kan tekuna, Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Tsawar muryarsa kuwa ta yi amsa kuwa a bisa teku.
4 An ji muryar Ubangiji A dukan ikonsa da zatinsa!
5 Muryar Ubangiji takan karya itatuwan al'ul, Har ma da itatuwan al'ul na Lebanon.
6 Yakan sa duwatsun Lebanon su yi tsalle kamar 'yan maruƙa, Ya kuma sa Dutsen Harmon ya yi tsalle kamar ɗan maraƙi.
7 Muryar Ubangiji ta sa walƙiya ta walƙata.
8 Muryarsa ta sa hamada ta girgiza, Ta girgiza hamadar Kadesh.
9 Muryar Ubangiji ta sa barewa ta haihu, Ta sa itatuwa su kakkaɓe, Sa'ad da aka yi sowa a cikin Haikalinsa, Aka ce, “Daukaka ga Allah!”
10 Ubangiji yana sarautar ruwa mai zurfi, Yana sarauta kamar sarki har abada.
11 Ubangiji yana ba jama'arsa ƙarfi, Ya sa musu albarka da salama.
1 Ina yabonka, ya Ubangiji saboda ka cece ni, Ka kuwa hana magabtana su haɗiye ni.
2 Na roƙi taimako a gare ka, ya Ubangiji Allahna, Ka kuwa warƙar da ni.
3 Ka dawo da ni daga lahira. Na gangara tare da waɗanda suke gangarawa cikin zurfafa a ƙasa, Amma ka ceci raina.
4 Ku raira yabo ga Ubangiji, Ku amintattun jama'arsa! Ku tuna da abin da Mai Tsarki ya aikata, Ku yi masa godiya!
5 Fushinsa ba ya daɗewa, Alherinsa kuwa har matuƙa ne. Mai yiwuwa ne yă zama ana kuka da dare, Amma a yi murna da safe.
6 Ina zaune jalisan, na ce wa kaina, “Faufau ba za a taɓa cin nasara a kaina ba.”
7 Kana yi mini alheri, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni kamar a kagarar dutse. Amma sa'ad da ka ɓoye mini fuskarka, Sai in cika da tsoro.
8 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Ina roƙon taimakonka.
9 Wane amfani za a samu daga mutuwata? Ina ribar da za a samu daga zuwana kabari? Ko matattu suna iya yabonka? Za su iya shelar madawwamin alherinka?
10 Ka ji ni, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai! Ka taimake ni, ya Ubangiji!
11 Ka mai da baƙin cikina Ya zama rawar farin ciki, Ka tuɓe mini tufafin makoki, Ka sa mini na farin ciki.
12 Don haka ba zan yi shiru ba, Zan raira maka yabo, Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan gode maka har abada.
1 Na zo gare ka, ya Ubangiji, domin ka kiyaye ni. Kada ka bari a yi nasara da ni. Kai Allah mai adalci ne, Ka cece ni, ina roƙonka!
2 Ka ji ni! Ka cece ni yanzu! Ka zama mafakata, don ka kiyaye ni, Ka zama mai kāre ni, don ka cece ni.
3 Kai ne mafakata da kariyata, Ka bi da ni yadda ka alkawarta.
4 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka kafa domina, Kai ne inuwata.
5 Ina ba da kaina gare ka domin ka kiyaye ni. Za ka fanshe ni, ya Ubangiji, Kai Allah mai aminci ne.
6 Kana ƙin waɗanda suke yi wa gumaka sujada, Amma ni na dogara gare ka.
7 Zan yi murna da farin ciki, Saboda madawwamiyar ƙaunarka. Ka ga wahalata, Ka kuwa san damuwata.
8 Ba ka bar magabtana su kama ni ba, Ka kiyaye ni.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, Gama ina shan wahala, Idanuna sun gaji saboda yawan kuka, Na kuwa tafke ƙwarai!
10 Baƙin ciki ya gajerta kwanakina, Kuka kuma ya rage shekaruna. Na raunana saboda yawan wahalata, Har ƙasusuwana suna zozayewa!
11 Magabtana duka suna mini ba'a, Maƙwabtana sun raina ni, Waɗanda suka san ni kuwa suna jin tsorona, Sa'ad da suka gan ni a kan titi sukan guje mini.
12 Duk an manta da ni kamar matacce, Na zama kamar abin da aka jefar.
13 Na ji magabtana da yawa suna raɗa, Razana ta kewaye ni! Suna ƙulla maƙarƙashiya don su kashe ni.
14 Amma a gare ka na dogara, ya Ubangiji, Kai ne Allahna.
15 Kana lura da ni kullum, Ka cece ni daga magabtana, Daga waɗanda suke tsananta mini.
16 Ni, bawanka ne, Ka dube ni da alherinka, Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka!
17 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Kada ka bari a ci nasara a kaina! Ka sa a ci nasara a kan mugaye, Ka sa su yi shiru a lahira.
18 Ka rufe bakin maƙaryatan can Dukan masu girmankai da masu fāriya, Waɗanda suke wa adalai maganar raini!
19 Abin al'ajabi ne irin tanadin da ka yi wa masu tsoronka! Abin da kake aikatawa a gaban kowa kuma, Yana da banmamaki. Kana kiyaye waɗanda suke amincewa da kai.
20 Ka ɓoye su a wurinka lafiya daga makircin mutane, A inuwa mai lafiya ka ɓoye su daga zargin magabtansu.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Gama ya nuna mini ƙaunarsa mai ban al'ajabi, Sa'ad da aka kewaye ni, aka fāɗa mini!
22 Na ji tsoro, na zaci ka jefar da ni ne daga gabanka. Amma ka ji kukana sa'ad da na yi kira gare ka neman taimako.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, ku amintattun jama'arsa duka! Ubangiji yana kiyaye masu aminci, Amma yakan hukunta masu girmankai da tsanani.
24 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, Dukanku da kuke sa zuciya ga Ubangiji!
1 Mai farin ciki ne mutumin da aka gafarta masa zunubansa, Mai farin ciki ne kuma wanda aka gafarta masa laifofinsa.
2 Mai farin ciki ne wanda Ubangiji bai zarge shi a kan wani laifi ba, Wanda ba algus ko kaɗan a cikinsa.
3 Sa'ad da ban hurta zunubaina ba, Na gajiyar da kaina da yawan kuka dukan yini.
4 Ka hukunta ni dare da rana, ya Ubangiji, Ƙarfina duka ya ƙare sarai, Kamar yadda laima yake bushewa, Saboda zafin bazara.
5 Sa'an nan na hurta zunubaina gare ka, Ban ɓoye laifofina ba. Na ƙudurta in hurta su gare ka, Ka kuwa gafarta dukan laifofina.
6 Saboda haka dukan jama'arka masu biyayya, Za su yi addu'a gare ka, lokacin bukata. Sa'ad da babbar rigyawa ta malalo, Ba za ta kai wurinsu ba.
7 Kai ne maɓoyata, Za ka cece ni daga wahala. Ina raira waƙa da ƙarfi saboda cetonka, Domin ka kiyaye ni.
8 Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi, Zan koya maka, in kuma ba ka shawara.
9 Kada ka zama wawa kamar doki ko alfadari, Wanda dole sai da linzami, da ragama za a sarrafa shi, Sa'an nan yă yi maka biyayya.”
10 Tilas ne mugu yă sha wahala, Amma masu dogara ga Ubangiji, Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.
11 Dukanku adalai, ku yi murna, Ku yi farin ciki, Saboda abin da Ubangiji ya yi! Dukanku da kuke yi masa biyayya, Ku yi sowa ta farin ciki!
1 Dukanku adalai ku yi murna, A kan abin da Ubangiji ya yi, Ku yabe shi, ku da kuke masa biyayya!
2 Ku kaɗa garaya, kuna yi wa Ubangiji godiya. Ku raira masa waƙa, da kayan kaɗe-kaɗe masu tsarkiya.
3 Ku raira masa sabuwar waƙa, Ku kaɗa garaya da gwaninta, Ku kuma raira waƙa da ƙarfi!
4 Kalmomin Ubangiji gaskiya ne, Ayyukansa duka kuwa abin dogara ne.
5 Ubangiji yana ƙaunar abin da yake na adalci da gaskiya, Madawwamiyar ƙaunarsa ta cika duniya.
6 Ubangiji ya halicci duniya da umarninsa, Rana, da wata, da taurari kuma bisa ga maganarsa.
7 Ya tattara tekuna wuri ɗaya. Ya rurrufe zurfafan teku a ɗakunan ajiya.
8 Bari duk duniya ta ji tsoron Ubangiji! Ku ji tsoronsa ku mutanen duniya!
9 Da magana ya halicci duniya, Ta wurin umarninsa kowane abu ya bayyana.
10 Ubangiji yakan sassoke manufofin sauran al'umma, Yakan hana su aikata shirye-shiryensu.
11 Amma shirye-shiryensa sukan tabbata har abada. Nufe-nufensa kuma dawwamammu ne har abada.
12 Mai farin ciki ce al'ummar da Ubangiji yake Allahnta, Masu farin ciki ne jama'ar da Ubangiji ya zaɓo wa kansa!
13 Daga Sama Ubangiji ya dubo dukan 'yan adam.
14 Daga inda yake mulki, yakan dubo dukan mazaunan duniya.
15 Shi ya siffata tunaninsu, yana sane da dukan abin da suke yi.
16 Ba saboda ƙarfin mayaƙa sarki yakan ci nasara ba, Mayaƙi ba yakan yi rinjaye saboda ƙarfinsa ba.
17 Dawakan yaƙi ba su da amfani don cin nasara, Ƙarfin nan nasu ba zai iya ceto ba.
18 Ubangiji yana kiyaye masu tsoronsa, Waɗanda suke dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa.
19 Yakan cece su daga mutuwa, Yakan rayar da su a lokacin yunwa.
20 Ga Ubangiji muke sa zuciya, Shi mai taimakonmu ne, mai kiyaye mu.
21 Saboda da shi muke murna, Muna dogara ga sunansa mai tsarki.
22 Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji, Da yake a gare ka muke sa zuciya.
1 Zan yi godiya ga Ubangiji kullayaumin, Faufau ba zan taɓa fasa yabonsa ba.
2 Zan yabe shi saboda abin da ya yi, Da ma dukan waɗanda suke da tawali'u su kasa kunne, su yi murna!
3 Ku yi shelar girman Ubangiji tare da ni, Mu yabi sunansa tare!
4 Na yi addu'a ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini, Ya kuɓutar da ni daga dukan tsorona.
5 Waɗanda ake zalunta suka dube shi suka yi murna, Ba za su ƙara ɓacin rai ba.
6 Marasa galihu suka yi kira gare shi, ya kuwa amsa. Ya cece su daga dukan wahalarsu.
7 Mala'ikansa yana tsaron waɗanda suke tsoron Ubangiji, Ya cece su daga hatsari.
8 Ku gane da kanku yadda Ubangiji yake da alheri! Mai farin ciki ne mutumin da ya sami kwanciyar rai a wurinsa!
9 Ku yi tsoron Ubangiji ku jama'arsa duka, Masu tsoronsa suna da dukan abin da suke bukata.
10 Har zakoki sukan rasa abinci su ji yunwa, Amma masu biyayya ga Ubangiji, Ba abu mai kyau da sukan rasa.
11 Ku zo, ku abokaina, ku kasa kunne gare ni, Zan koya muku ku ji tsoron Ubangiji.
12 Kuna so ku ji daɗin rai? Kuna son tsawon rai da farin ciki?
13 To, ku yi nisa da mugun baki, Da faɗar ƙarairayi.
14 Ku rabu da mugunta, ku aikata alheri, Ku yi marmarin salama, ku yi ƙoƙarin samunta.
15 Ubangiji yana lura da adalai, Yana kasa kunne ga koke-kokensu,
16 Amma yana ƙin masu aikata mugunta, Saboda haka har mutanensu sukan manta da su.
17 Adalai sukan yi kira ga Ubangiji, yakan kuwa kasa kunne, Yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai, Yakan ceci waɗanda suka fid da zuciya.
19 Mutumin kirki yakan sha wahala da yawa, Amma Ubangiji yakan cece shi daga cikinsu duka.
20 Ubangiji yakan kiyaye shi sosai, Ba ko ɗaya daga cikin ƙasusuwansa da zai karye ba.
21 Mugunta za ta kashe mugu, Waɗanda suke ƙin adalai za a hukunta su.
22 Ubangiji zai fanshi bayinsa, Waɗanda suka tafi wurinsa neman mafaka Za a bar su da rai.
1 Ka yi hamayya da masu hamayya da ni, ya Ubangiji, Ka yi faɗa da masu faɗa da ni!
2 Ɗauki garkuwa da makamanka, ka zo ka taimake ni.
3 Ka daga mashin yaƙinka sama, da gatarinka, Ka yi gaba da masu fafarata. Ka faɗa mini kai ne Mai Cetona!
4 Ka sa a kori waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni, a kunyatar da su! Ka sa waɗanda suke mini maƙarƙashiya su juya da baya, su ruɗe!
5 Ka sa su zama kamar tattakar da iska take kwashewa, Kamar waɗanda mala'ikan Ubangiji yake korarsu!
6 Ka sa hanyarsu ta duhunta, ta yi santsi, A sa'ad da mala'ikan Ubangiji yake fyaɗe su ƙasa!
7 Suka kafa mini tarko ba dalili, Sun kuma haƙa rami mai zurfi don in faɗa ciki.
8 Amma kafin su farga, hallaka za ta kama su. Tarkunan da suka kafa za su kama su, Su kuma fāɗa cikin ramin da suka haƙa!
9 Sa'an nan zan yi murna saboda Ubangiji, Zan yi murna, gama ya cece ni.
10 Da zuciya ɗaya zan ce wa Ubangiji, “Ba wani kamarka! Kakan kāre marasa ƙarfi daga masu ƙarfi, Talaka da matalauci kuma daga azzalumai!”
11 Mugaye suna ba da muguwar shaida a kaina, Suna kai ƙarata a kan laifofin da ban san kome a kansa ba.
12 Sun sāka mini alheri da mugunta, Cike nake da nadama.
13 Amma sa'ad da suke ciwo, nakan sa tufafin makoki, Na ƙi cin abinci, Na yi addu'a da kaina a sunkuye,
14 Kamar yadda zan yi wa aboki ko ɗan'uwa addu'a. Ina tafe a takure saboda makoki, Kamar wanda yake makoki domin mahaifiyarsa.
15 Sa'ad da nake shan wahala, Murna suke yi duka, Sun kewaye ni, suna ta yi mini dariya, Baƙi sun duke ni, suna ta buguna.
16 Suka wahalshe ni, suka yi mini dariya, Suna hararata da ƙiyayya.
17 Sai yaushe, za ka duba, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da ni daga farmakinsu, Ka ceci raina daga waɗannan zakoki!
18 Sa'an nan zan yi maka godiya a gaban babban taron jama'a. Zan yabe ka a gaban babban taro.
19 Kada ka bar maƙiyana, maƙaryatan nan, su ga fāɗuwata! Kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, Su ƙyaface ni, su yi murna saboda baƙin cikina!
20 Ba su yin maganar zumunci, A maimakon haka sukan ƙaga ƙarairayi a kan masu ƙaunar limana.
21 Sukan zarge ni da kakkausan harshe, Su ce, “Mun ga abin da ka yi!”
22 Amma kai, ya Ubangiji ka ga wannan. Saboda haka kada ka ƙyale su, ya Ubangiji, Kada ka yi nisa!
23 Ka tashi, ya Ubangiji, ka kāre ni. Ya Allah ka tashi, ka bi mini hakkina.
24 Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, ka shaida rashin laifina, Kada ka bar maƙiyana su ƙyaface ni, ya Allahna!
25 Kada ka bar su su ce wa kansu, “Madalla! Da ma abin da muke so ke nan!” Kada ka bar su su ce, “Mun rinjaye shi!”
26 Ka sa waɗanda suka ƙyaface ni a wahalata, A rinjaye su, su ruɗe. Ka sa waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni, Su sha kunya da wulakanci!
27 Ka sa waɗanda suke murna da kuɓutata Su yi ta sowa ta murna, suna cewa, “Ubangiji mai girma ne! Yana murna da cin nasarar bawansa!”
28 Sa'an nan zan yi shelar adalcinka, Dukan yini kuwa zan yi ta yabonka.
1 Zunubi yakan yi magana da mugun daga can gindin zuciyarsa, Yakan ƙi Allah, ba ya jin tsoronsa.
2 Domin yana ganin kansa shi wani abu ne, A tsammaninsa Allah ba zai tona asirinsa ba, Ya hukunta zunubinsa.
3 Maganarsa mugunta ce cike da ƙarairayi, Ba shi da sauran isasshiyar hikima da zai aikata nagarta.
4 Yana ƙulla mugunta lokacin da yake kwance a gadonsa, Halinsa ba shi da kyau, Ba ya ƙin abin da yake mugu.
5 Madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ta kai har sammai, Amincinka ya kai sararin sammai.
6 Adalcinka kafaffe ne, Kamar manyan duwatsu. Hukuntanka kamar teku mai zurfi suke. Ya Ubangiji, kai kake lura da mutane da dabbobi.
7 Ina misalin darajar madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji! Mutane sukan sami mafaka a ƙarƙashin fikafikanka.
8 Sukan yi biki da yalwataccen abincin da yake Haikalinka, Kakan shayar da su daga koginka na alheri.
9 Kai ne mafarin dukan rai, Saboda haskenka ne kuma, muke ganin haske,
10 Ka yi ta ƙaunar waɗanda suka san ka, Ka yi wa adalai alheri.
11 Kada ka bar masu girmankai su fāɗa mini, Kada ka bar mugaye su kore ni.
12 Dubi inda mugaye suka fāɗi! Can suka kwanta, ba su iya tashi.
1 Kada ka damu saboda mugaye, Kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.
2 Za su shuɗe kamar busasshiyar ciyawa, Za su mutu kamar yadda tsire-tsire suke bushewa.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka aikata nagarta, Ka zauna a ƙasar, ka sami lafiya.
4 Ka nemi farin cikinka a wurin Ubangiji, Zai kuwa biya maka bukatarka.
5 Ka miƙa kanka ga Ubangiji, Ka dogara gare shi, zai kuwa taimake ka.
6 Zai sa nagartarka ta haskaka kamar haske, Adalcinka kuma yă haskaka kamar tsakar rana.
7 Ka natsu a gaban Ubangiji, Ka yi haƙuri, ka jira shi, Kada ka damu da waɗanda suke da dukiya, Ko su da suka yi nasara da aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Kada ka yi fushi, kada ka hasala! Kada ka damu! Gama ba zai yi maka amfanin kome ba.
9 Waɗanda suka dogara ga Ubangiji, Za su yi zamansu lafiya a ƙasar, Amma za a kori mugaye.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci mugaye za su shuɗe, Za ka neme su, amma ba za a same su ba,
11 Amma masu ladabi za su zauna lafiya a ƙasar, Su ji daɗin cikakkiyar salama.
12 Mugu yakan yi wa mutumin kirki makarƙashiya, Yana harararsa da ƙiyayya.
13 Ubangiji yana yi wa mugu dariya, Domin Ubangiji ya sani ba da daɗewa ba mugun zai hallaka.
14 Mugaye sun zare takuba, Sun tanƙware bakkunansu Don su kashe matalauta da masu bukata, Su karkashe mutanen kirki.
15 Amma takubansu za su sassoke su, Za a kakkarya bakkunansu.
16 Ƙanƙanen abin da mutumin kirki yake da shi, Ya fi dukan dukiyar mugaye amfani,
17 Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu, Amma zai kiyaye mutanen kirki.
18 Ubangiji yana kula da masu yi masa biyayya, Ƙasar kuwa za ta zama tasu har abada.
19 Ba za su sha wahala a lokacin tsanani ba, Za su sami yalwa a lokacin yunwa.
20 Amma mugaye za su mutu, Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji, Za su ɓace kamar hayaƙi.
21 Mugu yakan ci bashi, yă ƙi biya, Amma mutumin kirki mai alheri ne, Mai bayarwa hannu sake.
22 Waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka, Za su zauna lafiya lau a ƙasar, Amma waɗanda ya la'anta Za a kore su su fita.
23 Ubangiji yakan bi da mutum lafiya A hanyar da ya kamata yă bi, Yakan ji daɗin halinsa,
24 In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba, Gama Ubangiji zai taimake shi Yă tashi tsaye.
25 Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne, Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba, Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.
26 A koyaushe yakan bayar a sake, Yana ba da rance ga waɗansu, 'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.
27 Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta, Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada,
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai, Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa, Yana kiyaye su koyaushe, Amma za a kori zuriyar mugaye.
29 Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar, Su gāje ta har abada.
30 Kalmomin mutumin kirki suna da hikima, Yana faɗar abin da yake daidai.
31 Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.
32 Mugu yakan yi fakon mutumin kirki, Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,
33 Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba, Ko kuwa yă bari a kāshe shi Sa'ad da ake masa shari'a.
34 Ka sa zuciyarka ga Ubangiji Ka kiyaye dokokinsa, Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar, Za ka kuwa ga an kori mugaye.
35 Na ga wani mugu, azzalumi, Ya fi kowa tsayi, Kamar itacen al'ul na Lebanon,
36 Amma bayan ƙanƙanen lokaci, Da na zaga, ban gan shi ba, Na neme shi, amma ban same shi ba.
37 Dubi mutumin kirki, ka lura da adali, Mutumin salama yakan sami zuriya,
38 Amma za a hallaka masu zunubi ƙaƙaf, Za a kuma shafe zuriyarsu.
39 Ubangiji yakan ceci adalai, Ya kiyaye su a lokatan wahala.
40 Yakan taimake su, yă kuɓutar da su, Yakan cece su daga mugaye, Gama sukan zo wurinsa don yă kāre su.
1 Kada ka yi fushi har ka tsauta mini, ya Ubangiji! Kada ka hukunta ni da fushinka!
2 Ka hukunta ni, ka kuwa yi mini rauni, Ka kuma buge ni har ƙasa.
3 Saboda fushinka ina ciwo mai tsanani, Duk jikina ya kamu da ciwo saboda zunubina.
4 Ina nutsewa cikin ambaliyar zunubaina, Ina jin nauyinsu, sun danne ni ƙasa.
5 Saboda wawancina, miyakuna sun ruɓe, suna wari,
6 An tanƙware ni, an ragargaza ni, Ina ta kuka dukan yini.
7 Ina fama da zazzaɓi, Ina rashin lafiya ƙwarai.
8 An ragargaza ni sarai, an kuwa ci nasara a kaina, Na damu a zuciyata, ina nishi don zafi.
9 Ka san bukatata, ya Ubangiji, Kana jin dukan nishe-nishena.
10 Zuciyata tana ɗar, ƙarfina ya ƙāre, Idanuna sun dushe.
11 Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna, Har iyalina ma sun guje mini.
12 Masu son kashe ni, sun haƙa mini tarkuna, Masu so su cuce ni, suna barazanar lalatar da ni, Yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 Kamar kurma nake, ba na iya ji, Kamar kuma bebe, ba na iya magana.
14 Ni kamar mutumin da ba ya iya amsawa nake, don ba na ji.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji, Kai za ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna.
16 Kada ka bar magabtana su yi murna saboda wahalata. Kada ka bar su su yi kirari a kan faɗuwata!
17 Ina gab da fāɗuwa, Ina cikin azaba kullum.
18 Na hurta zunubaina, Sun cika ni da taraddadi.
19 Magabtana lafiyayyu ne masu ƙarfi. Waɗanda yake ƙina ba dalili, suna da yawa.
20 Masu rama nagarta da mugunta, Suna gāba da ni, Domin ina ƙoƙarin aikata abin da yake daidai.
21 Kada ka yashe ni, ya Ubangiji, Kada ka rabu da ni, ya Allahna!
22 Sai ka taimake ni yanzu, ya Ubangiji, Mai Cetona!
1 Na ce, “Zan yi hankali da abin da nake yi, Don kada harshena yă sa ni zunubi, Ba zan ce kome ba sa'ad da mugaye suke kusa.”
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da suke da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi,
3 Zuciyata kuwa ta cika da taraddadi, Bisa ga yawan tunanina, haka yawan wahalata zai zama, Dole ne in yi ta tambaya,
4 “Ya Ubangiji, kwana nawa zan yi a duniya? Yaushe zan mutu? Ka koya mini ranar da ajalina zai auko.
5 “Ga shi, ka gajerta yawan kwanakina! Yawan kwanakina a wurinka kamar ba kome ba ne. Hakika duk mutum mai rai, Bai fi shaƙar iska ba.
6 Bai kuma fi inuwa ba! Duk abin da yake yi banza ne, Yakan tara dukiya, amma bai san wanda zai more ta ba!
7 “A kan me zan sa zuciya, ya Ubangiji? A gare ka nake dogara.
8 Ka cece ni daga dukan zunubaina, Kada ka bar wawaye su yi mini ba'a.
9 Zan yi shiru, ba zan ce kome ba, Saboda ka sa na sha wahala haka.
10 Kada ka ƙara hukunta ni! Na kusa mutuwa saboda bugun da kake yi mini!
11 Kakan hukunta zunuban mutum ta wurin tsautawarka, Kamar yadda asu yake lalata abu. Hakika mutum bai fi shaƙar iska ba!
12 “Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka kuma kasa kunne ga roƙona, Kada ka yi shiru sa'ad da na yi kuka gare ka! Yadda dukan kakannina suka yi, Ni baƙonka ne na ɗan lokaci.
13 Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai, Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”
1 Na yi ta jiran taimakon Ubangiji, Sa'an nan ya kasa kunne gare ni, ya ji kukana.
2 Ya fisshe ni daga rami mai hatsari! Ya aza ni a kan dutse lafiya lau. Ya kawar mini da tsoro.
3 Ya koya mini raira sabuwar waƙa, Waƙar yabon Allahnmu. Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata, Za su kuwa dogara ga Ubangiji.
4 Mai farin ciki ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, Wanda bai juya ga gumaka ba, Ko ya haɗa kai da masu sujada ga allolin karya.
5 Ka yi mana abubuwa masu yawa, ya Ubangiji Allahna. Ba wani kamarka! Idan na yi ƙoƙari in faɗe su duka, Sun fi ƙarfin in faɗa.
6 Ba ka bukatar baye-baye da hadayu, Ba ka so a miƙa maka hadayun ƙonawa Na dabbobi a bisa bagade ba, Ko baya-baye don a kawar da zunubai. A maimakon haka, ka ba ni kunnuwan da zan saurare ka.
7 Sai na amsa, “Ga ni, umarnanka zuwa gare ni Suna a Littafin Shari'a.
8 Ina ƙaunar in aikata nufinka sosai, ya Allah! Ina riƙe da koyarwarka a zuciyata.”
9 A taron dukan jama'arka, ya Ubangiji, Na ba da albishir na cetonka. Ka sani ba zan fasa hurta shi ba.
10 Ban riƙe labarin cetonka don kaina kaɗai ba, Nakan yi maganar amincinka, da taimakonka a koyaushe. Ba na yin shiru a taron dukan jama'arka, Amma ina ta shaida madawwamiyar ƙaunarka da amincinka.
11 Ya Ubangiji, na sani ba za ka fasa yi mini jinƙai ba! Ƙaunarka da amincinka za su kiyaye lafiyata kullum.
12 Wahalai iri iri sun kewaye ni, har ba su ƙidayuwa! Alhakin zunubaina ya tarar da ni, Har ba na iya gani, Sun fi gashin kaina yawa, na karaya.
13 Ka cece ni, ya Allah, Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
14 Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina Su koma baya, su sha kunya!
15 Ka sa waɗanda suke mini ba'a Su razana sabili da faɗuwarsu!
16 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka Su yi murna, su yi farin ciki! Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”
17 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki, Ya Allah, ka zo wurina da hanzari. Kai ne mataimakina da Mai Cetona, Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!
1 Mai farin ciki ne wanda yake kula da matalauta, Ubangiji zai taimake shi sa'ad da yake shan wahala.
2 Ubangiji zai kiyaye shi, yă keɓe ransa. Ubangiji zai sa yă ji daɗi a ƙasar, Ba zai bar shi a hannun magabtansa ba.
3 Ubangiji zai taimake shi sa'ad da yake ciwo Ya mayar masa da lafiyarsa.
4 Na ce, “Na yi maka zunubi, ya Ubangiji, Ka yi mini jinƙai ka warkar da ni!”
5 Magabtana suna mugayen maganganu a kaina, Suna cewa, “Yaushe ne zai mutu a manta da shi?”
6 Masu zuwa su gaishe ni ba da zuciya ɗaya suke zuwa ba, Sukan tattara duk mugun labari a kaina Sa'an nan su je su yi ta bazawa ko'ina.
7 Maƙiyana duk suna raɗa da junansu a kaina, Sukan ɗauka na fi kowa mugunta.
8 Suna cewa, “Yana ciwon ajali, Ba zai taɓa tashi daga gadonsa ba.”
9 Har da shaƙiƙin abokina, Wanda na fi amincewa da shi. Wanda muke ci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 Ka ji ƙaina ya Ubangiji, ka maido mini da lafiyata, Zan kuwa sāka wa magabtana!
11 Zan sani kana jin daɗina, Domin ba za su rinjaye ni ba,
12 Za ka taimake ni domin ina yin abin da yake daidai, Za ka sa ni a gabanka har abada.
13 Bari mu yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila. Ku yabe shi yanzu da har abada! Amin! Amin!
1 Kamar yadda kishimi yake marmarin ruwan sanyi daga rafi, Haka nake marmarinka, ya Allah.
2 Ina jin ƙishinka, ya Allah, ya Allah Mai Rai, Yaushe zan tafi in yi sujada a gabanka?
3 Dare da rana ina kuka, Hawayena kaɗai su ne abincina, A kowane lokaci maƙiyana suna ta tambayata, “Ina Allahnka?”
4 Zuciyata takan ɓaci in na tuna da abin da ya wuce, Sa'ad da nakan tafi tare da taron jama'a zuwa Haikalin Allah, Ina bishe su a jere. Taron jama'a masu farin ciki, suna raira waƙa, Suna ta da murya, suna yabon Allah.
5 Me ya sa nake baƙin ciki haka? Me ya sa nake damuwa ƙwarai? Zan dogara ga Allah, Zan sāke yin yabonsa, Mai Cetona, Allahna.
6 Zuciyata ta karai Saboda haka zan tuna da kai A wajen Urdun, da kusa da Dutsen Harmon, da na Mizar, Zan tuna da kai.
7 Zurfafan tekuna suna kiran junansu, Matsirgar ruwa na Allah kuwa suna ta ruri! Igiyoyin ruwa na baƙin ciki Suka yi wa raina ambaliya.
8 Ubangiji ya nuna madawwamiyar ƙaunarsa kowace rana! Ni ma in raira yabo gare shi kowane dare, In yi addu'a ga Allah, wanda ya ba ni rai.
9 Ga Allah wanda yake tsarona na ce, “Me ya sa ka manta da ni? Me ya sa nake ta shan wahala Saboda muguntar maƙiyana?”
10 An ragargaza ni da zargin maƙiyana Waɗanda suke tambayata kullum, “Ina Allahnka?”
11 Me ya sa ni ɓacin rai haka? Me ya sa ni damuwa? Zan dogara ga Allah. Har yanzu ma zan yabe shi, Mai Cetona, Allahna.
1 Ya Allah, ka kuɓutar da ni, Ka kiyaye al'amarina daga marasa tsoronka, Ka cece ni daga ƙaryar mugaye!
2 Ya Allah, kai ne kake kāre ni, Me ya sa ka yashe ni? Me ya sa nake ta shan wahala saboda muguntar maƙiyana?
3 Ka aiko da haskenka, da gaskiyarka, Bari su bishe ni, Su kawo ni Sihiyona, tsattsarkan tudunka, Su kawo ni Haikalinka, inda zatinka yake!
4 Sa'an nan zan tafi wurin bagadenka, ya Allah, Zuwa gare ka, kai wanda kake sa ni in yi murna da farin ciki, In raira waƙar yabo a gare ka da garayata, Ya Allah, Allahna!
5 Me ya sa nake baƙin ciki? Me ya sa nake damuwa? Zan dogara ga Allah, Zan ƙara yabonsa, Mai Cetona, Allahna.
1 Da kunnuwanmu muka ji, ya Allah, Kakanninmu suka faɗa mana, Manya manyan abubuwa da ka aikata a lokacinsu, A zamanin dā,
2 Yadda kai da kanka ka kori arna, Ka dasa jama'arka a ƙasarsu, Yadda ka hori sauran al'umma, Amma ka sa jama'arka su wadata.
3 Ba da takubansu suka ci ƙasar ba, Ba kuwa da ikonsu suka rinjayi ƙasar ba, Amma da ikonka ne da kuma ƙarfinka, Ta wurin tabbatar musu kana tare da su, Kana nuna musu kana ƙaunarsu.
4 “Ya Allah, kai ne Sarkina, Ka ba jama'arka nasara.
5 Da ikonka muka kori abokan gābanmu, Saboda kasancewarka tare da mu Muka rinjayi magabtanmu.
6 Ban dogara ga bakana ba, Takobina kuwa ba zai cece ni ba.
7 Amma ka cece mu daga abokan gābanmu, Ka kori waɗanda suke ƙinmu.
8 Za mu yabe ka kullum, Mu yi maka godiya har abada.”
9 Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu, Ka bari aka kore mu, Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba.
10 Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu, Suka ƙwace abin da muke da shi.
11 Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki, Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa.
12 Ka sayar da jama'arka A bakin 'yan kuɗi ƙalilan, Ba ka ci ribar cinikin ba.
13 Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai, Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.
14 Ka maishe mu abin raini a wurin arna, Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.
15 Kullum a cikin kunya nake, Kunya ta lulluɓe ni ɗungum,
16 Saboda dukan wulakanci, Da zagin da nake sha daga maƙiyana da abokan gābana.
17 Dukan wannan ya same mu, Ko da yake ba mu manta da kai ba, Ba mu kuma ta da alkawarin da ka yi da mu ba.
18 Ba mu ci amanarka ba, Ba mu ƙi yin biyayya da umarnanka ba.
19 Duk da haka ka ƙi taimakonmu da namomin jejin nan, Ka bar mu a cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Da a ce mun daina yin sujada ga Allahnmu, Muka yi addu'a ga gumaka,
21 Hakika ka gane, Domin ka san asirin tunanin mutane.
22 Ya Allah, saboda kai ne ake karkashe mu a kowane lokaci, Ake kuma maishe mu kamar tumakin da za a yanyanka.
23 Ka tashi, ya Ubangiji! Me ya sa kake zama kamar mai barci? Ka tashi! Kada ka yashe mu har abada!
24 Me ya sa ka ɓuya mana? Kada ka manta da ƙuncinmu da wahalarmu!
25 Mun fāɗi, an turmushe mu a ƙasa, An bar mu kwance cikin ƙura.
26 Ka tashi ka taimake mu! Ka fanshe mu saboda madawwamiyar ƙaunarka!
1 Kwanyata ta cika da kyawawan kalmomi, Lokacin da nake tsara waƙar sarki, Harshena kuwa kamar alkalami ne na ƙwararren marubuci.
2 Kai ne mafi kyau a cikin dukan mutane, Kai mai kyakkyawan lafazi ne, Kullum Allah yakan sa maka albarka!
3 Ka sha ɗamara da takobinka, ya Maɗaukakin Sarki, Kai mai iko ne, Maɗaukaki!
4 Ka yi hawan ɗaukaka zuwa nasara, Domin ka tsare gaskiya da adalci. Saboda ikonka za ka yi babban rinjaye.
5 Kibanka suna da tsini, Suna huda zuciyar abokan gābanka, Al'ummai suna fāɗuwa ƙasa a ƙafafunka.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai dawwama har abada abadin! Kana mulkin mallakarka da adalci.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai, Kana ƙin abin da yake mugu. Saboda haka Allah, Allahnka, ya zaɓe ka, Ya kuwa kwararo maka farin ciki mai yawa fiye da kowa.
8 Tufafinka suna ƙanshin turaren mur, da na aloyes, da na kashiya, A kowace fādar hauren giwa, mawaƙa suna yi maka waƙar.
9 Daga cikin matan da suke fadarka, har da 'ya'yan sarakuna. A daman kursiyinka kuwa ga sarauniya a tsaye. Tana saye da kayan ado na zinariya mafi kyau duka.
10 Ki ji abin da zan faɗa, ya ke amaryar sarki, Ki manta da mutanenki da danginki.
11 Saboda ke kyakkyawa ce sarki zai so ki, Shi ne maigidanki, sai ki yi masa biyayya.
12 Mutanen Taya za su kawo miki kyautai, Attajirai za su zo su sami farin jini a gare ki.
13 Gimbiya tana fāda, kyakkyawa ce ainun, Da zaren zinariya aka saƙa rigarta,
14 Aka kai ta wurin sarki tana saye da riga mai ado. Ga 'yan matanta a biye, Aka kawo su wurin sarki.
15 Da farin ciki da murna suka zo, Suka shiga fādar sarki.
16 Za ka haifi 'ya'ya maza da yawa, Waɗanda za su maye matsayin kakanninka, Za ka sa su zama masu mulkin duniya duka.
17 Waƙata za ta sa a yi ta tunawa da sunanka har abada, Dukan jama'a za su yabe ka a dukan zamanai masu zuwa.
1 Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, Ko da duniya za ta girgiza, Duwatsu kuma su fāɗa cikin zurfafan teku,
3 Ko da a ce tekuna za su yi ruri su tumbatsa, Tuddai kuma su girgiza saboda tangaɗin tekun.
4 Akwai kogin da yake kawo farin ciki a birnin Allah, Da cikin tsattsarkan Haikali na Maɗaukaki.
5 Allah yana zaune cikin birnin, Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau. Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa.
6 An kaɓantar da sauran al'umma, mulkoki suka girgiza, Allah ya yi tsawa, duniya kuwa ta narke.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!
8 Zo ku ga abin da Ubangiji ya yi! Dubi irin ayyukan al'ajabi da ya yi a duniya!
9 Ya hana yaƙoƙi ko'ina a duniya, Yana karya bakkuna, yana lalatar da māsu, Yana ƙone karusai da wuta.
10 Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah, Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma, Maɗaukaki kuma a duniya!”
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!
1 Ku yi tāfi saboda farin ciki, Ya ku jama'a duka! Ku raira waƙoƙi da karfi, ku yabi Allah!
2 A ji tsoron Ubangiji Mai Iko Dukka, Shi babban Sarki ne, ya mallaki dukan duniya.
3 Ya ba mu nasara a bisa jama'o'i, Ya sa muka yi mulkin al'ummai,
4 Ya zaɓar mana ƙasar da muke zaune, Wadda take mallaka ce ta fāriya, ta jama'arsa Wadda yake ƙauna.
5 Allah ya hau kan kursiyinsa! Aka yi ta sowa ta murna, ana ta busa ƙahoni, Lokacin da Ubangiji yake hawa!
6 Ku raira yabbai ga Allah, Ku raira yabbai ga sarkinmu!
7 Allah sarki ne na duniya duka, Ku yabe shi da waƙoƙi!
8 Allah yana zaune kan kursiyinsa mai tsarki, Yana mulkin al'ummai,
9 Masu mulkin al'ummai suka tattaru Tare da jama'ar Allah na Ibrahim. Allah shi ne garkuwar jarumawa, Yana mulkin duka!
1 Ubangiji mai girma ne, Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu, A kan tsattsarkan dutsensa.
2 Dutsen Sihiyona, dutse mai tsawo, Mai kyan gani ne na Allah, Birnin babban Sarki. Yakan kawo farin ciki ga dukan duniya!
3 Allah ya nuna akwai zaman lafiya a wurinsa, A kagarar birnin.
4 Sarakuna suka tattaru, Suka zo Dutsen Sihiyona,
5 Da suka gan shi sai suka yi mamaki, Suka tsorata suka gudu.
6 Tsoro ya kama su suka razana, Kamar mace wadda take gab da haihuwa.
7 Allah yakan hallaka manyan jiragen ruwa da iskar gabas.
8 Mun ji labarin waɗannan al'amura, Yanzu kuwa mun gan su A birnin Allahnmu, Mai Runduna, Zai kiyaye birnin lafiya har abada.
9 A cikin Haikalinka, ya Allah, Muna tunanin madawwamiyar ƙaunarka.
10 A ko'ina jama'a suna yabonka, Sunanka ya game duniya duka. Kana mulki da adalci.
11 Bari jama'ar Sihiyona su yi murna! Gama kana shari'a ta gaskiya, Bari biranen Yahuza su yi farin ciki.
12 Ku tafi ku kewaye Dutsen Sihiyona, Ku ƙirga yawan hasumiyarsa.
13 Ku lura da garukanta, ku bincike kagaranta, Saboda ku iya faɗa wa tsara mai zuwa,
14 Cewa wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin, Shi ne zai bishe mu a dukan zamanai masu zuwa.
1 Ku ji wannan, ko wannenku, Ku saurara jama'a duka na ko'ina,
2 Da manya da ƙanana duka ɗaya, Da attajirai da matalauta baki ɗaya.
3 Zan yi magana da hikima, Zan yi tunani mai ma'ana.
4 Zan mai da hankalina ga ka-cici-ka-cici, In bayyana ma'anarsa sa'ad da nake kaɗa molo.
5 Don me zan ji tsoro a lokacin hatsari, Sa'ad da mugaye suka kewaye ni,
6 Mutanen da suke dogara ga dukiyarsu, Waɗanda suke fariya saboda yawan wadatarsu?
7 Har abada mutum ba zai iya fansar wani ba, Ba kuwa zai iya biyan kuɗin ransa ga Allah ba.
8 Gama kuɗin biyan ran mutum ba shi da iyaka. Abin da zai iya biya, sam ba zai isa ba,
9 Ba kuwa zai rayar da shi, Ko ya hana shi mutuwa har abada ba.
10 Yakan sa masu hikima su ma su mutu, Haka nan ma wawaye da mutanen banza, Za su mutu su bar dukiyarsu ga zuriyarsu.
11 Kaburburansu za su zama gidajensu har abada, Can za su kasance kullum, Ko da yake a dā suna da ƙasa ta kansu.
12 Girman mutum ba zai hana shi mutuwa ba, Zai mutu kamar dabba.
13 Dubi abin da zai faru ga waɗanda suke dogara ga kansu, Da irin ƙaddarar waɗanda dukiya ta ishe su.
14 Za a ƙaddara su ga mutuwa kamar tumaki, Mutuwa ce za ta yi kiwonsu. Da safe adalai za su ci nasara a kansu, Sa'ad da gawawwakinsu suke ruɓewa a ƙasar matattu, Nesa da gidajensu.
15 Amma Allah zai fanshe ni, Zai ɗauke ni daga ikon mutuwa.
16 Kada ka damu sa'ad da mutum ya zama attajiri, Ko kuwa dukiyarsa ta ƙasaita,
17 Domin ba zai ɗauke ta a lokacin mutuwarsa ba, Dukiyarsa ba za ta shiga kabari tare da shi ba.
18 Ko da a ce mutum ya sami falalar wannan rai, Ana kuwa ta yabonsa saboda nasarar da ya ci,
19 Duk da haka zai tarar da kakanninsa waɗanda suka mutu, Inda duhu ya dawwama har abada.
20 Girman mutum ba zai hana shi mutuwa ba, Zai mutu kamar dabba.
1 Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana, Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma.
2 Allah yana haskakawa daga Sihiyona, Da cikar jamalin Sihiyona.
3 Allahnmu ya zo, ba a ɓoye yake ba, Wuta mai cinyewa na tafe a gabansa, Babban hadiri kuwa na kewaye da shi.
4 Ya kira sammai da duniya su zama shaidu, Su ga yadda yake shara'anta jama'arsa.
5 Ya ce, “Ku tattaro mini amintattuna, Waɗanda suka cika alkawarin da yake tsakanina da su, Ta wurin miƙa hadaya.”
6 Sammai suna shelar adalcin Allah, Domin shi yake yin shari'a!
7 “Ku ji, ya ku jama'ata, zan kuwa yi magana, Zan ba da shaida gāba da ku, ya Isra'ila. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Ban tsauta muku saboda hadayunku ba, Ko saboda hadayu na ƙonawa da kuke ta miƙa mini kullum.
9 Ba na bukatar bijimai daga gonakinku, Ko awaki daga garkunanku.
10 Gama namomin jeji nawa ne, Dubban shanu da suke kan tuddai kuma nawa ne.
11 Dukan tsuntsayen da suke tashi a sararin sama nawa ne, Da dukan masu rai da suke ƙasa.
12 “Da ina jin yunwa ba sai na faɗa muku ba, Gama da duniya da dukan abin da yake cikinta nawa ne.
13 Nakan ci naman bijimai ne? Ko nakan sha jinin awaki?
14 Bari ku miƙa wa Allah hadayarku ta godiya, Ku ba Mai Iko Dukka, dukan hadayun da kuka alkawarta.
15 Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.”
16 Amma Allah ya ce wa mugaye, “Don me za ku haddace umarnaina? Don me za ku yi magana a kan alkawaraina?
17 Kun ƙi in tsauta muku, Kun yi watsi da umarnaina.
18 Sa'ad da kuka ga ɓarawo kukan yi abuta da shi. Kuna haɗa kai da mazinata.
19 “Kullum a shirye kuke ku hurta mugunta, Ba ku jin nauyin faɗar ƙarya.
20 A shirye kuke ku sari 'yan'uwanku, Ku sa musu laifi.
21 Kun aikata waɗannan duka, ni kuwa ban ce kome ba, Saboda haka kuka zaci ni kamar ku nake. Amma yanzu zan tsauta muku, In bayyana muku al'amarin a fili.
22 “Ku ji wannan ku da kuke ƙyale ni, In ba haka ba zan hallaka ku, Ba wanda zai cece ku.
23 Wanda yake yin godiya a sa'ad da yake miƙa hadayarsa, yana girmama ni, Da wanda yake yi mini biyayya kuma, zan nuna masa cetona.”
1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, Sabili da madawwamiyar ƙaunarka. Ka shafe zunubaina, Saboda jinƙanka mai girma!
2 Ka wanke muguntata sarai, Ka tsarkake ni daga zunubina!
3 Na gane laifina, Kullum ina sane da zunubina.
4 Na yi maka zunubi, kai kaɗai na yi wa, Na kuwa aikata mugunta a gare ka. Daidai ne shari'ar da ka yi mini, Daidai ne ka hukunta ni.
5 Mugu ne ni tun lokacin da aka haife ni, Mai zunubi ne ni tun daga ranar da aka haife ni.
6 Amintacciyar zuciya ita kake so, Ka cika tunanina da hikimarka.
7 Ka kawar da zunubina, zan kuwa tsarkaka, Ka wanke ni, zan kuwa fi auduga fari.
8 Bari in ji sowa ta farin ciki da murna. Ko da yake ka ragargaza ni, Ka kakkarya ni, duk da haka zan sāke yin murna.
9 Ka kawar da fuskarka daga zunubaina, Ka shafe duk muguntata.
10 Ka halitta tsarkakakkiyar zuciya a cikina, ya Allah, Ka sa sabon halin biyayya a cikina.
11 Kada ka kore ni daga gabanka, Kada ka ɗauke mini Ruhunka Mai Tsarki.
12 Ka sāke mayar mini da farin ciki na cetonka, Ka ƙarfafa ni da zuciya ta biyayya.
13 Sa'an nan zan koya wa masu zunubi umarnanka, Za su kuwa komo wurinka.
14 Ka rayar da raina, ya Allah Mai Cetona, Zan kuwa yi shelar adalcinka da farin ciki.
15 Ka taimake ni in yi magana, ya Ubangiji, Zan kuwa yabe ka.
16 Ba ka son sadakoki, ai, da na ba ka, Ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 Hadayata, ita ce halin ladabi, ya Allah, Zuciya mai ladabi da biyayya, Ba za ka ƙi ba, ya Allah.
18 Ya Allah, ka yi wa Sihiyona alheri, ka taimake ta, Ka sāke gina garun Urushalima.
19 Sa'an nan za ka ji daɗin hadaya ta ainihi, Da dukan hadayun ƙonawa. Za a miƙa bijimai hadayu a bisa bagadenka.
1 Me ya sa kake fariya da muguntarka, Ya kai, babban mutum? Ƙaunar Allah tana nan a koyaushe.
2 Kana shirya maƙarƙashiya don ka lalatar da waɗansu, Harshenka kamar aska mai kaifi yake. Kana ƙirƙiro ƙarairayi kullum.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da nagarta, Kana kuwa ƙaunar faɗar ƙarya fiye da gaskiya.
4 Kana jin daɗin cutar mutane da maganganunka, Ya kai, maƙaryaci!
5 Don haka Allah zai ɓata ka har abada, Zai kama ka, yă jawo ka daga alfarwarka, Zai kawar da kai daga ƙasar masu rai.
6 Adalai za su ga wannan, su ji tsoro, Za su yi maka dariya, su ce,
7 “Duba, ga mutumin da bai dogara ga Allah Don ya sami zaman lafiyarsa ba. A maimakon haka, sai ya dogara ga wadatarsa. Yana neman zaman lafiyarsa ta wurin muguntarsa.”
8 Amma ni, kamar itacen zaitun nake, wanda yake girma kusa da Haikalin Allah, Ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa har abada abadin.
9 Zan gode maka, ya Ubangiji, Saboda abin da ka aikata. Zan dogara gare ka, Sa'ad da nake sujada tare da jama'arka, Domin kai mai alheri ne.
1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah.” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.
2 Daga Sama Allah ya dubi mutane, Ya ga ko akwai masu hikima Waɗanda suke yi masa sujada.
3 Amma dukansu sun koma baya, Su duka mugaye ne, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai, Babu ko ɗaya.
4 Allah ya ce, “Ashe, ba su sani ba? Ashe, mugayen nan jahilai ne? Ta wurin yi wa jama'ata fashi suke rayuwa, Ba sa yin addu'a gare ni.”
5 Amma sa'an nan za su firgita ƙwarai, Irin yadda ba su taɓa yi ba, Gama Allah ya warwatsa ƙasusuwan maƙiyanka. Ya kore su sarai, saboda ya ƙi su.
6 Dā ma ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona! Sa'ad da Allah ya sāke arzuta jama'arsa, Zuriyar Yakubu za ta yi farin ciki, Jama'ar Isra'ila kuwa za ta yi murna.
1 Ka cece ni ta wurin ikonka, ya Allah, Ka cece ni ta wurin ƙarfinka!
2 Ka ji addu'ata, ya Allah, Ka saurari kalmomina!
3 Masu girmankai sun tasar mini, Mugaye suna nema su kashe ni, Mutanen da ba su kula da Allah ba.
4 Na sani Allah ne mai taimakona, Na sani Ubangiji shi ne mai tsarona!
5 Ubangiji ya hukunta wa maƙiyana da irin muguntarsu! Gama zai hallaka su saboda shi mai aminci ne.
6 Da murna zan miƙa maka hadaya, Zan yi maka godiya, ya Ubangiji, Domin kai mai alheri ne.
7 Ka cece ni daga dukan wahalaina, Na kuwa ga an kori maƙiyana.
1 Ka ji addu'ata, ya Allah, Kada ka ƙi jin roƙona!
2 Ka saurare ni, ka amsa mini, Gama damuwata ta gajiyar da ni tiƙis.
3 Hankalina ya tashi saboda yawan kurarin maƙiyana, Saboda danniyar mugaye. Sukan jawo mini wahala, Suna jin haushina suna ƙina.
4 Azaba ta cika zuciyata, Tsorace-tsoracen mutuwa sun yi mini nauyi.
5 Tsoro da rawar jiki sun kama ni, Na cika da razana.
6 Na ce, “Da a ce ina da fikafikai kamar kurciya, Da sai in tashi, in tafi, in nemi wurin hutawa!
7 In tafi can nesa, In yi wurin zamana a hamada.
8 Zan hanzarta in nemi mafaka Daga iska mai ƙarfi da hadiri.”
9 Ka hallaka su, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, Gama na ga hargitsi da tawaye a birni.
10 Dare da rana suna ta yawo a kan garu suna ta kewaye birnin, Birnin kuwa cike yake da laifi da wahala.
11 Akwai hallaka a ko'ina, Tituna suna cike da azzalumai da 'yan danfara.
12 Da a ce maƙiyina ne yake mini ba'a, Da sai in jure. Da a ce abokin gābana ne yake shugabancina, Da sai in ɓuya masa.
13 Amma kai ne, aminina, Abokin aikina ne, abokina ne kuma!
14 Dā mukan yi taɗi da juna ƙwarai, Mukan tafi Haikali tare da sauran jama'a.
15 Allah ya sa mutuwa ta auko wa maƙiyana ba labari, Allah ya sa su gangara ƙasar matattu da ransu! Mugunta tana cikin gidajensu da zukatansu.
16 Amma ina kira ga Allah, yă taimake ni, Ubangiji kuwa zai cece ni.
17 Koke-kokena da nishe-nishena Suna hawa zuwa gare shi da safe, da tsakar rana, da dad dare, Zai kuwa ji muryata.
18 Zai fisshe ni lafiya Daga yaƙe-yaken da nakan yi da magabtana masu yawa.
19 Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal, Zai ji ni, zai kore su. Ba abin da suka iya yi a kai, Domin ba su tsoron Allah.
20 Abokina na dā, Ya yi wa abokansa faɗa, Ya ta da alkawarinsa.
21 Kalmominsa sun fi mai taushi, Amma ƙiyayya tana a zuciyarsa, Kalmominsa sun fi mai sulɓi, Amma suna yanka kamar kakkaifan takobi.
22 Ka gabatar da wahalarka ga Ubangiji, Zai kuwa taimake ka, Ba zai bari a ci nasara a kan mutumin kirki ba, faufau.
23 Amma kai, ya Allah, za ka jefar da masu kisankai, da maƙaryata can ƙasa cikin zurfafa, Kafin su kai rabin kwanakinsu a duniya. Amma ni, zan dogara gare ka.
1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, Gama mutane sun tasar mini, Maƙiyana suna tsananta mini koyaushe!
2 Dukan yini maƙiyana suna tasar mini, Waɗanda suke faɗa da ni sun cika yawa.
3 Sa'ad da nake jin tsoro, ya Maɗaukaki, A gare ka nake dogara.
4 Ga Allah nake dogara, ina yabon alkawarinsa, Gare shi na dogara, ba zan ji tsoro ba. Me mutum kawai zai yi mini?
5 Maƙiyana suke ta wahalshe ni dukan yini, A kan kowane abu da nake yi, Kullum suna ta tunanin yadda za su cuce ni!
6 Sukan taru a ɓoye, Suna kallon duk abin da nake yi. Suna sa zuciya za su iya kashe ni.
7 Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu, Da fushinka ka kori waɗannan mutane!
8 Ka san irin wahalar da nake sha, Kana riƙe da lissafin yawan hawayena. Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba?
9 A ranar da na yi kira gare ka, Za a komar da abokan gābana baya, Gama na sani Allah yana tare da ni!
10 Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa, Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa.
11 A gare shi nake dogara, Ba zan ji tsoro ba. Me mutum kawai zai yi mini?
12 Zan miƙa maka abin da na yi alkawari, ya Allah, Zan miƙa maka hadaya ta godiya.
13 Domin ka cece ni daga mutuwa, Ka hana a ci nasara a kaina. Saboda haka a gaban Allah nake tafiya A hasken da yake haskaka wa masu rai.
1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi jinƙai, Gama na zo gare ka neman tsira. Zan sami kāriya a ƙarƙashin fikafikanka, Sai dukan hatsari ya wuce.
2 Zan yi kira ga Allah, Maɗaukaki, Zan yi kira ga Allah, mai biyan dukan bukatata.
3 Daga sammai Allah zai amsa mini, Zai kori waɗanda suka tasar mini, Allah zai nuna mini madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa.
4 Raina yana tsakiyar zakoki, Na kwanta a tsakiyar waɗanda suka yi niyyar cinye mutane. Haƙoransu kamar māsu da kibau suke, Harsunansu masu kaifi ne kamar takobi.
5 Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!
6 Maƙiyana sun kafa tarko don su kama ni, Damuwa ta fi ƙarfina. Sun yi wushefe a kan hanyata, Amma su da kansu suka fāɗa a ciki.
7 A shirye nake, ya Allah, Na shirya sosai! Zan raira waƙoƙi in yabe ka!
8 Ka farka, ya raina! Ku farka, molona da garayata! Zan sa rana ta farka!
9 Zan gode maka a cikin sauran al'umma, ya Ubangiji! Zan yabe ka a cikin jama'a!
10 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har sammai, Amincinka kuma har sararin sammai.
11 Ka bayyana girmanka, ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!
1 Hakika za ku yanka daidai, ku manya? Za ku shara'anta wa mutane daidai?
2 A'a, tunanin muguntar da za ku aikata kaɗai kuke yi, Kuna aikata laifofin ta da hargitsi a ƙasar.
3 Mugaye, laifi suke yi dukan kwanakinsu, Tun daga ranar da aka haife su suke ta faɗar ƙarya.
4 Cike suke da dafi kamar macizai, Sukan toshe kunnuwansu kamar kuraman gamsheƙa,
5 Wanda ba ya jin muryar gardi, Ko kuma waƙar gwanin sihiri.
6 Ka kakkarya haƙoransu, ya Allah, Ka ciccire fiƙoƙin waɗannan zakoki masu zafin rai, ya Ubangiji!
7 Bari su ɓace kamar ruwan da ya tsanye, Bari a murtsuke su kamar ciyayi a hanya.
8 Bari su zama kamar katantanwu waɗanda sukan narke su yi yauƙi, Allah ya sa su zama kamar jinjirin da aka haifa matacce. Wanda bai taɓa ganin hasken rana ba.
9 Kafin tukunya ta ji zafin wuta, Da zafin fushi, Allah zai watsar da su tun suna da rai.
10 Adalai za su yi murna sa'ad da suka ga an hukunta masu zunubi, Za su wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Mutane za su ce, “Hakika an sāka wa adalai, Hakika akwai Allah wanda yake shara'anta duniya!”
1 Ka cece ni daga maƙiyana, ya Allahna, Ka kiyaye ni daga waɗanda suka tasar mini!
2 Ka cece ni daga waɗannan mugaye, Ka tsirar da ni daga masu kisankan nan!
3 Duba! Suna jira su auka mini, Mugaye suna taruwa gāba da ni, Ba domin wani zunubi ko wani laifin da na yi ba,
4 Ba domin na yi wani laifi ba, ya Ubangiji, Har da suka gaggauta gāba da ni. Kai da kanka ka gani, ya Allah na Isra'ila! Ka tashi ka taimake ni.
5 Ka tashi, ya Ubangiji, Allah Maɗaukaki, ka taimake ni, Ka tashi ka hukunta al'ummai, Kada ka yi wa waɗannan mugaye, maciya amana, jinƙai!
6 Da maraice suka komo, Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.
7 Ji abin da suke fada! Harsunansu suna kama da takuba a bakinsu, Duk da haka suna ta tambaya, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 Amma kai dariya kake yi musu, ya Ubangiji, Ka mai da al'ummai duka abin bandariya!
9 Mai tsarona, kai ne kake kiyaye ni, Kai ne mafakata, ya Allah.
10 Allahna wanda yake ƙaunata, zai zo gare ni, Zai sa in ga an kori magabtana.
11 Kada ka kashe su, ya Allah, don kada jama'ata su manta. Ka watsar da su da ikonka, ka hallaka su ya Ubangiji mai kiyaye mu!
12 Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne, Da ma a kama su saboda girmankansu, Domin suna la'antarwa, suna ƙarya!
13 Da fushinka ka hallaka su, Ka hallaka su ɗungum. Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila, Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya!
14 Da maraice maƙiyana suka komo, Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.
15 Suna kai da kawowa ko'ina neman abinci, In ba su sami abin da ya ishe su ba, Sukan yi gunaguni.
16 Amma zan raira waƙa a kan ikonka, Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfi Ga zancen madawwamiyar ƙaunarka. Kai mafaka ne a gare ni, Wurin ɓuya a kwanakin wahala.
17 Zan yabe ka, mai tsarona, Allah ne mafakata, Allah wanda ya ƙaunace ni.
1 Ka rabu da mu, ya Allah, har aka ci nasara a kanmu, Ka yi fushi da mu, amma yanzu sai ka juyo wurinmu!
2 Ka sa ƙasar ta girgiza, ka tsaga ta. Yanzu sai ka warkar da tsaguwarta, gama tana gab da fāɗuwa!
3 Ka sa jama'arka su sha wahala ƙwarai, Ka ba mu ruwan inabin da ya bugar da mu.
4 Ka ta da tuta ga masu tsoronka, Domin su juya su gudu daga abokin gāba.
5 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu'ata, Domin jama'ar da kake ƙauna ta sami cetonka.
6 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce, “Da nasara zan raba Shekem, Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama'ata.
7 Gileyad tawa ce, har da Manassa ma, Ifraimu ne kwalkwalina, Yahuza kuma sandana ne na sarauta.
8 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki, Edom kuwa kamar akwatin takalmina. Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.”
9 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara? Wa zai kai ni Edom?
10 Da gaske ka yashe mu ke nan? Ba za ka yi tafiya tare da sojojinmu ba?
11 Ka taimake mu, mu yaƙi abokan gāba, Domin taimako irin na mutum banza ne!
12 Idan Allah yana wajenmu, Za mu yi nasara, Zai kori abokan gābanmu.
1 Ya Allah, ka ji kukana, Ka ji addu'ata!
2 Sa'ad da nake nesa da gida, zuciyata ta karai, Zan yi kira gare ka! Ka kai ni lafiyayyiyar mafaka.
3 Kai ne kāriyata mai ƙarfi Da take kiyaye ni daga maƙiyana.
4 Ka yarda in zauna a alfarwarka dukan kwanakin raina, Ka yarda in sami zaman lafiya a ƙarƙashin fikafikanka.
5 Ya Allah, kā ji alkawaraina, Kā kuwa ba ni abin da ya dace, Tare da waɗanda suke ɗaukaka ka.
6 Ka ƙara wa sarki tsawon rai, Ka sa ya rayu dukan lokaci!
7 Ka sa ya yi mulki har abada a gabanka, ya Allah, Ka tsare shi da madawwamiyar ƙaunarka, da amincinka.
8 Don haka zan yi ta raira waƙar yabonka kullayaumin, A sa'ad da nake miƙa maka abin da na alkawarta.
1 Ga Allah kaɗai na dogara, Cetona daga gare shi yake fitowa.
2 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona, Shi ne kariyata, Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.
3 Har yaushe dukanku za ku fāɗa wa wani don ku yi nasara da shi, Kamar rusasshen garu, Ko kuma dangar da ta fāɗi?
4 Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja, Kuna jin daɗin yin ƙarairayi. Kuna sa masa albarka, Amma a zuciyarku la'antarwa kuke yi.
5 Ga Allah kaɗai na dogara, A gare shi na sa zuciyata.
6 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona, Shi ne kariyata, Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam.
7 Cetona da darajata daga Allah ne, Shi ne ƙaƙƙarfan makiyayina, Shi ne mafakata.
8 Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu.
9 Talakawa kamar shaƙar numfashi suke, Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani. Ko an auna su a ma'auni, sam ba su da nauyin kome, Sun fi numfashi shakaf.
10 Kada ku dogara da aikin kama-karya. Kada ku sa zuciya za ku ci ribar kome ta wurin fashi. In kuwa dukiyarku ta ƙaru, Kada ku dogara gare ta.
11 Sau ɗaya Allah ya faɗa, Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko.
12 Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce. Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa Kowane mutum bisa ga ayyukansa.
1 Ya Allah, kai ne Allahna, Ina sa zuciya gare ka. Duk niyyata ta nemanka ce, Raina yana ƙishinka, Kamar bussasshiyar ƙasa, Wadda ta zozaye, ba ta da ruwa.
2 Bari in gan ka a tsattsarkan wurinka, In dubi ɗaukakarka da darajarka.
3 Madawwamiyar ƙaunarka ta fi rai kansa, Saboda wannan zan yabe ka.
4 Muddin raina, zan yi maka godiya, Zan ta da hannuwana sama, in yi addu'a gare ka.
5 Raina zai yi liyafa, yă ƙoshi sosai, Ni kuwa zan raira waƙoƙin murna na yabo a gare ka.
6 Sa'ad da nake kwance a gadona na tuna da kai, Dare farai ina ta tunawa da kai,
7 Domin kai kake taimakona kullayaumin. Da murna, nake raira waƙa, A inuwar fikafikanka,
8 Raina yana manne maka, Ikonka yana riƙe da ni.
9 Waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni, Za su gangara zuwa lahira,
10 Za a kashe su cikin yaƙi, Kyarketai kuwa za su cinye gawawwakinsu.
11 Sarki zai yi farin ciki ga Allah, Duk waɗanda suka yi alkawarai da sunan Allah Za su yi murna, Amma za a rufe bakunan maƙaryata.
1 Ina shan wahala, ya Allah, ka ji addu'ata! Ina jin tsoro, ka cece ni daga maƙiyana!
2 Ka kiyaye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, Da iskancin mugayen mutane.
3 Sukan wasa harsunansu kamar takuba, Sukan kai bāra da mugayen maganganu kamar kibau.
4 Sukan yi kwanto su harbi mutanen kirki da kibau, Nan da nan sukan yi harbi, ba su kuwa jin tsoro.
5 Suna ƙarfafa junansu cikin yin mugayen ƙulle-ƙullensu, Sukan yi ta taɗi a kan inda za su kafa tarkunansu. “Ba wanda zai gan mu,” in ji su.
6 Sukan shirya maƙarƙashiya, su ce, “Ai, mun gama shirin aikata laifi sarai.” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa!
7 Amma Allah zai harbe su da kibansa, Za a yi musu rauni nan da nan.
8 Zai hallaka su saboda maganganunsu, Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa.
9 Dukansu za su ji tsoro, Za su faɗi abin da Allah ya aikata, Su yi tunani a kan ayyukansa.
10 Dukan masu adalci za su yi murna, Saboda abin da Ubangiji ya aikata. Za su sami mafaka a gare shi, Dukan mutanen kirki za su yabe shi.
1 Ya Allah, dole mutane su yabe ka a Sihiyona, Tilas su ba ka abin da suka alkawarta.
2 Saboda kakan amsa addu'o'i, Dukan mutane za su zo wurinka.
3 Zunubanmu sun kāshe mu, Amma za ka gafarta zunubanmu.
4 Masu farin ciki ne waɗanda ka zaɓe su Su zauna a tsattsarkan wurinka! Za mu ƙoshi da kyawawan abubuwa da suke wurin zamanka, Da albarkun tsattsarkan Haikalinka!
5 Ka amsa mana, ya Allah Mai Cetonmu, Ka kuma cece mu ta wurin aikata al'amuran banmamaki. Mutane daga ko'ina a duniya, Har da waɗanda suke can nesa a hayin tekuna, Sun dogara gare ka.
6 Ka kakkafa duwatsu ta wurin ikonka, Ka bayyana ƙarfin ikonka.
7 Kakan kwantar da rurin tekuna, Kakan kwantar da rurin igiyar ruwa, Kakan kwantar da tarzomar jama'a.
8 Dukan duniya ta tsorata, Saboda manyan ayyuka da ka aikata. Ayyukanka sukan kawo sowa ta farin ciki Daga wannan iyakar duniya zuwa wancan.
9 Kakan nuna kana kulawa da ƙasar, Ta wurin aiko mata da ruwa. Ka arzuta ta, ta zama dausayi. Rafuffukan da ka bayar ba su taɓa ƙafewa ba, Sun sa ƙasar ta ba da amfanin gonaki, Abubuwan da ka aikata ke nan.
10 Ka kwarara ruwa mai yawa a gonakin da aka nome, Ka jiƙe su da ruwa, Ka tausasa ƙasar da yayyafi, Ka sa ƙananan tsire-tsire su yi girma.
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka! Inda ka tafi duka akwai wadata!
12 Makiyaya suna cike da tumaki masu ƙiba, Tuddai kuma suna cike da farin ciki.
13 Sauruka suna cike da tumaki, Kwaruruka suna cike da alkama, Suna sowa suna raira waƙa ta farin ciki!
1 Ku yabi Allah da babbar murya ta farin ciki, Ya jama'a duka!
2 Ku raira waƙar darajar sunansa, Ku yabe shi da ɗaukaka!
3 Ku faɗa wa Allah cewa, “Al'amuran da kake aikatawa Suna da banmamaki ƙwarai! Ikonka yana da girma ƙwarai, Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro.
4 Duk wanda yake a duniya, yana yi maka sujada, Yana raira maka waƙar yabbai, Yana raira yabbai ga sunanka.”
5 Zo, ka ga abin da Allah ya yi, Ayyukansa masu ban al'ajabi Waɗanda ya aikata ga mutane.
6 Ya sa teku ta zama busasshiyar ƙasa, Kakanninmu suka haye kogi da ƙafa. A can muka yi farin ciki saboda abin da ya yi.
7 Har abada yana mulki ta wurin ƙarfinsa, Yana duban al'ummai, Don kada 'yan tawaye su tayar masa!
8 Ku yabi Allahnmu, ya ku dukan al'ummai, Bari a ji yabon da kuke yi masa.
9 Shi ne yake rayar da mu, Bai kuwa yarda mu fāɗi ba.
10 Ka jarraba mu, ya Allah, Kamar yadda ake tace azurfa da wuta, Haka nan ka jarraba mu.
11 Ka bar mu muka fāɗa a tarko, Ka ɗora mana kaya masu nauyi.
12 Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu, Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa, Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri.
13 Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka, Zan miƙa maka abin da na alkawarta.
14 Zan ba ka abin da na ce zan bayar, A lokacin da nake shan wahala.
15 Zan miƙa tumaki don a ƙona a kan bagade, Nan za a ji ƙanshi mai daɗi na ƙonannun awaki, Zan miƙa hadayu na bijimai da na awaki.
16 Ku zo ku ji, dukanku, ku da kuke girmama Allah, Ni kuwa zan faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Na yi kira gare shi neman taimako, A shirye nake in yabe shi da waƙoƙi.
18 Da ban watsar da zunubaina ba, Da Ubangiji bai ji ni ba.
19 Amma hakika Allah ya ji ni, Ya saurari addu'ata.
20 Ina yabon Allah, Domin bai ƙi addu'ata ba, Bai kuwa hana mini madawwamiyar ƙaunarsa ba.
1 Ka yi mana jinƙai, ya Allah, ka sa mana albarka, Ka dube mu da idon rahama,
2 Domin dukan duniya ta san nufinka, Dukan sauran al'umma kuma su san cetonka.
3 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka!
4 Da ma sauran al'umma su yi murna, su raira waƙa ta farin ciki, Domin kana yi wa jama'a shari'a ta adalci, Kana kuma bi da dukan sauran al'umma.
5 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka!
6 Ƙasa ta ba da amfaninta, Allah, wanda yake Allahnmu ne, ya sa mana albarka.
7 Allah ya sa mana albarka, Da ma dukan jama'a ko'ina su girmama shi.
1 Da ma Allah ya tashi ya warwatsa maƙiyansa! Da ma su waɗanda suke ƙinsa su gudu!
2 Kamar yadda iska take korar hayaƙi, Haka nan zai kore su, Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta, Haka nan mugaye za su hallaka a gaban Allah.
3 Amma adalai za su yi murna, Su kuma yi farin ciki a gaban Allah, Za su yi murna ƙwarai da gaske.
4 Ku raira waƙa ga Allah, Ku raira waƙar yabo ga sunansa, Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai. Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa!
5 Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa, Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye, Wato matan da mazansu suka mutu.
6 Yakan ba waɗanda suke da kewa gida, su zauna a ciki, Yakan fitar da 'yan sarƙa ya kai su 'yanci mai daɗi, Amma 'yan tawaye za su zauna a ƙasar da ba kowa a ciki.
7 Sa'ad da ka bi da jama'arka, ya Allah, Sa'ad da ka yi tafiya a hamada,
8 Duniya ta girgiza, sararin sama ya kwararo ruwa, Saboda bayyanar Allah, har Dutsen Sinai ya girgiza, Saboda bayyanar Allah na Isra'ila.
9 Ka sa aka yi ruwan sama mai yawa, ya Allah, Ka rayar da ƙasarka wadda ta zozaye.
10 Jama'arka suka gina gidajensu a can, Ta wurin alherinka ka yi wa matalauta tanadi.
11 Ubangiji ya ba da umarni, Sai mata masu yawa suka baza labari cewa,
12 “Sarakuna da rundunan sojojinsu suna gudu! Matan da suke a gida suka rarraba ganima.”
13 Suna kamar kurciyoyin da aka dalaye da azurfa, Waɗanda fikafikansu suna ƙyalli kamar kyakkyawar zinariya. (Me ya sa waɗansunku suke zaune cikin shingen tumaki?)
14 Sa'ad da Allah Mai Iko Dukka Ya warwatsar da sarakuna a dutsen Zalmon, Sai ya sa dusar ƙanƙara ta sauka a wurin.
15 Wane irin babban dutse ne wannan dutsen Bashan? Tulluwarka nawa, dutsen Bashan?
16 Me ya sa, daga manyan kawunanka Kake yi wa dutsen da Allah ya zaɓa Ya zauna a kai, duban raini? A nan Ubangiji zai zauna har abada!
17 Daga Sinai da dubban manyan karusansa, Ubangiji ya zo tsattsarkan Haikalinsa.
18 Ya hau kan tsaunuka Tare da ɗumbun waɗanda ya kamo daga yaƙi, Yana karɓar kyautai daga wurin mutane, Daga wurin 'yan tawaye kuma. Ubangiji Allah zai zauna a can.
19 Ku yabi Ubangiji, Wanda yake ɗaukar nawayarmu ta yau da kullum, Shi ne Allah wanda ya cece mu.
20 Allahnmu, Allah Mai Ceto ne, Shi ne Ubangiji, Ubangijinmu, Wanda yake cetonmu daga mutuwa.
21 Hakika Allah zai farfashe kawunan abokan gābansa, Da na waɗanda suka nace bin hanyoyinsu na zunubi.
22 Ubangiji ya ce, “Zan komo da su daga Bashan, Zan komo da su daga zurfin teku,
23 Don ku wanke sawayenku a cikin jinin maƙiyanku, Karnukanku kuwa za su lashe iyakar abin da suke so.”
24 Ya Allah, jama'a duka sun ga irin tafiyarka ta nasara, Irin tafiyar Allah, Sarkina, zuwa tsattsarkan wurinsa.
25 Mawaƙa suna kan gaba, mabusa suna biye, A tsakiya kuwa 'yan mata suna kaɗa bandiri.
26 “Ku jama'ar Allah, ku yabe shi cikin taronku, Ku yabi Ubangiji, dukanku, ku zuriyar Isra'ila!”
27 Ga Biliyaminu mafi ƙanƙanta Cikin kabilai, a kan gaba, Sa'an nan shugabannin Yahuza da ƙungiyarsu, Daga nan sai shugabannin Zabaluna da na Naftali suna biye da su.
28 Ka nuna ikonka, ya Allah, Ikon nan da ka nuna saboda mu.
29 Daga Haikalinka a Urushalima, Sarakuna sukan kawo maka kyautai.
30 Ka tsauta wa Masar, naman jejin nan Mai zafin hali da yake cikin iwa, Ka tsauta wa sauran al'umma, taron bijiman nan da 'yan maruƙansu, Har dukansu su durƙusa, su miƙa maka azurfarsu. Ka warwatsar da jama'ar nan Masu son yin yaƙi!
31 Wakilai za su zo daga Masar, Habashawa za su miƙa hannuwansu sama, Su yi addu'a ga Allah.
32 Ku raira waƙa ga Allah, ku mulkokin duniya, Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,
33 Shi wanda ya hau cikin sararin sama, Daɗaɗɗen sararin sama! Ku kasa kunne ga muryarsa mai ƙarfi!
34 Ku yi shelar ikon Allah, Ɗaukakarsa tana bisa kan Isra'ila, Ikonsa yana cikin sararin sama.
35 Allah al'ajabi ne a tsattsarkan wurinsa, Allah na Isra'ila! Yana ba da ƙarfi da iko ga jama'arsa. Ku yabi Allah!
1 Ka cece ni, ya Allah! Ruwa ya sha kaina.
2 Ina nutsewa cikin laka mai zurfi, Ba kuwa ƙasa mai ƙarfi, Na tsunduma cikin ruwa mai zurfi, Raƙuman ruwa kuwa sun kusa kashe ni.
3 Na gaji da kira, ina neman taimako, Maƙogwarona yana yi mini ciwo, Idanuna duka sun gaji, Saboda ina zuba ido ga taimakonka.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili Sun fi gashin kaina yawa, Waɗanda suke baza ƙarya suke ƙina, Suna da ƙarfi, suna kuwa so su kashe ni. Suka tilasta ni in mayar da abubuwan da ba satarsu na yi ba.
5 Zunubaina ba a ɓoye suke a gare ka ba ya Allah, Ka san irin wawancin da na yi!
6 Kada ka bar ni in jawo kunya ga waɗanda suka dogara gare ka, Ya Ubangiji Allah Mai Iko Dukka! Kada ka bar ni in jawo abin kunya Ga waɗanda suke maka sujada, ya Allah na Isra'ila!
7 Sabili da kai ne aka ci mutuncina, Kunya ta rufe ni.
8 Kamar baƙo nake ga 'yan'uwana, Haka ma ga iyalina, kamar baƙo nake.
9 Ƙaunar da nake da ita ta yin ibada a Haikalinka Tana iza ni a ciki kamar wuta, Zargin da suke yi a kanka, ya fāɗa a kaina.
10 Na ƙasƙantar da kaina ta wurin yin azumi, Jama'a kuwa suka ci mutuncina.
11 Na sa tufafin makoki, Sai suka maishe ni abin dariya.
12 A tituna suna ta magana a kaina, Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina.
13 Amma ni, zan yi addu'a gare ka, ya Ubangiji, Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa, Sabili da muhimmiyar ƙaunarka, Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto.
14 Ka cece ni daga nutsewa cikin wannan laka, Ka kiyaye ni daga maƙiyana, Daga kuma wannan ruwa mai zurfi.
15 Kada ka bar ambaliyar ruwa ta rufe ni. Kada ka bar ni in mutu cikin zurfafa, Ko in nutse a cikin kabari.
16 Sabili da madawwamiyar ƙaunarka, ka amsa mini, ya Ubangiji, Ka juyo wurina, saboda juyayinka mai girma!
17 Kada ka ɓoye kanka daga bawanka, Ina shan babbar wahala, ka yi hanzari ka amsa mini!
18 Ka zo ka fanshe ni, Ka kuɓutar da ni daga abokan gābana.
19 Ka san yadda ake cin mutuncina, Da yadda ake kunyata ni, ake ƙasƙantar da ni, Kana ganin dukan abokan gābana.
20 Zuciyata ta karai saboda cin mutuncin da ake ci mini, Ni kuwa ba ni da mataimaki, Na sa zuciya za a kula da ni, Amma babu. Na sa zuciya zan sami ta'aziyya, Amma ban samu ba.
21 Sa'ad da na ji yunwa, sai suka ba ni dafi, Sa'ad da na ji ƙishi, sai suka ba ni ruwan tsami.
22 Allah ya sa bukukuwansu su zama lalacewarsu, Shagulgulansu kuma su zama sanadin fāɗuwarsu!
23 Ka makantar da su, har da ba za su iya gani ba, Kullum ka sa bayansu ya ƙage!
24 Ka kwarara musu fushinka, Bari zafin fushinka ya ci musu!
25 Allah ya sa su gudu su bar sansaninsu, Kada wani ya ragu da rai cikin alfarwansu!
26 Sun tsananta wa waɗanda ka hukunta, Suna taɗin shan wuyar waɗanda ka aukar wa cutar.
27 Ka riɓaɓɓanya zunubansu, Kada ka bar su su sami rabon kome daga cikin cetonka.
28 Ka sa a goge sunansu daga cikin littafin rai, Kada a sa su a lissafin jama'arka.
29 Amma ni mai bukata ne, ina shan wahala, Ka tsame ni, ya Allah, ka cece ni!
30 Zan raira waƙar yabo ga Allah, Zan yi shelar girmansa ta wurin yi masa godiya,
31 Wannan zai daɗaɗa wa Ubangiji rai Fiye da hadayar bijimi, Fiye da a ba shi bijimi bana bakwai.
32 Sa'ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna, Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su.
33 Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata, Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba.
34 Ku yabi Allah, ku al'arshi da duniya, ku yabi Allah, Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu!
35 Gama zai ceci Sihiyona, Ya sāke gina garuruwan Yahuza, Jama'arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar.
36 Zuriyar bayinsa za su gāje ta, Masu ƙaunarsa za su zauna a wurin.
1 Ka cece ni, ya Allah! Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
2 Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!
3 Ka sa waɗanda suke mini ba'a Su razana sabili da fāɗuwarsu!
4 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka Su yi murna, su yi farin ciki! Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”
5 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki, Ya Allah, ka zo wurina da hanzari. Kai ne mataimakina da Mai Cetona, Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!
1 A gare ka, ya Ubangiji, lafiya lau nake, Faufau kada ka bari a yi nasara da ni!
2 Sabili da kai adali ne ka taimake ni, ka cece ni. Ka kasa kunne gare ni, ka cece ni!
3 Ka zama mini lafiyayyiyar mafaka, Da kagara mai ƙarfi, domin ka tsare ni, Kai ne mafakata da kāriyata.
4 Ya Allahna, ka cece ni daga mugaye, Daga ikon mugga, wato mugayen mutane.
5 Ya Ubangiji, a gare ka nake sa zuciya, Tun ina yaro, nake dogara gare ka.
6 A duk kwanakina a gare ka nake dogara, Kana kiyaye ni tun da aka haife ni, Kullayaumi zan yabe ka!
7 Raina abin damuwa ne ga mutane da yawa, Amma kai ne kāriyata mai ƙarfi.
8 Ina yabonka dukan yini, Ina shelar darajarka.
9 Yanzu da na tsufa, kada ka yashe ni, Yanzu da ƙarfina ya ƙare kuma, kada ka rabu da ni!
10 Maƙiyana, waɗanda suke so su kashe ni, Suna magana, suna ƙulle-ƙulle gāba da ni.
11 Suna cewa, “Ai, Allah ya rabu da shi, Gama ba wanda zai cece shi!”
12 Kada ka yi nisa da ni haka, ya Allah, Ka yi hanzari ka taimake ni, ya Allahna!
13 Ka sa a kori waɗanda suka tasar mini, A hallaka su! Ka sa a kunyata waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni, A wulakanta su sarai!
14 A koyaushe zan sa zuciya gare ka, Zan yi ta yabonka.
15 Zan ba da labarin adalcinka, Zan yi magana a kan cetonka duk yini, Ko da yake ya fi ƙarfin in san shi duka.
16 Zan tafi in yi yabon ikonka, ya Ubangiji Allah, Zan yi shelar adalcinka, Naka, kai kaɗai.
17 Kai ne ka koya mini, ya Allah, tun lokacin da nake yaro, Har wa yau kuwa ina ba da labarin ayyukanka masu banmamaki.
18 Yanzu da na tsufa, na kuma yi furfura, Kada ka rabu da ni, ya Allah! Ka kasance tare da ni sa'ad da nake shelar ikonka da ƙarfinka ga mutanen dukan zamanai masu zuwa.
19 Adalcinka, ya Allah, ya kai har sammai. Ka aikata manyan ayyuka, Ba waninka!
20 Ka aiko mini da wahala da azaba, Amma za ka mayar mini da ƙarfina, Za ka tashe ni daga kabari.
21 Za ka girmama ni har abada, Za ka sāke ta'azantar da ni.
22 Hakika zan yabe ka da garaya, Zan yabi amincinka, ya Allahna. Da garayata zan yi maka waƙoƙi, Ya Mai Tsarki na Isra'ila.
23 Zan ta da muryar farin ciki Sa'ad da nake raira maka waƙar yabbai, Zan raira waƙa da zuciya ɗaya, Gama dā ka fanshe ni.
24 Zan yi magana a kan adalcinka dukan yini, Saboda an yi nasara da waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni, sun ruɗe.
1 Ka koya wa sarki ya yi shari'a Da adalcinka, ya Allah, Ka kuma ba shi shari'arka,
2 Don ya yi mulkin jama'arka bisa kan shari'a, Ya kuma bi da mulki da adalci.
3 Ka sa ƙasar ta mori wadatarta, Ka sa al'ummar ta san adalci.
4 Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari'ar gaskiya, Ya taimaki waɗanda suke da bukata, Ya kuma hukunta azzalumai!
5 Ka sa su girmama ka Muddin rana tana haskakawa, Muddin wata yana ba da haske dukan lokaci.
6 Ka sa sarki ya zama kamar ruwan sama a gonaki, Ya zama kamar yayyafi a bisa ƙasa.
7 Ka sa adalci ya bunƙasa a zamaninsa, Wadata ta dawwama muddin wata na haskakawa.
8 Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku, Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya.
9 Kabilan hamada za su durƙusa a gabansa, Abokan gābansa za su kwanta warwar a cikin ƙura.
10 Sarakunan Esbanya da na tsibirai, Za su ba shi kyautai, Sarakunan Arabiya da na Habasha Za su kawo masa kyautai.
11 Dukan sarakuna za su durƙusa a gabansa, Dukan sauran al'umma za su bauta masa!
12 Yakan ceci matalauta waɗanda suka yi kira gare shi, Da waɗanda suke da bukata, Da waɗanda ba a kula da su.
13 Yakan ji tausayin gajiyayyu da matalauta, Yakan ceci rayukan waɗanda suke da bukata.
14 Yakan cece su daga zalunci da kama-karya, Rayukansu suna da daraja a gare shi.
15 Ran sarki yă daɗe! Da ma a ba shi zinariya daga Arabiya, Da ma a yi masa addu'a dukan lokaci, Allah ya sa masa albarka kullum!
16 Da ma a sami hatsi mai yawa a ƙasar, Da ma amfanin gona yă cika tuddan, Yă yi yawa kamar itatuwan al'ul na Lebanon, Da ma birane su cika da mutane, Kamar ciyayin da suke girma a sauruka.
17 Da ma a yi ta tunawa da sunansa har abada, Da ma shahararsa ta ɗore muddin rana tana haskakawa. Da ma dukan sauran al'umma su yabi sarkin, Dukan jama'a su roƙi Allah yă sa musu albarka, Kamar yadda ya sa wa sarki albarka.
18 Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila, Wanda shi kaɗai ne yake aikata al'amuran nan masu banmamaki!
19 Ku yabi sunansa mai daraja har abada, Allah ya sa ɗaukakarsa ta cika dukan duniya! Amin! Amin!
20 Ƙarshen addu'o'in Dawuda, ɗan Yesse ke nan.
1 Hakika, Allah yana yi wa Isra'ila alheri, Da waɗanda suke da tsarkin zuciya!
2 Amma ina gab da fāɗuwa, Ƙafafuna sun kusa zamewa,
3 Saboda na ji kishin masu girmankai, Sa'ad da na ga mugaye suna arziki.
4 Ba su jin zafin ciwo, Su ƙarfafa ne, lafiyayyu.
5 Ba su shan wahala yadda sauran mutane suke sha, Ba su da wahala kamar sauran mutane,
6 Don haka suka ɗaura girmankai kamar dutsen wuya, Suka sa hargitsi kuma kamar riga.
7 Zuciyarsu, cike take da mugunta, Tunaninsu kuma cike suke da mugayen ƙulle-ƙulle.
8 Sukan yi wa waɗansu ba'a, Suna faɗar mugayen abubuwa, Masu girmankai ne su, suna shawara A kan yadda za su zalunci waɗansu.
9 Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama, Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya,
10 Har jama'ar Allah ma sukan koma wurinsu, Suna ɗokin gaskata dukan abin da suke faɗa musu.
11 Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba, Maɗaukaki ba zai bincika ba!”
12 Haka mugaye suke. Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi.
13 Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki, Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi?
14 Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini, Kana horona kowace safiya!
15 Da na faɗi waɗannan abubuwa, Da na zama marar gaskiya ga jama'arka.
16 Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan, Ko da yake ya cika wuya,
17 Sai sa'ad da na shiga Haikalinka, Sa'an nan na fahimci abin da zai sami mugaye.
18 Hakika ka sa su a wurare masu santsi, Ka sa su su fāɗi su hallaka sarai!
19 Cikin ƙyaftawar ido aka hallaka su, Suka yi mummunan ƙarshe!
20 Ya Ubangiji, kamar mafarki suke Wanda akan manta da shi da safe, Sa'ad da mutum ya farka yakan manta da kamanninsa.
21 Sa'ad da zuciyata ta ɓaci, Hankalina ya tashi,
22 Sai na zama wawa, ban fahimta ba, Na nuna halin dabba a gabanka.
23 Duk da haka ina tare da kai kullayaumin, Kana riƙe da hannuna.
24 Shawararka, tana bi da ni, Daga ƙarshe kuma za ka karɓe ni da daraja.
25 In banda kai, wa nake da shi a Sama? Tun da yake ina da kai, me kuwa nake bukata a duniya?
26 Kwanyata da jikina za su raunana, Amma Allah ne ƙarfina, Shi nake so har abada!
27 Hakika waɗanda za su rabu da kai za su mutu, Za ka hallakar da marasa aminci gare ka.
28 Amma a gare ni, ya fi mini kyau, in kasance kusa da Allah! Na sami mafaka a wurin Ubangiji Allah, Da zan yi shelar dukan abin da ya aikata.
1 Don me ka yashe mu haka, ya Allah? Za ka yi ta fushi da jama'arka har abada ne?
2 Ka tuna da jama'arka waɗanda ka zaɓa su zama naka tuntuni, Ka tuna da jama'arka waɗanda ka fansa, Don su zama kabilarka. Ka tuna da Dutsen Sihiyona, inda zatinka yake!
3 Ka zo, ka yi yawo a wannan kufai, Abokan gābanmu sun lalatar da kome na cikin Haikali!
4 Abokan gābanka suka yi sowa ta nasara A inda akan sadu da kai, Sun ƙwace Haikalin.
5 Suna kama da masu saran itace, Suna saran itatuwa da gaturansu.
6 Da gaturansu da gudumarsu, Sun ragargaje ƙyamaren da aka yi da katako.
7 Sun sa wa Haikalinka wuta, Sun ƙazantar da wurin da akan yi maka sujada, Sun farfashe shi duk.
8 Sun yi niyya su murƙushe mu sarai, Sun ƙone kowane tsattsarkan wuri na ƙasar.
9 Ba sauran tsarkakan alamu, Ba sauran annabawan da suka ragu, Ba kuwa wanda ya san ƙarewar wannan.
10 Ya Allah, har yaushe abokan gābanmu za su yi ta yi mana ba'a? Za su yi ta zargin sunanka har abada ne?
11 Me ya sa ka ƙi taimakonmu? Ka tasar musu ka hallaka su!
12 Amma ya Allah, kai ne Sarkinmu tun daga farko, Ka yi nasara da duniya.
13 Da ƙarfin ikonka ka raba teku, Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,
14 Ka ragargaje kawunan kadduna, Ka kuwa ba mutanen hamada su ci.
15 Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu, Ka sa manyan koguna su ƙafe.
16 Ka halicci yini da dare, Ka sa rana da wata a wurarensu.
17 Ka yi wa duniya kan iyaka, Ka kuwa yi lokatan damuna da na rani.
18 Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a, Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.
19 Kada ka ba da jama'arka marasa taimako A hannun mugayen maƙiyansu, Kada ka manta da jama'arka waɗanda ake tsananta musu!
20 Ka tuna da alkawarin da ka yi mana, Akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar!
21 Kada ka bari a kori waɗanda ake zalunta, Amma bari matalauta da masu mayata su yabe ka.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre kanka! Ka tuna fa, marasa tsoronka suna ta yi maka ba'a dukan yini!
23 Kada ka manta da hargowar maƙiyanka, Kada ka manta da hayaniyar da magabtanka suke ta yi.
1 Muna yabonka, ya Allah, muna yabonka! Muna shelar sunanka mai girma, Muna kuwa faɗa abubuwan banmamaki da ka aikata!
2 “Na ƙayyade lokacin yin shari'a,” in ji Ubangiji Allah, “Zan kuwa yi shari'ar gaskiya.
3 Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace, Zan ƙarfafa harsashin gininta.
4 Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama, Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya,
5 Na dai faɗa musu su daina yanga, Su daina yin taƙama.”
6 Hukunci ba daga gabas, ko yamma, Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba.
7 Allah yake yin shari'a, Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu.
8 Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo, Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi, Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha, Suka shanye shi ƙaƙaf.
9 Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba, Ko in daina raira yabbai gare shi.
10 Shi zai karya ikon mugaye, Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.
1 Allah sananne ne a Yahuza, Mashahuri ne kuma a Isra'ila.
2 Wurin zamansa yana Urushalima, A dutsen Sihiyona zatinsa yake.
3 A can yake kakkarya kiban abokan gāba, Da garkuwoyinsu, da takubansu, i, har da dukan makamansu.
4 Ina misalin darajarka, ya Allah! Ina misalin ɗaukakarka a sa'ad da ka komo daga kan duwatsu, Daga korar abokan gābanka!
5 An kwashe ganimar sojojinsu masu ƙarfin hali, Yanzu suna barci, barcin matattu, Ba waninsu da ya ragu, Da zai yi amfani da makamansa.
6 Sa'ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu, Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu.
7 Amma mutane suna jin tsoronka! Wa zai iya tsayawa a gabanka Sa'ad da ka yi fushi?
8 Daga Sama ka sanar da shari'arka, Duniya ta tsorata, ta yi tsit,
9 Sa'ad da ka tashi domin ka yanke hukunci, Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya.
10 Hasalar mutane ba ta ƙara kome, sai dai ta ƙara maka yabo. Waɗanda suka tsira daga yaƙe-yaƙe za su kiyaye idodinka.
11 Ku ba Ubangiji Allahnku abin da kuka alkawarta masa, Dukanku sauran al'umma da kuke kusa, ku kawo masa kyautai. Allah yakan sa mutane su ji tsoronsa,
12 Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai, Ya tsoratar da manyan sarakuna.
1 Na ta da murya, na yi kuka ga Allah, Na ta da murya, na yi kuka, ya kuwa ji ni.
2 A lokacin wahala, nakan yi addu'a ga Ubangiji, Dukan dare nakan ɗaga hannuwana sama in yi addu'a, Amma ban sami ta'aziyya ba.
3 Lokacin da na tuna da Allah na yi ajiyar zuciya. Sa'ad da nake tunani, Nakan ji kamar in fid da zuciya.
4 Ba ya barina in yi barci, Na damu har na kāsa magana.
5 Na yi tunanin kwanakin da suka wuce, Nakan kuma tuna da shekarun da suka wuce da daɗewa.
6 Dare farai ina ta tunani mai zurfi, A cikin tunani nakan yi wa kaina tambaya.
7 A kullum ne Ubangiji zai yashe ni? Ba kuma zai ƙara yin murna da ni ba?
8 Ya daina ƙaunata ke nan? Alkawarinsa ba shi da wani amfani?
9 Allah ya manta da yin jinƙai ne? Fushinsa ya maye matsayin juyayinsa ne?
10 Sa'an nan sai na ce, “Abin da ya fi mini zafi duka, Shi ne ikon Maɗaukaki ya ragu.”
11 Zan tuna da manyan ayyukanka, ya Ubangiji, Zan tuna da al'amura masu banmamaki da ka aikata a dā.
12 Zan tuna da dukan abubuwan da ka yi, Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka.
13 Dukan abin da kake yi mai tsarki ne, ya Allah! Ba wani allah mai girma kamarka!
14 Kai ne Allah wanda kake aikata al'ajabai, Ka nuna ikonka cikin sauran al'umma.
15 Ta wurin ikonka ka fanshi jama'arka, Zuriyar Yakubu da ta Yusufu.
16 Ya Allah, sa'ad da ruwaye suka gan ka, sai su tsorata, Zurfafan teku kuma suka yi rawar jiki.
17 Gizagizai suka zubo da ruwa, Aka buga tsawa daga sama, Aka kuwa yi walƙiya ko'ina.
18 Bugawar tsawarka ta gama ko'ina, Hasken walƙiya ya haskaka dukan duniya, Duniya ta yi rawa, ta girgiza, ta kaɗu.
19 Ka yi tafiya a teku, Ka haye teku mai zurfi, Amma ba a ga shaida inda ka taka ba.
20 Ka bi da jama'arka yadda makiyayi yake yi, Musa da Haruna suke lura da su.
1 Ku kasa kunne ga koyarwata, ya ku jama'ata, Ku kula da abin da nake faɗa.
2 Zan yi magana da ku, In faɗa muku asirai na dā,
3 Abubuwan da muka ji muka kuwa sani, Waɗanda kakanninmu suka faɗa mana.
4 Ba za mu ɓoye waɗannan abubuwa daga 'ya'yanmu ba, Amma za mu faɗa wa tsara mai zuwa Labarin ikon Ubangiji, da manya manyan ayyukansa, Da abubuwan banmamaki waɗanda ya aikata.
5 Ya ba da dokoki ga jama'ar Isra'ila, Da umarnai ga zuriyar Yakubu. Ya ba kakanninmu ka'idodi, Don su koya wa 'ya'yansu dokokinsa,
6 Saboda tsara mai zuwa ta koye su, Su kuma su koya wa 'ya'yansu.
7 Ta haka su ma za su dogara ga Allah, Ba za su manta da abin da ya yi ba, Amma a kullum za su riƙa biyayya da umarnansa.
8 Kada su zama kamar kakanninsu, Jama'ar 'yan tawaye marasa biyayya. Ba su taɓa dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya ba, Ba su kuwa yi masa aminci ba.
9 Ifraimawa waɗanda suka yi yaƙi da bakkuna da kibau Suka gudu a ranar yaƙi.
10 Ba su kiyaye alkawarinsu da Allah ba, Sun ƙi biyayya da dokokinsa.
11 Sun manta da abin da ya aikata, Da mu'ujizan nan da ya nuna musu.
12 Kakanninsu na kallo sa'ad da Allah ya aikata wata mu'ujiza A filin Zowan a ƙasar Masar.
13 Ya raba teku, ya ratsa da su ta cikinta, Ya sa ruwa ya tsaya kamar bango.
14 Da rana sai ya bi da su da girgije, Da dare kuwa ya bi da su da hasken wuta.
15 Ya tsaga duwatsu, suka buɗe a hamada, Ya ba su ruwa daga cikin zurfafa.
16 Ya sa rafi ya fito daga cikin dutse, Ya sa ruwan ya yi gudu kamar a kogi.
17 Amma sun ci gaba da yi wa Allah zunubi, A hamada suka yi wa Maɗaukaki tawaye.
18 Da gangan suka jarraba Allah, Da suka ce ya ba su irin abincin da suke so.
19 Suka yi magana gāba da Allah, suka ce, “Ko Allah yana da iko ya ba mu abinci a hamada?
20 Gaskiya ce, ya bugi dutse, Ruwa kuwa ya fito a yalwace, Amma ko yana da iko ya ba da abinci da nama ga jama'arsa?”
21 Saboda haka Allah ya yi fushi sa'ad da ya ji su, Ya aukar wa jama'arsa da wuta, Fushinsa ya haɓaka a kansu,
22 Saboda ba su amince da shi ba, Ba su kuma gaskata yana da ikon cetonsu ba.
23 Amma ya yi magana da sararin sama, Ya umarci ƙofofinsa su buɗe,
24 Ya ba su tsaba daga sama, Da ya sauko musu da manna, su ci.
25 Ta haka suka ci abincin mala'iku. Allah ya ba su iyakar abin da za su iya ci.
26 Sa'an nan sai ya sa iskar gabas ta hura, Da ikonsa kuma ya sa iskar kudu ta tashi.
27 Ya aika da tsuntsaye bisansu kamar ƙura, Yawansu kamar yashi a gaɓa,
28 Sai suka fāɗo a zango, Kewaye da alfarwai ko'ina.
29 Sai mutane suka ci suka ƙoshi, Allah ya ba su iyakar abin da suke bukata.
30 Amma sa'ad da suke cikin ci, Tun ba su ƙoshi ba,
31 Sai Allah ya yi fushi da su. Ya karkashe ƙarfafan mutane, Da samarin Isra'ila na gaske!
32 Ko da yake ya aikata mu'ujizai da yawa, Duk da haka jama'a suka ci gaba da yin zunubi, Ba su kuwa gaskata shi ba.
33 Ta haka ya ƙare kwanakinsu kamar fitar numfashi, Bala'i ya aukar wa rayukansu farat ɗaya.
34 Amma sa'ad da ya kashe waɗansunsu, Sai sauran suka juyo gare shi suka tuba, Suka yi addu'a sosai a gare shi.
35 Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su, Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu.
36 Amma maganganunsu duka ƙarya ne, Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.
37 Ba su yi masa biyayya ba, Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.
38 Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai, Ya gafarta zunubansu, Bai hallaka su ba. Sau da yawa yakan kanne fushinsa, Ya dakatar da hasalarsa.
39 Yakan tuna su mutane ne kawai, Kamar iskar da take hurawa ta wuce .
40 Sau da yawa suka tayar masa a hamada. Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai!
41 Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai, Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra'ila yin fushi.
42 Suka manta da ikonsa mai girma. Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu,
43 Lokacin da ya aikata manyan ayyuka da mu'ujizai A filin Zowan, ta ƙasar Masar.
44 Ya mai da koguna su zama jini, Masarawa kuwa suka kasa sha daga rafuffukansu.
45 Ya aiko da ƙudaje gare su, suka wahalshe su, Kwaɗi suka lalata filayensu.
46 Ya aiko da gamzari don su ci amfanin gonakinsu, Ya aiko da ɗango su lalata gonakinsu.
47 Ya kashe kurangar inabinsu da ƙanƙara, Ya kuma kashe itatuwan ɓaurensu da jaura.
48 Ya karkashe shanunsu da ƙanƙara, Ya kuma karkashe garkunan tumakinsu da na awakinsu da tsawa.
49 Ya buge su da fushinsa mai zafi, da hasalarsa, Ya sa su damuwa ƙwarai, Da ya aiko da mala'iku masu hallakarwa.
50 Bai kanne fushinsa ba, Bai bar su da rai ba, Amma ya karkashe su da annoba.
51 Ya karkashe 'yan fari maza Na dukan iyalan da suke Masar.
52 Sa'an nan ya bi da jama'arsa Kamar makiyayi, ya fito da su, Ya yi musu jagora cikin hamada.
53 Ya bi da su lafiya, ba su kuwa ji tsoro ba, Amma teku ta cinye abokan gābansu.
54 Ya kawo su tsattsarkar ƙasarsa, Ya kawo su a duwatsun da shi kansa ya ci da yaƙi.
55 Ya kori mazaunan wurin sa'ad da jama'arsa suka dirkako, Ya rarraba ƙasar ga kabilan Isra'ila, A nan ya ba su izini su zauna a wurin, a cikin alfarwansu.
56 Amma sai suka yi wa Allah Mai Iko Dukka tawaye, Suka jarraba shi. Ba su kiyaye dokokinsa ba,
57 Amma suka yi tawaye da rashin aminci Kamar kakanninsu, Kamar kiban da aka harba da tanƙwararren baka, Waɗanda ba su da tabbas.
58 Suka sa shi ya yi fushi saboda Masujadansu na arnanci. Suka sa ya ji kishi saboda gumakansu.
59 Allah ya yi fushi sa'ad da ya ga haka, Don haka ya rabu da jama'arsa ɗungum.
60 Ya bar alfarwarsa da take a Shilo, Wato wurin da yake zaune a dā, a tsakiyar mutane.
61 Ya yardar wa abokan gāba su ƙwace akwatin alkawari, Inda aka ga ikonsa da darajarsa,
62 Ya ji fushi da jama'arsa, Ya bar abokan gābansu su karkashe su.
63 Aka karkashe samari a cikin yaƙi, 'Yan mata kuma suka rasa ma'aura.
64 Aka karkashe firistoci da takuba, Matansu ba su yi makoki dominsu ba.
65 Daga bisani sai Ubangiji ya tashi Kamar wanda ya farka daga barci, Kamar jarumi wanda ya bugu da ruwan inabi.
66 Ya tura abokan gābansa baya, Da mummunar kora mai bankunya Da ba za su sāke tashi ba.
67 Ubangiji ya rabu da zuriyar Yusufu, Bai kuma zaɓi kabilar Ifraimu ba.
68 A maimakonsu sai ya zaɓi kabilar Yahuza. Ya zaɓi Dutsen Sihiyona, wanda yake ƙauna ƙwarai.
69 A can ya gina Haikalinsa, Kamar wurin zamansa a Sama. Ya kafa shi da ƙarfi kamar duniya, Tabbatacce a kowane lokaci.
70 Ya zaɓi bawansa Dawuda, Ya ɗauko shi daga wurin kiwon tumaki,
71 Ya ɗauko shi daga inda yake lura da 'yan raguna. Ya naɗa shi Sarkin Isra'ila, Ya naɗa shi makiyayin jama'ar Allah.
72 Dawuda kuwa ya lura da su da zuciya ɗaya, Da gwaninta kuma ya bi da su.
1 Ya Allah, arna sun fāɗa wa ƙasar jama'arka! Sun ƙazantar da Haikalinka tsattsarka, Sun bar Urushalima kufai.
2 Suka bar wa tsuntsaye gawawwakin jama'arka su ci, Suka bar wa namomin jeji gawawwakin bayinka.
3 Suka zubar da jinin jama'arka kamar ruwa, Jini ya yi ta gudu kamar ruwa Ko'ina a Urushalima, Ba ma wanda ya ragu don yă binne gawawwaki.
4 Sauran al'ummar da take kewaye da mu, Suka maishe mu abin ba'a, suka yi mana dariya, Suka yi mana ba'a.
5 Har yaushe za ka yi ta fushi da mu, ya Ubangiji? Har abada ne? Kullum ne fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
6 Ka yi fushi da al'umman da ba su yi maka sujada, Ka yi fushi da jama'ar da suka ƙi ka!
7 Sun karkashe mutanenmu, Sun kuwa lalatar da ƙasarmu.
8 Kada ka hukunta mu saboda zunuban kakanninmu, Amma ka yi mana jinƙai yanzu, Gama mun fid da zuciya sarai.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, Saboda girmanka. Ka cece mu, ka gafarta mana zunubanmu, Don mutane su yabe ka.
10 Don me al'ummai za su tambaye mu cewa, “Ina Allahnku?” Bari mu ga ka hukunta al'ummai Saboda sun zubar da jinin bayinka!
11 Ka kasa kunne ga nishin 'yan sarƙa, Ka kuɓutar da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa, Ta wurin ikonka mai girma.
12 Ya Ubangiji, ka rama wa al'umman nan har sau bakwai, Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka.
13 Mu waɗanda muke jama'arka, tumakin garkenka, Za mu gode maka, mu yabe ka har abada.
1 Ka kasa kunne gare mu, ya Makiyayin Isra'ila, Ka ji mu, kai da kake shugaban garkenka, Da kake zaune a kan kursiyinka, a bisa kerubobi.
2 Ka bayyana ƙaunarka ga kabilar Ifraimu, Da ta Biliyaminu, da ta Manassa! Ka nuna mana ikonka, Ka zo ka cece mu!
3 Ka komo da mu, ya Allah! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!
4 Har yaushe ke nan ya Ubangiji Allah Mai Runduna, Za ka yi ta fushi da addu'o'in jama'arka?
5 Ka ciyar da mu da hawaye, Ka shayar da mu da babban ƙoƙo na hawaye.
6 Ka bar al'umman da take makwabtaka da mu Su yi ta faɗa a kan ƙasarmu, Abokan gābanmu kuma suna yi mana ba'a.
7 Ka komo da mu, ya Allah Mai Runduna! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!
8 Ka fito da kurangar inabi daga cikin Masar, Ka kori sauran al'umma, Ka dasa kurangar a ƙasarsu.
9 Ka gyara mata wuri don ta yi girma, Saiwoyinta suka shiga ƙasa sosai, Ta yaɗu, ta rufe dukan ƙasar.
10 Ta rufe tuddai da inuwarta, Ta rufe manya manyan itatuwan al'ul da rassanta.
11 Rassanta sun miƙe har Bahar Rum, Har zuwa Kogin Yufiretis.
12 Me ya sa ka rushe shingen da yake kewaye da ita? Ga shi yanzu, duk mai wucewa yana iya satar 'ya'yanta.
13 Aladen jeji kuma za su tattake ta, Namomin jeji duka za su cinye ta.
14 Ka juyo wurinmu, ya Allah Mai Runduna! Daga Sama, ka dube mu, Ka zo ka ceci kurangar inabinka!
15 Ka zo ka ceci kurangar inabin nan Wadda kai da kanka ka dasa, Wannan ƙaramar kuranga, Ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!
16 Abokan gābanmu sun sa mata wuta, sun sare ta, Ka yi fushi da su, ka hallaka su!
17 Ka kiyaye jama'arka wadda ka zaɓa, Ka keɓe ta. Al'umman nan wadda ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!
18 Ba za mu ƙara rabuwa da kai ba, Ka rayar da mu, mu kuwa za mu yabe ka.
19 Ka komo da mu, ya Ubangiji Allah Mai Runduna! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!
1 Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah Mai Cetonmu, Ku raira yabbai ga Allah na Yakubu!
2 A fara waƙa, ku buga bandiri, Ku yi waƙoƙi masu daɗi da molaye, da garayu.
3 Ku busa ƙaho domin idin, A amaryar wata, Da a tsakiyar farin wata.
4 Wannan doka ce a Isra'ila, Umarni ne kuma daga Allah na Yakubu.
5 Ya ba da wannan umarni ga jama'ar Isra'ila, A lokacin da ya fita gāba da ƙasar Masar. Na ji wata murya da ban saba ji ba tana cewa,
6 “Na ɗauke muku kayayyaki masu nauyi da kuke ɗauke da su a kā, Na sa kuka ajiye kwandunan aikinku.
7 Sa'ad da kuke shan wahala Kuka yi kira a gare ni, na kuwa cece ku. Daga maɓuyata cikin hadiri, na amsa muku, Na jarraba ku a maɓuɓɓugan Meriba.
8 “Ya kuma jama'ata Isra'ila ku kasa kunne, Ina kuwa so ku saurara gare ni.
9 Faufau kada ku bauta wa gumaka, Ko ku yi sujada ga wanina.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku, Wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar. Ku buɗe bakinku, zan ciyar da ku.
11 “Amma jama'ata ba su kasa kunne gare ni ba. Isra'ila ta ƙi yi mini biyayya.
12 Saboda haka na bar su su yi ta kangarewarsu, Su aikata duk irin abin da suka ga dama.
13 Ina kuwa so jama'ata su kasa kunne gare ni, Su kuwa yi mini biyayya!
14 Da sai in kori abokan gābansu nan da nan, In yi nasara da dukan maƙiyansu.
15 Maƙiyana, za su sunkuya a gabana saboda tsoro, Hukuncinsu na har abada ne.
16 Zan ciyar da ku da kyakkyawar alkama, In ƙosar da ku da zuma.”
1 Allah yana matsayinsa a taron jama'arsa, Yakan zartar da nufinsa a taron alloli.
2 Tilas ku daina yin rashin gaskiya a shari'a, Ku daina goyon bayan mugaye!
3 Ku kāre hakkin talakawa da na marayu, Ku yi adalci ga matalauta, Da waɗanda ba su da mataimaki.
4 Ku kuɓutar da talakawa da matalauta, Ku cece su daga ikon mugaye!
5 “Waɗanne irin jahilai ne ku, wawaye! Kuna zaune cikin duhu, Ga shi, ba adalci a duniya sam!
6 Na faɗa muku, ku alloli ne, Cewa dukanku 'ya'ya ne na Maɗaukaki.
7 Amma za ku mutu kamar kowane mutum, Ku fāɗi kamar kowane basarauce.”
8 Ya Allah, ka zo, ka mallaki duniya, Dukan al'ummai naka ne.
1 Ya Allah, kada ka yi shiru, Kada ka tsaya cik, Ya Allah, kada kuma ka yi tsit!
2 Duba, abokan gābanka suna tawaye, Maƙiyanka sun tayar.
3 Suna ta ƙulle-ƙulle a asirce gaba da jama'arka, Suna shirya maƙarƙashiya gāba da waɗanda kake tsaronsu.
4 Suna cewa, “Ku zo, mu hallakar da al'ummarsu, Don a manta da Isra'ila har abada!”
5 Suka yarda a kan abin da suka shirya, Suka haɗa kai gāba da kai.
6 Su ne mutanen Edom, da Isma'ilawa, Da mutanen Mowab, da Hagarawa,
7 Da mutanen Gebal, da na Ammon, da na Amalek, Da na Filistiya, da na Taya.
8 Assuriya ma ta haɗa kai da su, Haɗa kai ke nan mai ƙarfi da zuriyar Lutu.
9 Ka yi musu yadda ka yi wa Madayanawa, Ka yi musu yadda ka yi wa Sisera Da Yabin a Kogin Kishon,
10 Waɗanda aka kora a Endor, Gawawwakinsu kuwa suka ruɓe a ƙasa.
11 Ka yi wa shugabannin yaƙinsu yadda ka yi wa Oreb da Ziyib, Ka kori dukan masu mulkinsu yadda ka kori Zeba da Zalmunna,
12 Waɗanda suka ce, “Za mu ƙwace ƙasar da take ta Allah, ta zama tamu.”
13 Ya Allahna, ka warwatsa su kamar ƙura, Ka warwatsa su kamar ciyayin da iska take hurawa.
14 Kamar yadda wuta take cin jeji, Kamar yadda harshen wuta yake ƙone tuddai,
15 Ka runtume su da hadirinka, Ka razanar da su da iskarka mai ƙarfi.
16 Ya Ubangiji, ka sa kunya ta rufe su, Don su so su bauta maka.
17 Ka sa a kore su, a razanar da su har abada, Ka sa su mutu, mutuwar ƙasƙanci!
18 Ka sa su sani kai kaɗai ne Ubangiji, Kai kaɗai ne mamallakin dukan duniya!
1 Ina ƙaunar Haikalinka ƙwarai, Ya Allah Mai Iko Dukka!
2 A can nake so in kasance! Ina marmarin farfajiyar Haikalin Ubangiji. Da farin ciki mai yawa zan raira waƙa ga Allah Mai Rai.
3 Har ba'u ma sukan yi sheƙa, Tsattsewa suna da sheƙunansu, A kusa da bagadanka suke kiwon 'ya'yansu. Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina, Allahna.
4 Masu murna ne waɗanda suke zaune a Haikalinka, Kullum suna raira yabonka!
5 Masu murna ne waɗanda suka sami ƙarfinsu daga gare ka, Su waɗanda suka ƙosa su kai ziyara a Dutsen Sihiyona.
6 Sa'ad da suke ratsa busasshen kwari, Sai ya zama maɓuɓɓugar ruwa, Ruwan sama na farko yakan rufe wurin da tafkuna.
7 Sukan yi ta ƙara jin ƙarfi a cikin tafiyarsu, Za su kuwa ga Allahn alloli a Sihiyona!
8 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji Allah Mai Runduna, Ka ji ni, ya Allah na Yakubu!
9 Duba, ya Allah, kai ne garkuwarmu, Ka dubi fuskar Sarkinmu, zaɓaɓɓenka.
10 Kwana guda da za a yi a Haikalinka, Ya fi kwana dubu da za a yi a wani wuri dabam. Na gwammace in tsaya a ƙofar Haikalin Allahna, Da in zauna a gidajen mugaye.
11 Ubangiji shi ne makiyayinmu, sarkinmu mai daraja, Yakan sa mana albarka, da alheri, da daraja, Ba ya hana kowane abu mai kyau ga waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
12 Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka, Ya Allah Mai Runduna!
1 Ya Ubangiji, ka yi wa ƙasarka alheri, Ka sāke arzuta Isra'ila kuma.
2 Ka gafarta wa jama'arka zunubansu, Ka kuwa gafarta musu dukan kuskurensu,
3 Ka daina yin fushi da su, Ka kuwa kawar da zafin fushinka.
4 Ka komo da mu, ya Allah Mai Cetonmu, Ka daina jin haushinmu!
5 Za ka yi fushi da mu har abada? Ba za ka taɓa hucewa ba?
6 Ka daɗa mana ƙarfi, ka yarda ka sabunta ƙarfinmu, Mu kuwa, jama'arka, za mu yabe ka.
7 Ka ƙaunace mu da madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ka taimake mu da cetonka.
8 Ina kasa kunne ga abin da Ubangiji Allah yake cewa, Mu da muke mutanensa, ya alkawarta mana salama, Idan ba mu koma kan al'amuranmu na wauta ba.
9 Hakika a shirye yake yă ceci waɗanda suke girmama shi, Kasancewarsa a ƙasar, ceto ne ga ƙasar.
10 Ƙauna da aminci za su sadu wuri ɗaya, Adalci da salama za su gamu.
11 Amincin mutum zai yunƙura daga duniya, yă nufi sama. Adalcin Allah kuwa zai dubo daga Sama.
12 Ubangiji zai arzuta mu, Ƙasarmu kuwa za ta ba da amfanin gona mai yawa.
13 Adalci zai yi tafiya a gaban Ubangiji, Yă shirya masa tafarki.
1 Ka kasa kunne gare ni, ya Ubangiji, ka amsa mini, Gama ba ni da ƙarfi, ba ni kuwa da mataimaki.
2 Ka cece ni daga mutuwa, saboda ni mai aminci ne a gare ka, Ka cece ni saboda ni bawanka ne, ina kuwa dogara gare ka.
3 Kai ne Allahna, saboda haka ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, Ina yin addu'a a gare ka dukan yini.
4 Ka sa bawanka yă yi murna, ya Ubangiji, Saboda addu'o'ina sun hau zuwa gare ka.
5 Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara, Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka.
6 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka ji kukana na neman taimako!
7 Nakan kira gare ka a lokacin wahala, Saboda kakan amsa addu'ata.
8 Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji, Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa.
9 Dukan sauran al'umma da ka halitta Za su zo su rusuna har ƙasa a gabanka. Za su yabi girmanka,
10 Gama kai kaɗai ne Maɗaukaki, ya Allah, Kai kaɗai ne ka aikata abubuwa na banmamaki.
11 Ya Ubangiji, ka koya mini abin da kake so in yi, Ni kuwa zan yi maka biyayya da aminci. Ka koya mini in bauta maka da zuciya ɗaya.
12 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji Allahna, Zan riƙa shelar girmanka har abada.
13 Wane irin girma madawwamiyar ƙaunarka take da shi a gare ni! Gama ka cece ni daga zurfin kabari.
14 Masu girmankai sun tasar mini, ya Allah, Ƙungiyar mugaye tana ƙoƙari ta kashe ni, Mutanen da ba su kula da kai ba.
15 Ya Ubangiji, kai Allah ne mai jinƙai, mai ƙauna, Mai jinkirin fushi, kullum kai mai alheri ne, mai aminci.
16 Ka juyo gare ni, ka yi mini jinƙai, Ka ƙarfafa ni, ka cece ni, Gama ina bauta maka, kamar yadda mahaifiyata ta yi.
17 Ka nuna mini alherinka, ya Ubangiji, Sa'an nan su waɗanda suke ƙina za su sha kunya, Sa'ad da suka ga ka ta'azantar da ni, Ka kuma taimake ni.
1 Allah ya gina birninsa a bisa tsarkakan tuddai,
2 Yana ƙaunar birnin Urushalima fiye da kowane wuri a Isra'ila.
3 Ya birnin Allah, ka kasa kunne, Ga abubuwan banmamaki da ya faɗa a kanka.
4 “Sa'ad da na lasafta sauran al'umma da suke yi mini biyayya, Zan sa Masar da Babila a cikinsu, Zan ce da Filistiya, da Taya, da Habasha, Su ma na Urushalima ne.”
5 A kan Sihiyona kuwa za a ce, “Dukan sauran al'umma nata ne.” Maɗaukaki kuwa zai ƙarfafa ta.
6 Ubangiji zai rubuta lissafin jama'o'i, Ya sa su duka cikin jimilla ta Urushalima.
7 Duk mazauna a wurin za su raira waƙa, su yi rawa, Su ce, “Dukan maɓuɓɓugaina suna cikinka.”
1 Ya Ubangiji Allah, Mai Cetona, Duk yini ina ta kuka, Da dare kuma na zo gare ka.
2 Ka ji addu'ata, Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako!
3 Wahala mai yawa ta auko mini, Har ina gab da mutuwa.
4 Ina daidai da sauran mutanen da suke gab da mutuwa, Dukan ƙarfina ya ƙare.
5 An yashe ni a cikin matattu, Kamar waɗanda aka karkashe, Suna kuma kwance cikin kaburburansu, Waɗanda ka manta da su ɗungum, Waɗanda taimakonka ya yi musu nisa.
6 Ka jefar da ni cikin zurfin kabari, Da cikin rami mafi zurfi, mafi duhu.
7 Fushinka yana da nauyi a kaina, An turmushe ni a cikin tuƙuƙinka.
8 Ka sa abokaina su yashe ni, Ka sa sun ware ni. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta.
9 Idanuna sun raunana saboda wahala. Ya Ubangiji, kowace rana ina kira gare ka, Ina ta da hannuwana zuwa gare ka da addu'a!
10 Kakan yi wa matattu mu'ujizai ne? Sukan tashi su yabe ka?
11 Akan yi maganar madawwamiyar ƙaunarka a kabari? Ko amincinka a inda ake hallaka?
12 Za a iya ganin mu'ujizanka a cikin duhu? Ko kuwa alherinka a lahira?
13 Ya Ubangiji, ina kira gare ka, neman taimako, Kowace safiya nakan yi addu'a gare ka.
14 Me ya sa ka yashe ni, ya Ubangiji? Me ya sa ka ɓoye kanka daga gare ni?
15 Tun ina ƙarami nake shan wahala, Har ma na kusa mutuwa, Na tafke saboda nauyin hukuncinka.
16 Hasalarka ta bi ta kaina, Tasar mini da kake ta yi, ta hallaka ni.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa, Ta kowace fuska, sun rufe ni.
18 Ka sa har abokaina na kusa sun yashe ni, Duhu ne kaɗai abokin zamana.
1 Ya Ubangiji zan raira waƙar Madawwamiyar ƙaunarka koyaushe, Zan yi shelar amincinka a dukan lokaci.
2 Na sani ƙaunarka za ta dawwama har abada, Amincinka kuma tabbatacce ne kamar sararin sama.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da mutumin da na zaɓa, Na yi wa bawana Dawuda alkawari cewa,
4 ‘Daga zuriyarka kullum za a sami sarki, Zan kiyaye mulkinka har abada.’ ”
5 Talikan da suke Sama suna raira waƙa a kan Abubuwan banmamakin da kake yi, Suna raira waƙa kan amincinka, ya Ubangiji.
6 Ba wani kamarka a Sama, ya Ubangiji, Ba wani daga su cikin talikai da yake daidai da kai.
7 Ana girmama ka a cikin majalisar talikai, Duk waɗanda suke kewaye da kai suna yin tsoronka ƙwarai.
8 Ya Ubangiji Allah, Mai Runduna, Ba wani mai iko kamarka, Kai mai aminci ne a kowane abu.
9 Kai kake mulkin haukan teku, Kakan kwantar da haukan raƙuman ruwa.
10 Ka ragargaza dodon nan Rahab, ka kashe shi, Da ƙarfin ikonka ka cinye maƙiyanka.
11 Duniya taka ce, haka ma samaniya taka ce, Kai ne ka halicci duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Kai ne ka yi kudu da arewa, Dutsen Tabor da Dutsen Harmon Suna raira waƙa gare ka don farin ciki.
13 Kai kake da iko! Kai kake da ƙarfi!
14 A gaskiya da adalci aka kafa mulkinka, Akwai ƙauna da aminci a dukan abin da kake yi.
15 Masu farin ciki ne jama'ar da suke yi maka sujada, suna raira waƙoƙi, Waɗanda suke zaune a hasken alherinka.
16 Suna murna dukan yini saboda da kai, Suna kuwa yabonka saboda alherinka.
17 Kana sa mu ci babbar nasara, Da alherinka kakan sa mu yi rinjaye,
18 Sabili da ka zaɓar mana mai kāre mu, Kai, Mai Tsarki na Isra'ila, Kai ne ka ba mu sarkinmu.
19 Ka faɗa wa amintattun bayinka a wahayin da ka nuna musu tun da daɗewa, ka ce, “Na sa kambin sarauta a kan shahararren soja, Na ba da gadon sarauta ga wanda aka zaɓa daga cikin jama'a.
20 Na zaɓi bawana Dawuda, Na naɗa shi sarkinku.
21 Ƙarfina zai kasance tare da shi, Ikona kuma zai ƙarfafa shi.
22 Abokan gābansa ba za su taɓa cin nasara a kansa ba, Mugaye ba za su kore shi ba.
23 Zan ragargaza magabtansa, In karkashe duk waɗanda suke ƙinsa.
24 Zan ƙaunace shi kullum, in amince da shi, Zan sa ya yi nasara kullayaumin.
25 Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum, Har zuwa Kogin Yufiretis.
26 Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna, Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’
27 Zan maishe shi ɗan farina, Mafi girma daga cikin dukan sarakuna.
28 Zan riƙa ƙaunarsa har abada, Alkawarin da na yi da shi kuma zai tabbata har abada.
29 A kullayaumin daga cikin zuriyarsa ne za a naɗa sarki, Mulkinsa zai dawwama kamar sararin sama.
30 “Amma idan zuriyarsa sun ƙi yin biyayya da shari'ata, Ba su kuwa zauna cikin ka'idodina ba,
31 In sun ƙyale koyarwata, Ba su kiyaye umarnaina ba,
32 To, sai in hukunta su saboda zunubansu, Zan bulale su saboda laifofinsu.
33 Amma fa, ba zan daina ƙaunar Dawuda ba, Ba kuwa zan rasa cika alkawarin da na yi masa ba.
34 Ba zan keta alkawarin da na yi masa ba, Ba zan soke ko ɗaya daga cikin alkawaran da na yi masa ba.
35 “Da sunana mai tsarki na yi alkawari sau ɗaya tak, Ba zan yi wa Dawuda ƙarya ba!
36 Zuriyarsa za ta kasance kullum, Zan lura da mulkinsa muddin rana tana haskakawa.
37 Zai dawwama kamar wata, Kamar amintaccen mashaidin nan da yake a sararin sama.”
38 Amma kana fushi da zaɓaɓɓen sarkinka, Ka rabu da shi, ka yashe shi.
39 Ka soke alkawarinka wanda ka yi wa bawanka, Ka jefar da kambinsa a cikin ƙazanta.
40 Ka rurrushe garun birninsa, Ka mai da sansaninsa mai kagara kufai.
41 Dukan waɗanda suke wucewa za su sace masa kayansa, Maƙwabtansa duka suna yi masa ba'a.
42 Ka ba maƙiyansa nasara, Ka sa dukansu su yi murna.
43 Ka sa makamansa su zama marasa amfani, Ka bari a ci shi da yaƙi.
44 Ka ƙwace masa sandan sarautarsa, Ka buge gadon sarautarsa ƙasa.
45 Ka sa shi ya tsofe kafin lokacinsa, Ka rufe shi da kunya.
46 Har yaushe za ka ɓoye kanka, ya Ubangiji? Har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Ka tuna kwanakin mutum kaɗan ne, ya Ubangiji, Ka tuna yadda ka halicci mutane duka masu mutuwa ne!
48 Wa zai rayu har abada, ba zai mutu ba? Ƙaƙa mutum zai hana kansa shiga kabari?
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunarka ta dā? Ina alkawaran nan waɗanda ka yi wa Dawuda?
50 Kada ka manta da yadda aka ci mutuncina, ni da nake bawanka, Da yadda na daure da dukan cin mutuncin da arna suka yi mini.
51 Ya Ubangiji, kada ka manta da yadda maƙiyanka suka ci mutuncin zaɓaɓɓen sarki da ka naɗa! Suka yi ta cin mutuncinsa duk inda ya tafi.
52 Mu yabi Ubangiji har abada! Amin! Amin!
1 Ya Ubangiji, a koyaushe kai ne wurin zamanmu.
2 Kafin a kafa tuddai, Kafin kuma ka sa duniya ta kasance, Kai Allah ne, Madawwami. Ba ka da farko, ba ka da ƙarshe.
3 Kakan sa mutane su koma yadda suke, Su zama ƙura.
4 A gare ka shekara dubu, kamar kwana ɗaya ne, Kamar jiya ce wadda ta shige, Gajeruwa ce kamar sa'a guda ta dare.
5 Kakan kwashe mutane kamar yadda ambaliyar ruwa take yi, Kamar mafarki suke, ba su daɗewa. Kamar tsire-tsire suke waɗanda suke tsirowa da safe,
6 Su yi girma har su yi huda, Sa'an nan su yi yaushi su bushe da yamma.
7 Mun halaka ta wurin fushinka, Mun razana saboda hasalarka.
8 Ka jera zunubanmu a gabanka, Zunubanmu na ɓoye kuwa, Ka sa su a inda za ka gan su.
9 Fushinka ya gajerta tsawon ranmu, Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya.
10 Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba'in, In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne. Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaru Suke kawo mana, damuwa ce da wahala, Nan da nan sukan wuce, Tamu da ƙare.
11 Wa ya san iyakar ikon fushinka? Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo?
12 Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne, Domin mu zama masu hikima.
13 Ya Ubangiji, sai yaushe za ka ji tausayinmu? Ka ji tausayin bayinka!
14 Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya, Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu.
15 Yanzu sai ka sa mu yi farin ciki mai yawa, Kamar yadda ka sa muka yi baƙin ciki A dukan shekarun nan, da muka sha wahala.
16 Ka yarda mana, mu bayinka, mu ga ayyukanka masu girma, Ka yardar wa zuriyarmu su ga ikonka mai girma.
17 Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu. Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi! I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!
1 Duk wanda ya je wurin Maɗaukaki Zai zauna lafiya, Duk wanda yake zaune a inuwar Mai Iko Dukka,
2 Ya iya ce wa Ubangiji, “Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni! Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!”
3 Hakika zai kiyaye ka Daga dukan hatsarorin da ka ɓoye, Daga kuma dukan mugayen cuce-cuce.
4 Zai rufe ka da fikafikansa, Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu. Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.
5 Ba za ka ji tsoron hatsarori da dare ba, Ko fāɗawar da za a yi maka da rana,
6 Ko annobar da take aukowa da dare, Ko mugayen da suke kisa da tsakar rana.
7 Mutum dubu za su fāɗi daura da kai, Dubu goma kuma za su fāɗi dama da kai, Amma kai, ba za a cuce ka ba.
8 Da idonka za ka duba, Ka ga yadda ake hukunta wa mugaye.
9 Domin ka ɗauka Ubangiji yake kiyaye ka, Maɗaukaki ne yake tsaronka,
10 To, ba bala'in da zai same ka, Ba za a yi wa gidanka aikin ƙarfi da yaji ba.
11 Allah zai sa mala'ikunsa su lura da kai, Za su kiyaye ka duk inda za ka tafi.
12 Za su ɗauke ka a hannuwansu, Don kada ka buga ƙafarka a dutse.
13 Za ka tattake zakoki da macizai, Za ka tattake zakoki masu zafin rai Da macizai masu dafi.
14 Allah ya ce, “Zan ceci waɗanda suke ƙaunata, Zan kiyaye waɗanda suka san ni.
15 Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.
16 Zan ba su tsawon rai lada, Hakika kuwa zan cece su.”
1 Abu mai kyau ne a yi wa Ubangiji godiya, A raira waƙa don girmansa, Allah mafi ɗaukaka,
2 A yi shelar madawwamiyar ƙaunarka kowace safiya, Amincinka kuma kowane maraice,
3 Da abubuwan kaɗe-kaɗe masu tsarkiya, Da amon garaya mai daɗi.
4 Ya Ubangiji, Ayyukanka masu iko suna sa ni murna, Saboda abin da ka aikata Ina raira waƙa domin farin ciki.
5 Ayyukanka da girma suke, ya Ubangiji! Tunaninka da zurfi suke!
6 Ga wani abin da wawa ba zai iya sani ba, Dakiki kuma ba zai iya ganewa ba,
7 Shi ne mai yiwuwa ne mugu ya yi girma kamar tsire-tsire, Masu aikata mugayen ayyuka kuma su arzuta, Duk da haka za a hallaka su ɗungum.
8 Gama kai, ya Ubangiji, Maɗaukaki ne har abada.
9 Mun sani maƙiyanka za su mutu, Dukan mugaye kuwa za a yi nasara da su.
10 Ka sa ni na yi ƙarfi kamar bijimi mai faɗa, Ka sa mini albarka da farin ciki.
11 Na ga fāɗuwar maƙiyana, Na ji kukan mugaye.
12 Adalai za su yi yabanya Kamar itatuwan giginya, Za su yi girma kamar itatuwan al'ul na Lebanon.
13 Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji, Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu.
14 Waɗanda suke yin 'ya'ya da tsufansu, A kullum kuwa kore shar suke, Suna da ƙarfinsu kuma.
15 Wannan ya nuna Ubangiji adali ne, Shi wanda yake kāre ni, Ba kuskure a gare shi.
1 Ubangiji sarki ne! Yana saye da ɗaukaka, suturarsa ƙarfi ne. Hakika duniya ta kahu sosai a inda take, Ba kuwa za ta jijjigu ba.
2 Kursiyinka, ya Ubangiji, ya kahu tun daga farko, Kana nan tun fil azal.
3 Ya Ubangiji, zurfafan teku suna ta da muryarsu, Suna ta da muryarsu da ruri.
4 Ubangiji yana mulki cikin Sama, Mulkinsa mafifici ne, Fiye da rurin teku, Fiye da ikon raƙuman ruwan teku.
5 Dokokinka dawwamammu ne, ya Ubangiji, Haikalinka kuwa tsattsarka ne ƙwarai, Har abada abadin.
1 Ya Ubangiji, kai Allah ne wanda yake yin hukunci, Ka bayyana fushinka!
2 Kai ne mai yi wa dukan mutane shari'a, Ka tashi, ka sāka wa masu girmankai Abin da ya dace da su!
3 Har yaushe mugaye za su yi ta murna? Har yaushe ne, ya Ubangiji?
4 Har yaushe za su yi shakiyanci, Su yi ta ɗaga kai? Har yaushe, ya Ubangiji?
5 Suna ragargaza jama'arka, ya Ubangiji, Suna zaluntar waɗanda suke naka.
6 Suna karkashe gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, Da kuma baƙin da suke zaune a ƙasarmu.
7 Suna cewa, “Ai, Ubangiji ba ya ganinmu, Allah na Isra'ila ba ya lura da abin da yake faruwa!”
8 Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka? Sai yaushe za ku koya?
9 Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba? Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba?
10 Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba? Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?
11 Ubangiji ya san tunaninsu, Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali.
12 Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa, Mutumin da kake koya masa shari'arka.
13 Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala, Kafin a haƙa wa mugaye kabari.
14 Ubangiji ba zai rabu da jama'arsa ba, Ba zai rabu da waɗanda suke nasa ba.
15 Adalci kuma zai sāke dawowa cikin majalisun alƙalai, Dukan adalai kuwa za su yi na'am da shi.
16 Wa zai tsaya mini gāba da mugaye? Wa zai goyi bayana gāba da masu aikata mugunta?
17 Da ba domin Ubangiji ya taimake ni ba, Ai, da tuni na kai ƙasar da ba a motsi.
18 Na ce, “Ina kan fāɗuwa,” Amma, ya Ubangiji, madawwamiyar ƙaunarka ta riƙe ni.
19 Sa'ad da nake alhini, ina cikin damuwa, Ka ta'azantar da ni, ka sa in yi murna.
20 Ba ruwanka da alƙalai azzalumai, marasa gaskiya, Waɗanda suka mai da rashin gaskiya ita ce gaskiyarsu,
21 Sukan shirya wa mutanen kirki maƙarƙashiya, Sukan yanke wa marar laifi hukuncin kisa.
22 Amma Ubangiji yakan kāre ni, Allahna yakan kiyaye ni.
23 Shi zai hukunta su saboda muguntarsu, Ya hallaka su saboda zunubansu. Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
1 Ku zo mu yabi Ubangiji! Mu raira waƙa domin farin ciki ga mai kiyaye mu, Da Mai Cetonmu!
2 Mu zo gabansa da godiya, Mu raira waƙoƙin farin ciki na yabo!
3 Gama Ubangiji Allah ne mai iko, Shi yake mulki bisa sauran alloli duka.
4 Yana mulki bisa dukan duniya, Daga zurfafan kogwannin duwatsu zuwa tuddai mafiya tsayi.
5 Yana mulki bisa tekun da ya yi, Da kuma bisa ƙasar da ya siffata.
6 Ku zo, mu durƙusa, mu yi masa sujada, Mu durƙusa a gaban Ubangiji, Mahaliccinmu!
7 Shi ne Allahnmu, Mu ne jama'ar da yake lura da ita, Mu ne kuma garken da yake ciyarwa. Yau ku ji abin da yake faɗa.
8 “Kada ku taurare zuciyarku yadda kakanninku suka yi a Meriba, Kamar yadda suka yi a jeji a Masaha, a wancan rana.
9 A can suka gwada ni suka jarraba ni, Ko da yake da idanunsu suka ga abin da na yi dominsu.
10 A shekara arba'in ɗin nan, Jama'ar nan ta zama abar ƙyama gare ni, ‘Su marasa biyayya ne,’ in ji ni, ‘Gama sun ƙi bin umarnaina!’
11 Sai na ji haushi, na yi musu alkawari mai nauyi. Na ce, ‘Faufau ba za ku shiga ƙasar da zan ba ku hutawa a ciki ba.’ ”
1 Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji! Ku raira waƙa ga Ubangiji, ya duniya duka!
2 Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku yabe shi! Kowace rana ku ba da labari mai daɗi cewa, “Ya cece mu!”
3 Ku yi shelar ɗaukakar Ubangiji ga sauran al'umma, Ku yi shelar ayyukansa masu girma ga dukan kabilai.
4 Ubangiji da girma yake, tilas a ɗaukaka shi, Tilas a fi jin tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Allolin dukan al'ummai, gumaka ne kawai, Amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi, Girma da jamali suna cikin Haikalinsa.
7 Dukan jama'ar da suke bisa duniya su yabi Ubangiji! Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa!
8 Ku yabi sunan Ubangiji mai ɗaukaka, Ku kawo sadaka, ku shiga Haikalinsa.
9 Ku durƙusa a gaban Mai Tsarki, sa'ad da ya bayyana, Ku yi rawar jiki a gabansa, ku duniya duka!
10 A faɗa wa dukan sauran al'umma, “Ubangiji Sarki ne! Duniya ta kahu da ƙarfi a wurin zamanta, Ba za a iya kaushe ta ba, Shi zai shara'anta dukan jama'a da adalci.”
11 Duniya da sararin sama, ku yi murna! Ki yi ruri, ya ke teku da dukan masu rai da suke cikinki,
12 Ku yi murna ya ku filaye da dukan abubuwan da suke cikinku! Sa'an nan itatuwan da suke cikin kurama Za su ta da murya saboda farin ciki
13 A gaban Ubangiji, gama ya zo ne ya mallaki duniya. Zai mallaki dukan jama'ar duniya Da adalci da gaskiya.
1 Ubangiji Sarki ne! Ki yi murna ke duniya! Ku yi murna, dukanku tsibiran da suke cikin tekuna!
2 Gajimare da duhu sun kewaye shi. A kan adalci da gaskiya ya kafa mulkinsa.
3 Wuta tana tafe a gabansa, tana cinye maƙiyansa Waɗanda suke kewaye da shi.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya, Duniya kuwa ta gani ta yi ta rawar jiki.
5 Tuddai sun narke a gaban Ubangiji kamar kākin zuma, A gaban Ubangijin dukan duniya.
6 Sammai suna shelar adalcinsa, Dukan kabilai kuwa, sun ga ɗaukakarsa.
7 Dukan waɗanda suke yi wa siffofi sujada za su sha kunya, Haka kuma waɗanda suke fāriya da gumakansu. Dukan alloli za su rusuna a gabansa.
8 Jama'ar Sihiyona suna murna, Garuruwan Yahuza kuma suna farin ciki, Sabili da irin shari'unka, ya Ubangiji!
9 Ya Ubangiji Mai Iko Dukka, kai kake mulkin dukan duniya, Ka fi sauran alloli duka girma.
10 Ubangiji yana ƙaunar masu ƙin mugunta. Yakan kiyaye rayukan jama'arsa, Yakan cece su daga ikon mugaye.
11 Haske yakan haskaka adalai, Haka kuma murna ta cika ga masu nagarta.
12 Dukanku adalai ku yi murna, Saboda abin da Ubangiji ya yi! Ku tuna da abin da Mai Tsarki ya yi, Ku yi masa godiya!
1 Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji, Gama ya aikata ayyuka masu banmamaki! Ta wurin ikonsa, da ƙarfinsa mai tsarki ya yi nasara.
2 Ubangiji ya bayyana cin nasararsa, Ya sanar da ikonsa na ceto ga sauran al'umma.
3 Ya cika alkawarinsa wanda ya yi wa jama'ar Isra'ila, Da tabbatacciyar ƙauna da aminci. Dukan mutane ko'ina sun ga nasarar Allahnmu!
4 Ku raira waƙa ta farin ciki ga Ubangiji. Dukanku waɗanda suke a duniya, Ku yabe shi da waƙoƙi, kuna ta da murya da ƙarfi, Saboda farin ciki!
5 Ku raira yabbai ga Ubangiji da garayu, Ku kaɗa garayu!
6 Ku busa kakaki da ƙahoni, Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, Sarki!
7 Ki yi ruri, ya ke teku, Ke da dukan masu rai waɗanda suke cikinki, Ki raira waƙa, ke duniya, Da dukan waɗanda suke zaune cikinki!
8 Ku yi tāfi, ya ku tekuna, Ku raira waƙa tare, ya ku tuddai, don farin ciki.
9 A gaban Ubangiji, gama ya zo ne ya yi mulki bisa duniya! Zai yi mulki bisa dukan jama'ar duniya da adalci da gaskiya.
1 Ubangiji Sarki ne, Mutane suna rawar jiki, Yana zaune a bisa kursiyinsa a bisa kerubobi, Duniya ta girgiza.
2 Ubangiji mai iko ne a Sihiyona, Shi ne yake mulki a bisa dukan sauran al'umma.
3 Kowa da kowa zai yabi sunansa mai girma, Maɗaukaki, Mai Tsarki ne shi!
4 Maɗaukaki kana ƙaunar abin da yake daidai, Ka kawo adalci cikin Isra'ila, Ka kawo adalci da gaskiya.
5 Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a gaban kursiyinsa! Mai Tsarki ne shi!
6 Musa da Haruna firistocinsa ne, Sama'ila kuma mai yi masa sujada ne. Suka yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa musu.
7 Ya yi magana da su daga girgije, Suka yi biyayya da dokoki da umarnai da ya ba su.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa wa jama'arka, Ka nuna musu, kai Allah ne mai yin gafara, Amma kakan hukunta su saboda zunubansu.
9 Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a bisa dutsensa mai tsarki! Ubangiji Allahnmu Mai Tsarki ne!
1 Bari dukan duniya ta raira waƙar farin ciki ga Ubangiji!
2 Ku yi wa Ubangiji sujada da murna, Ku zo gabansa, kuna raira waƙoƙin farin ciki!
3 Kada fa a manta da cewa, Ubangiji shi ne Allah! Shi ne ya yi mu, mu kuwa nasa ne, Mu jama'arsa ne, mu garkensa ne.
4 Ku shiga Haikalinsa da godiya, Ku shiga wurinsa mai tsarki, ku yabe shi! Ku gode masa, ku yabe shi!
5 Ubangiji nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce, Amincinsa kuwa har abada abadin ne.
1 Waƙata ta aminci ce da gaskiya. Ina raira maka ita, ya Ubangiji.
2 Abin da nake yi ba zai zama laifi ba, Yaushe za ka zo wurina? Da zuciya mai tsabta zan zauna a gidana.
3 Ba zan jure da mugunta ba ko kaɗan. Na ƙi jinin ayyukan waɗanda suka bijire wa Allah, Ba ruwana da su.
4 Ba zan yi rashin aminci ba, Ba kuwa zan yi tunanin mugunta ba.
5 Zan hallakar da mai raɗar abokinsa, Ba zan jure da mutum mai girmankai, Ko mai alfarma ba.
6 Zan yarda da waɗanda suke amincewa da Allah, Zan yardar musu si yi zamansu a fādata, Zan yarda wa waɗanda suke da tabbataccen aminci Su yi mini hidima.
7 Maƙaryaci ba zai zauna a fādata ba, Ba zan yarda munafuki ya yi zamansa a wurina ba.
8 A kowace rana zan yi ta karkashe dukan mugayen da suke cikin ƙasarmu, Zan kori dukan mugaye daga birnin Ubangiji.
1 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka ji kukana na neman taimako!
2 Kada ka ɓoye mini sa'ad da nake shan wahala! Ka ji ni, ka amsa mini da sauri sa'ad da na yi kira!
3 Raina ya ɓace kamar hayaƙi, Jikina yana ƙuna kamar wuta.
4 An tattake ni kamar busasshiyar ciyarwa, Ba ni da marmarin cin abinci.
5 Ina nishi da ƙarfi, Ba abin da ya ragu gare ni, In banda ƙashi da fata.
6 Ni kamar tsuntsu nake cikin hamada, Kamar mujiya a kufai.
7 Kwana nake ba barci, Na zama kamar tsuntsun da yake fama da kewa A bisa kan ɗaki.
8 Maƙiyana suna cin mutuncina dukan yini. Waɗanda suke mini ba'a, Suna la'antarwa da sunana.
9 Toka ce abincina, Hawayena kuwa sun gauraya da abin shana,
10 Sabili da fushinka da hasalarka. Ka ɗauke ni, ka jefar da ni.
11 Raina kamar inuwar maraice yake, Kamar busasshiyar ciyawa nake.
12 Amma kai, ya Ubangiji, sarki ne kai har abada, Dukan zamanai masu zuwa za su tuna da kai.
13 Za ka tashi ka ji tausayin Sihiyona, Lokaci ya yi da za ka yi mata jinƙai, Wannan shi ne lokacin!
14 Bayinka suna ƙaunarta, Ko da yake an hallakar da ita, Suna jin tausayinta, Ko da yake ta zama kufai.
15 Sauran al'umma za su ji tsoron Ubangiji, Dukan sarakunan duniya za su ji tsoron ikonsa.
16 Sa'ad da Ubangiji ya sāke gina Sihiyona Zai bayyana girmansa.
17 Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita, Zai kuwa ji addu'arta.
18 Ku rubuta abin da Ubangiji ya aikata don zamani mai zuwa, Don waɗanda ba a haife su ba tukuna, Su ma su yabe shi.
19 Ubangiji ya duba ƙasa Daga Sama, tsattsarkan wurinsa, Daga Sama ya dubi duniya,
20 Don ya ji nishin ɗaurarru, Don ya saki waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa.
21 Saboda wannan mutane za su yi shelar sunan Ubangiji a Sihiyona, Za su yi masa godiya a Urushalima,
22 Sa'ad da sauran al'umma da mulkoki suka taru Don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Tun ina ƙaramin yaro Ubangiji ya sa na rasa ƙarfi, Ya gajerta kwanakina.
24 Ya Allahna, kada ka ɗauke ni a yanzu, Tun da yake ban tsufa ba tukuna! Ya Ubangiji har abada kake.
25 Ka halicci duniya tun tuntuni, Da ikonka ne ka yi sammai.
26 Su za su ɓace duka, amma kai za ka dawwama, Za su ƙare kamar yadda tufafi suke ƙarewa, Za ka sāke su kamar tufafi, za su kuwa ɓace.
27 Amma kai, kana yadda kake kullayaumin, Har abada kake.
28 'Ya'yanmu za su yi zaman lafiya, Zuriyarsu kuma za su zauna cikin kiyayewarka kullayaumin.
1 Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ka yabi sunansa mai tsarki!
2 Ka yabi Ubangiji, ya raina, Kada ka manta da yawan alherinsa.
3 Ya gafarta dukan zunubaina, Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.
4 Ya cece ni daga kabari, Ya sa mini albarka da ƙauna da jinƙai.
5 Ya cika raina da kyawawan abubuwa, Don in zauna gagau, Ƙaƙƙarfa kamar gaggafa.
6 Ubangiji yakan yi wa waɗanda ake zalunta shari'a ta gaskiya. Yakan ba su hakkinsu.
7 Ya faɗa wa Musa shirye-shiryensa. Ya yardar wa jama'ar Isra'ila su ga manyan ayyukansa.
8 Ubangiji mai jinƙai ne, mai ƙauna ne kuma, Mai jinƙirin fushi ne, cike yake da madawwamiyar ƙauna.
9 Ba zai yi ta tsautawa kullum ba, Ba zai yi ta jin haushi har abada ba.
10 Yakan yi mana rangwame sa'ad da yake hukunta mu, Ko sa'ad da yake sāka mana saboda zunubanmu da laifofinmu.
11 Kamar yadda nisan sararin sama yake bisa kan duniya, Haka kuma girman ƙaunarsa yake ga waɗanda suke tsoronsa.
12 Kamar yadda gabas take nesa da yamma, Haka nan ne ya nisantar da zunubanmu daga gare mu.
13 Kamar yadda uba yake yi wa 'ya'yansa alheri, Haka nan kuwa Ubangiji yake yi wa masu tsoronsa alheri.
14 Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi, Yakan tuna, da ƙura aka yi mu.
15 Mutum fa, ransa kamar ciyawa ne, Yakan yi girma, ya yi yabanya kamar furen jeji.
16 Sa'an nan iska ta bi ta kansa, yakan ɓace, Ba mai ƙara ganinsa.
17 Amma ƙaunar Ubangiji ga waɗanda suke girmama shi har abada ce. Alherinsa kuwa tabbatacce ne har dukan zamanai,
18 Ga waɗanda suke riƙe da alkawarinsa da gaskiya, Waɗanda suke biyayya da umarnansa da aminci.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a Sama, Shi yake sarautar duka.
20 Ku yabi Ubangiji, ku ƙarfafa, ku manyan mala'iku, Ku da kuke biyayya da umarnansa, Kuna kasa kunne ga maganarsa!
21 Ku yabi Ubangiji, ku dukan ikokin da suke a Sama, Ku yabi Ubangiji, ku bayinsa masu aikata abin da yake so!
22 Ku yabi Ubangiji, dukanku da kuke halittattunsa, A duk inda yake mulki! Ka yabi Ubangiji, ya raina!
1 Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ya Ubangiji Allahna, mai girma ne kai! Kana saye da ɗaukaka da daraja,
2 Ka yi lulluɓi da haske. Ka shimfiɗa sammai kamar alfarwa.
3 Ka gina wurin zamanka a bisa kan ruwan da yake sama. Gajimare ne karusanka, A bisa kan fikafikan iska kake tafiya.
4 Iska ce jakadanka, Walƙiya kuwa ita ce baiwarka.
5 Ka sa duniya ta kahu sosai a bisa harsashin gininta, Ba kuwa za a iya kawar da ita ba har abada.
6 Ka sa teku a bisanta kamar alkyabba, Ruwan kuwa ya rufe manyan duwatsu.
7 Amma sa'ad da ka tsauta wa ruwa, Sai ya tsere, Sa'ad da ya ji ka daka tsawa, Sai ya sheƙa a guje.
8 Ya haura kan duwatsu, ya gangara cikin kwaruruka, Wurin da ka shirya masa.
9 Ka ƙayyade masa kan iyaka da ba zai taɓa ƙetarewa ba, Don kada ya sāke rufe duniya.
10 Ka sa maɓuɓɓugai suka gudano cikin kwaruruka, Ka sa ruwa yana gudu tsakanin tuddai.
11 Su ne suke shayar da namomin jeji, Jakunan jeji kuma, a nan sukan kashe ƙishinsu.
12 A itatuwan da suke kusa da wurin, Tsuntsaye suke yin sheƙunansu suna ta raira waƙa.
13 Daga sararin sama kakan aiko da ruwa bisa duwatsu, Ƙasa kuwa takan cika da albarkunka.
14 Kakan sa ciyawa ta yi girma don shanu, Tsire-tsire kuma don amfanin mutum, Saboda haka mutum zai iya shuka amfanin gona,
15 Don ya yi ruwan inabin da zai sa shi farin ciki, Ya sami man zaitun wanda zai sa shi fara'a, Da abincin da zai ba shi ƙarfi.
16 Itatuwan al'ul na Lebanon sukan sami isasshen ruwan sama, Itatuwa ne na Ubangiji kansa, waɗanda shi ya dasa.
17 A nan tsuntsaye suke yin sheƙunansu, A bisa itatuwan fir shamuwa suke yin sheƙa.
18 A kan duwatsu masu tsayi awakin jeji suke zama, Remaye sukan ɓuya a kan tsaunukan bakin teku.
19 Ka halicci wata don ƙididdigar lokatai, Rana kuwa ta san daidai lokacin fāɗuwarta.
20 Ka halicci dare, da duhu inda namomin jeji suke fitowa.
21 Sagarun zakoki sukan yi ruri sa'ad da suke farauta, Suna neman abincin da Allah zai ba su.
22 Sa'ad da rana ta fito, Sai su koma su kwanta a kogwanninsu.
23 Sa'an nan mutane sukan fita su yi aikinsu, Su yi ta aiki har maraice ya yi.
24 Ya Ubangiji, ka halicci abubuwa masu yawa! Da hikima ƙwarai ka halicce su! Duniya cike take da talikanka.
25 Ga babbar teku mai fāɗi, Inda talikai da ba su ƙidayuwa suke zaune, Manya da ƙanana gaba ɗaya.
26 Jiragen ruwa suna tafiya a kansa, Dodon ruwa wanda ka halitta, a ciki yake wasa.
27 Dukansu a gare ka suke dogara, Don ka ba su abinci sa'ad da suke bukata.
28 Ka ba su, sun ci, Ka tanada musu abinci, sun ƙoshi.
29 Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata, In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu, Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.
30 Amma sa'ad da ka hura musu numfashi, sai su rayu, Kakan sabunta fuskar duniya.
31 Da ma darajar Ubangiji ta dawwama har abada! Da ma Ubangiji ya yi farin ciki da abin da ya halitta!
32 Ya dubi duniya, sai ta girgiza, Ya taɓa duwatsu, sai suka tuɗaɗo da hayaƙi.
33 Zan raira waƙa ga Ubangiji dukan raina, Zan raira yabbai ga Allah muddin raina.
34 Da ma ya ji daɗin waƙata, Saboda yakan sa ni in yi murna.
35 Da ma a hallakar da masu zunubi daga duniya, Da ma mugaye su ƙare ƙaƙaf! Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ka yabi Ubangiji!
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!
2 Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi, Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!
3 Ku yi murna saboda mu nasa ne, Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!
4 Ku je wurin Ubangiji neman taimako, Ku tsaya a gabansa koyaushe.
5 Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu, Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki, Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.
6
7 Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu, Umarnansa domin dukan duniya ne.
8 Zai cika alkawarinsa har abada, Alkawaransa kuma don dubban zamanai,
9 Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim, Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.
10 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila, Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,
11 “Zan ba ka ƙasar Kan'ana, Za ta zama mallakarka.”
12 Jama'ar Ubangiji kima ne, Baƙi ne kuwa a ƙasar.
13 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa, Daga wannan mulki zuwa wancan,
14 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba, Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.
15 Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu, Kada ku cuci annabawana!”
16 Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu, Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,
17 Sai ya aika da Yusufu ya riga su zuwa, Shi wanda aka sayar da shi kamar bawa.
18 Ƙafafunsa suka yi rauni saboda an ɗaure su da sarƙa, Aka kuma sa wa wuyansa ƙuƙumi na baƙin ƙarfe,
19 Har kafin faɗar da ya yi, ta cika. Maganar Ubangiji ta tabbatar da gaskiyar abin da ya faɗa.
20 Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi, Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi.
21 Ya sa shi ya lura da mulkinsa, Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.
22 Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma'aikatan hukuma. Ya ba shi ikon umartar mashawartansa.
23 Sa'an nan Yakubu ya tafi Masar, Ya zauna a ƙasar.
24 Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa, Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.
25 Ya sa Masarawa suka ƙi jinin jama'arsa, Suka yi wa bayinsa munafunci.
26 Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa.
27 Suka aikata manya manyan ayyuka na Allah, Suka kuma yi ayyukan al'ajabi a Masar.
28 Ya aika da duhu a bisa ƙasar. Musa da Haruna ba su tayar wa umarnansa ba.
29 Ya mai da ruwan kogunansu su zama jini, Ya karkashe kifayensu duka.
30 Ƙasarsu ta cika da kwaɗi, Har a fādar sarki.
31 Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwari Suka cika dukan ƙasar.
32 Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsu Maimakon ruwan sama.
33 Ya lalatar da 'ya'yan inabinsu da itatuwan ɓaurensu, Ya kakkarya itatuwansu.
34 Ya ba da umarni, sai fāri suka zo, Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa.
35 Suka cinye dukan tsire-tsire na ƙasa. Suka cinye dukan amfanin gonaki.
36 Ya karkashe dukan 'ya'yan fari maza Na dukan iyalan Masarawa.
37 Sa'an nan ya bi da Isra'ilawa, suka fita, Suka kwashi azurfa da zinariya, Dukansu kuma ƙarfafa ne lafiyayyu.
38 Masarawa suka yi murna da fitarsu, Gama sun tsoratar da su.
39 Ya sa girgije ya yi wa jama'arsa inuwa, Da dare kuma wuta ta haskaka musu.
40 Suka roƙa, sai aka ba su makware, Ya ba su abinci daga sama da za su ci su ƙoshi.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya bulbulo, Yana gudu cikin hamada kamar kogi.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki Wanda ya yi wa bawansa Ibrahim.
43 Haka kuwa ya bi da jama'arsa, suka fita suna raira waƙa, Ya bi da zaɓaɓɓun jama'arsa, suna sowa ta farin ciki.
44 Ya ba su ƙasar baƙi, Ya sa su gāje gonakinsu,
45 Don jama'arsa su yi biyayya da dokokinsa, Su kuma kiyaye umarninsa. Ku yabi Ubangiji!
1 Ku yabi Ubangiji! Ku yi wa Ubangiji godiya, gama nagari ne shi, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
2 Wa zai iya faɗar dukan manya manyan ayyuka da ya yi? Wa zai iya yi masa isasshen yabo?
3 Masu farin ciki ne waɗanda suke biyayya da umarnansa, Waɗanda kullayaumi suke aikata abin da yake daidai!
4 Ka tuna da ni sa'ad da za ka taimaki jama'arka, ya Ubangiji! Ka sa ni cikinsu, sa'ad da za ka cece su.
5 Ka yardar mini in ga wadatar jama'arka, In yi tarayya da jama'arka da farin cikinsu, In yi farin ciki tare da waɗanda suke murna ta fāriya domin su naka ne.
6 Mun yi zunubi yadda kakanninmu suka yi, Mugaye ne, mun aikata mugunta.
7 Kakanninmu a Masar Ba su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba, Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu, Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya.
8 Amma duk da haka ya cece su, kamar yadda ya alkawarta, Domin ya nuna ikonsa mai girma.
9 Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe, Har ya bi da jama'arsa su haye Kamar a bisa busasshiyar ƙasa.
10 Ya cece su daga maƙiyansu, Ya ƙwato su daga wurin abokan gābansu.
11 Ruwa ya cinye maƙiyansu, Ba wanda ya tsira.
12 Sa'an nan jama'arsa suka gaskata alkawarinsa, Suka raira yabo gare shi.
13 Amma nan da nan, suka manta da abin da ya yi, Suka aikata, ba su jira shawararsa ba.
14 Suka cika da sha'awa cikin hamada, Suka jarraba Allah,
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, Amma ya aukar musu da muguwar cuta.
16 Can cikin hamada suka ji kishin Musa Da Haruna, bayin Ubangiji, tsarkaka,
17 Sai ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan, Ta binne Abiram da iyalinsa.
18 Wuta ta sauko bisa magoya bayansu, Ta ƙone mugayen mutanen nan.
19 Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb, Suka yi masa sujada.
20 Suka musaya ɗaukakar Allah Da siffar dabba mai cin ciyawa.
21 Suka manta da Allah wanda ya cece su, Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.
22 Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al'ajabi a can! Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya!
23 Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama'arsa, Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah, Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba.
24 Sai suka ƙi ƙasan nan mai ni'ima, Saboda ba su gaskata alkawarin Allah ba.
25 Suka zauna cikin alfarwansu suna ta gunaguni, Sun ƙi su saurari Ubangiji.
26 Saboda haka ya yi musu kakkausan kashedi, Cewa shi zai sa su duka su mutu a jejin,
27 Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna, Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa.
28 Sai jama'ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba'al sujada, a Feyor, Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli.
29 Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu, Mugawar cuta ta auka musu,
30 Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin, Aka kuwa kawar da annobar.
31 Tun daga lokacin nan ake ta tunawa da shi, Saboda abin da ya yi. Za a yi ta tunawa da shi a dukan zamanai masu zuwa.
32 Jama'ar Ubangiji suka sa ya yi fushi. A maɓuɓɓugan Meriba, Musa ya shiga uku saboda su.
33 Suka sa Musa ya husata ƙwarai, Har ya faɗi abubuwan da bai kamata ya faɗa ba.
34 Suka ƙi su kashe arna, Yadda Ubangiji ya umarta,
35 Amma suka yi aurayya da su, Suka kwaikwayi halayen arnan.
36 Jama'ar Allah suka yi wa gumaka sujada. Wannan kuwa ya jawo musu hallaka.
37 Suka miƙa 'ya'yansu mata da maza hadaya ga allolin arna.
38 Suka karkashe mutane marasa laifi, Wato 'ya'yansu mata da maza. Suka miƙa su hadaya ga gumakan Kan'ana, Suka ƙazantar da ƙasar saboda kashe-kashenkan da suke yi.
39 Ta wurin ayyukansu, suka ƙazantar da kansu, Suka zama marasa aminci ga Allah.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da jama'arsa, Ransa bai ji daɗinsu ba.
41 Sai ya bar su ƙarƙashin ikon arna, Abokan gābansu suka mallake su.
42 Abokan gābansu suka zalunce su, Suka tilasta su, su yi musu biyayya.
43 Sau da yawa Ubangiji yakan ceci jama'arsa, Amma sun fi so su yi masa tawaye, Suna ta nutsawa can cikin zunubi.
44 Duk da haka Ubangiji ya ji su sa'ad da suka yi kira gare shi, Ya kula da wahalarsu.
45 Saboda su ne ya tuna da alkawarinsa, Ya sāke ra'ayinsa saboda ƙaunarsa mai yawa.
46 Ubangiji ya sa waɗanda suka kama su Su ji tausayinsu.
47 Ka cece mu, ya Ubangiji Allahnmu, Ka komo da mu daga cikin sauran al'umma, Domin mu yabi sunanka mai tsarki, Mu kuma yi murna mu yi maka godiya.
48 Sai mu yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila, Mu yabe shi yanzu da har abada kuma! Dukan jama'a za su amsa su ce, “Amin! Amin!” Ku yabi Ubangiji!
1 Ku gode wa Ubangiji, gama shi nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce!
2 Ku zo mu yabi Ubangiji tare, Dukanku waɗanda ya fansa, Gama ya ƙwato ku daga maƙiyanku.
3 Ya komo da ku daga ƙasashen waje, Daga gabas da yamma, kudu da arewa.
4 Waɗansu suka yi ta kai da kawowa a hamada inda ba hanya, Sun kasa samun hanyar da za ta kai su garin da za su zauna a ciki.
5 Suka yi ta fama da yunwa, da ƙishirwa, Suka fid da zuciya ga kome.
6 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga wahalarsu.
7 Ya fisshe su, ya bi da su sosai, Zuwa birnin da za su zauna.
8 Dole ne su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu!
9 Ya shayar da waɗanda suke jin ƙishirwa, Ya kuma ƙosar da mayunwata da alheransa.
10 Waɗansu suna zaune cikin duhu da inuwar mutuwa, 'Yan sarƙa suna shan wahala da sarƙoƙi,
11 Saboda sun tayar, sun ƙi bin umarnan Allah Maɗaukaki, Sun kuwa ƙi koyarwarsa.
12 Suka gaji tiƙis saboda tsananin aiki, Za su faɗi ƙasa, ba mataimaki.
13 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga wahalarsu.
14 Ya fisshe su daga cikin duhu da inuwar mutuwa, Ya tsintsinka sarƙoƙinsu.
15 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.
16 Ya kakkarya ƙofofin da aka yi da tagulla. Ya kuma ragargaza ƙyamaren da aka yi da baƙin ƙarfe.
17 Waɗansu suka yi ciwo sabili da zunubansu, Suna ta shan wahala saboda muguntarsu.
18 Ba su so su ga abinci, Sun kusa mutuwa.
19 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga azabar da suke sha.
20 Da umarninsa ya warkar da su, Ya cece su daga kabari.
21 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.
22 Dole su gode masa, su miƙa masa hadayu, Su raira waƙoƙin murna, Su faɗi dukan abin da ya yi!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku da jirage, Suna samun abin zaman garinsu daga tekuna.
24 Suka ga abin da Ubangiji ya aikata, Ayyukansa masu banmamaki waɗanda ya yi a tekuna.
25 Ya ba da umarni, sai babbar iska ta tashi, Ta fara hurowa, ta sa raƙuman ruwa su tashi.
26 Aka ɗaga jiragen ruwa sama, Sa'an nan suka tsinduma cikin zurfafa. Da mutanen suka ga irin hatsarin da suke ciki, Sai zuciyarsu ta karai.
27 Suka yi ta tuntuɓe suna ta tangaɗi kamar bugaggu, Gwanintarsu duka ta zama ta banza.
28 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga azabarsu.
29 Ya sa hadiri ya yi tsit, Raƙuman ruwa kuma suka yi shiru.
30 Suka yi murna saboda wurin ya yi shiru, Ya kuma kai su kwatar jiragen ruwa lafiya, Wurin da suke so.
31 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.
32 Dole su yi shelar girmansa cikin taron jama'a, Su kuma yabe shi a gaban majalisar dattawa.
33 Ubangiji ya sa koguna suka ƙafe ƙaƙaf, Ya hana maɓuɓɓugai su gudana.
34 Ya mai da ƙasa mai dausayi ta zama mai gishiri, marar amfani, Saboda muguntar waɗanda suke zaune a can.
35 Ya sāke hamada ta zama tafkunan ruwa, Ya kuma mai da busasshiyar ƙasa ta zama maɓuɓɓugai masu gudana.
36 Ya bar mayunwata su zauna a can, Suka kuwa gina birni don su zauna a ciki.
37 Suka shuka gonaki suka dasa kurangar inabi, Waɗanda suka ba da amfani mai yawan gaske.
38 Ya sa wa jama'arsa albarka, Suka kuwa haifi 'ya'ya da yawa. Bai bar garkunan shanunsu su ragu ba.
39 Sa'ad da aka ci nasara a kan jama'ar Allah, Aka ƙasƙantar da su ta wurin mugun zalunci, Da wahalar da aka yi musu.
40 Sai Allah ya wulakanta waɗanda suka zalunci jama'arsa. Ya sa su suka yi ta kai da kawowa A hamada inda ba hanya.
41 Ya tsamo masu bukata daga cikin baƙin cikinsu, Ya sa iyalansu su riɓaɓɓanya kamar garkunan tumaki.
42 Da adalai suka ga wannan, sai suka yi murna, Mugaye kuwa aka rufe bakinsu.
43 Da ma a ce masu hikima Za su yi tunani a kan waɗannan abubuwa, Da ma kuma su yarda Da madawwamiyar ƙaunar Ubangiji.
1 A shirye nake, ya Allah, Na shirya sosai! Zan raira waƙa in yabe ka! Ka farka, ya raina!
2 Ku farka, ya molona da garayata! Zan farkar da rana!
3 Zan yi maka godiya a tsakiyar sauran al'umma, ya Ubangiji! Zan yabe ka a tsakiyar kabilai!
4 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har can saman sammai, Amincinka kuma ya kai sararin sammai.
5 Ya Allah, ka bayyana girmanka a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!
6 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu'ata, Domin jama'ar da kake ƙauna ta sami cetonka.
7 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce, “Da nasara zan raba Shekem, Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama'ata.
8 Gileyad tawa ce, har da Manassa ma, Ifraimu ne kwalkwalina, Yahuza kuma sandana ne na sarauta.
9 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki, Edom kuwa kamar akwatin takalmina. Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.”
10 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara? Wa zai kai ni Edom?
11 Da gaske ka yashe mu ke nan? Ba za ka yi tafiya Tare da sojojinmu ba?
12 Ka taimake mu, mu yaƙi abokin gāba, Domin taimako irin na mutum banza ne!
13 Idan Allah yana wajenmu, Za mu yi nasara, Zai kori abokan gābanmu.
1 Ina yabonka, ya Allah, kada ka yi shiru!
2 Mugaye da maƙaryata sun tasar mini, Suna ta faɗar ƙarairayi a kaina.
3 Suna faɗar mugayen abubuwa a kaina. Suna tasar mini ba dalili.
4 Suna ƙina ko da yake ina ƙaunarsu, Har ina yi musu addu'a.
5 Sukan sāka mini alheri da mugunta, Sukan sāka mini ƙauna da ƙiyayya.
6 Ka zaɓi lalataccen mutum ya shara'anta maƙiyina, Ka sa ɗaya daga cikin maƙiyansa Ya gabatar da ƙararsa.
7 Ka sa a same shi da laifi a shari'ar da ake yi masa, Ka sa har addu'ar da yake yi Ta zama babban laifi!
8 Ka aukar masa da ajalinsa nan da nan, Ka sa wani ya ɗauki matsayinsa!
9 Ka sa 'ya'yansa su zama marayu, Matarsa kuwa ta zama gwauruwa!
10 Ka sa 'ya'yansa su rasa gidan zama, su riƙa yawon bara. Ka sa a kore su daga kufan da suke zaune!
11 Ka sa waɗanda suke binsa bashi su kwashe Dukan abin da yake da shi. Ka sa baƙi su kwashe dukan abin da ya sha wahalar nema.
12 Ka sa kada kowa ya yi masa alheri sam, Kada ka bar kowa ya lura da marayunsa.
13 Ka sa dukan zuriyarsa su mutu, Har a manta da sunansa a tsara mai zuwa.
14 Sai ka tuna, ya Ubangiji, da muguntar kakanninsa, Kada ka manta da zunuban mahaifiyarsa.
15 Ka tuna da zunubansu kullayaumin, ya Ubangiji, Amma su kansu a manta da su ɗungum!
16 Gama mutumin nan bai taɓa tunanin yin alheri ba, Yakan tsananta wa talakawa, da matalauta, da kasassu, har ya kashe su.
17 Yana jin daɗin la'antarwa, ka sa a la'anta shi! Ba ya son sa albarka, ka sa kada kowa ya sa masa albarka!
18 Yakan la'antar a sawwaƙe kamar yadda yake sa tufafinsa. Ka sa la'antarwa da yake yi Su jiƙa shi kamar ruwa, Su shiga har ƙasusuwansa kamar mai,
19 Su lulluɓe shi kamar tufa, Su kuma kewaye shi kamar ɗamara.
20 Ya Ubangiji, ka sa haka, Wato ya zama yadda za a hukunta wa maƙiyana ke nan, Waɗanda suke faɗar mugayen abubuwa a kaina!
21 Amma ya Ubangiji, Allahna, ka taimake ni, Yadda ka alkawarta, Ka cece ni sabili da alherin ƙaunarka.
22 Ni talaka ne, matalauci, Na ji zafi ƙwarai a can zuciyata.
23 Na kusa ɓacewa kamar inuwar maraice, An hurar da ni can kamar ƙwaro.
24 Gwiwoyina sun yi suwu saboda rashin abinci, Jikina kuma ya rame, ba shi da ƙarfi.
25 Sa'ad da mutane suka gan ni sun yi mini ba'a, Suna kaɗa kai saboda raini.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna, Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka!
27 Ka sa maƙiyana su sani, Kai ne Mai Cetona.
28 Watakila su la'anta ni, Amma kai za ka sa mini albarka, Ka sa a kori waɗanda suke tsananta mini. Da ma ka sa ni da nake bawanka, in yi murna.
29 Ka sa kunya ta rufe maƙiyana, Ka sa su sa kunyarsu kamar riga.
30 Da murya mai ƙarfi zan yi wa Ubangiji godiya. Zan yabe shi a taron jama'a,
31 Saboda yakan kāre talaka, Domin ya cece shi daga waɗanda Suka sa masa laifin mutuwa.
1 Ubangiji ya ce wa Mai Girma, Sarkina, “Zauna nan a damana, Har in sa maƙiyanka a ƙarƙashin sawayenka.”
2 Tun daga Sihiyona Ubangiji zai faɗaɗa sarautarka, ya ce, “Ka yi mulki bisa maƙiyanka.”
3 A ranar da za ka yi yaƙi da maƙiyanka, Jama'arka za su kawo maka gudunmawa don kansu. Kamar yadda raɓa take da sassafe, Haka samarinka za su zo wurinka a tsarkakan tsaunuka.
4 Ubangiji ya yi muhimmin alkawari, Ba kuwa zai fasa ba! “Za ka zama firist har abada Bisa ga tsabi'ar Malkisadik firist.”
5 Ubangiji yana damanka, Zai kori sarakuna a ranar da ya husata.
6 Zai shara'anta wa dukan sauran al'umma, Ya rufe fagen fama da gawawwaki, Zai kori sarakunan duk duniya.
7 Sarkin zai sha ruwan rafin da yake kan hanya, Ya wartsake ya sami ƙarfi. Zai yi tsayawar nasara.
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Zan yi wa Ubangiji godiya da zuciya ɗaya, A cikin taron jama'arsa.
2 Abubuwan banmamaki ne Ubangiji yake aikatawa! Duk waɗanda suke murna da su Suna so su fahimce su.
3 Dukan abin da yake yi, Cike yake da girma da ɗaukaka, Adalcinsa har abada ne.
4 Ubangiji ba zai bar mu mu manta da ayyukansa masu banmamaki ba, Shi mai alheri ne, mai jinƙai kuma.
5 Yakan tanada wa masu tsoronsa abinci, Bai taɓa mantawa da alkawarinsa ba.
6 Ya nuna ikonsa ga jama'arsa Saboda ya ba su ƙasashen baƙi.
7 Iyakar abin da yake yi duka, da aminci da adalci ne. Dukan umarnansa, abin dogara ne.
8 Sukan tabbata har abada, Da gaskiya da adalci aka ba da su.
9 Ya kawo wa jama'arsa ceto, Ya kuma yi musu madawwamin alkawari. Mai Tsarki ne shi, Maɗaukaki!
10 Hanyar samun hikima, ita ce tsoron Ubangiji, Yakan ba da kyakkyawar ganewa Ga dukan waɗanda suke bin umarnansa, Sai ku yabe shi har abada!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Mai farin ciki ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, Mai farin ciki ne shi wanda yake jin daɗin yin biyayya da umarnansa.
2 'Ya'yansa za su zama manyan ƙasar, Zuriyar mutumin kirki za ta yi albarka.
3 Iyalinsa za su zama attajirai masu dukiya, Adalcinsa zai tabbata har abada.
4 Haske yakan haskaka wa mutanen kirki a cikin duhu, Da waɗanda suke yin alheri, da jinƙai, da gaskiya.
5 Mai farin ciki ne mutumin da yakan ba da rance hannu sake, Wato wanda yake yin harkarsa da gaskiya.
6 Mutumin kirki ba zai kāsa ba daɗai, Ba za a taɓa mantawa da shi ba.
7 Ba ya tsoron jin mugun labari, Bangaskiyarsa tana da ƙarfi, Ga Ubangiji yake dogara.
8 Ba shi da damuwa ko tsoro, Ya tabbata zai ga faɗuwar maƙiyansa.
9 Yakan bayar ga matalauta hannu sake, Alherinsa kuwa dawwamamme ne. Zai zama mai iko wanda ake girmamawa.
10 Sa'ad da mugaye suka ga wannan, Sai suka tunzura, suka harare shi da fushi, suka ɓace, Sa zuciyarsu ta ƙare har abada.
1 Yabo Ya tabbata ga Ubangiji! Ku bayin Ubangiji, Ku yabi sunansa!
2 Za a yabi sunansa yanzu da har abada!
3 Daga gabas zuwa yamma a yabi sunan Ubangiji!
4 Ubangiji yake mulkin dukan sauran al'umma, Ɗaukakarsa tana bisa kan sammai.
5 Ba wani kamar Ubangiji Allahnmu. Yana zaune a can ƙwanƙolin sama,
6 Amma ya duba ƙasa, Ya dubi sammai da duniya.
7 Yakan ɗaga talakawa daga ƙura, Yakan ɗaga matalauta daga cikin azabarsu.
8 Yakan sa su zama abokan sarakuna, Sarakunan jama'arsa.
9 Yakan girmama matar da ba ta haihuwa a gidanta, Yakan sa ta yi farin ciki ta wurin ba ta 'ya'ya. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Sa'ad da jama'ar Isra'ila suka bar Masar, Sa'ad da zuriyar Yakubu suka bar baƙuwar ƙasar nan,
2 Yahuza ya zama tsattsarkar jama'ar Ubangiji, Isra'ila ya zama abin mallakarsa.
3 Bahar Maliya da ya duba, sai ya gudu, Kogin Urdun ya daina gudu.
4 Duwatsu suka yi ta tsalle kamar awaki, Tuddai kuwa suka yi ta tsalle suna kewayawa kamar tumaki.
5 Me ya faru ne, ya teku, da ya sa ki gudu? Kai fa Urdun, me ya sa ka daina gudu?
6 Ku fa duwatsu, me ya sa kuka yi ta tsalle kamar awaki? Tuddai, me ya sa kuka yi ta tsalle, Kuna kewayawa kamar tumaki?
7 Ki yi rawar jiki, ya ke duniya, Saboda zuwan Ubangiji, A gaban Allah na Yakubu,
8 Wanda ya sa duwatsu su zama tafkunan ruwa, Ya kuma sa kogwannin duwatsu su zama maɓuɓɓugai, Masu bulbulo da ruwa.
1 A gare ka kaɗai, ya Ubangiji, A gare ka kaɗai, ba a gare mu ba, Dole a girmama ka, Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka.
2 Me ya sa sauran al'umma suke tambayarmu, “Ina Allahnku?”
3 Allahnmu yana Sama, Yana aikata yadda yake so.
4 Amma nasu alloli na azurfa da zinariya ne, Da hannu aka siffata su.
5 Suna da baki, amma ba sa magana, Suna da idanu, amma ba sa gani.
6 Suna da kunnuwa, amma ba sa ji, Suna da hanci, amma ba sa jin ƙanshi.
7 Suna da hannuwa, amma ba sa iya riƙon kome, Suna da ƙafafu, amma ba sa iya tafiya. Ba su da murya sam.
8 Ka sa waɗanda suka yi su, Da dukan masu dogara gare su, Su zama kamar gumakan da suka yi!
9 Ku dogara ga Ubangiji, ya ku jama'ar Isra'ila! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.
10 Ku dogara ga Ubangiji, ya ku firistoci na Allah! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.
11 Ku dogara ga Ubangiji, dukanku waɗanda kuke tsoronsa! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.
12 Ubangiji yana tuna da mu, zai kuwa sa mana albarka, Zai sa wa jama'ar Isra'ila albarka, Da dukan firistoci na Allah.
13 Zai sa wa dukan waɗanda suke tsoronsa albarka. Babba da yaro.
14 Ubangiji ya ba ku 'ya'ya, Ku da zuriyarku.
15 Ubangiji, wanda ya yi sama da ƙasa Ya sa muku albarka!
16 Samaniya ta Ubangiji ce kaɗai, Amma ya ba mutane duniya.
17 Matacce ba ya yabon Ubangiji, Ko wanda ya gangara zuwa cikin kabari.
18 Amma mu da muke rayayyu, za mu yi masa godiya. A yanzu da har abada. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Ina ƙaunar Ubangiji, saboda yana jina, Yana kasa kunne ga addu'o'ina.
2 Yakan kasa kunne gare ni, A duk lokacin da na yi kira gare shi.
3 Mutuwa ta ɗaure ni da igiyarta tam, Razanar kabari ta auka mini, Na cika da tsoro da alhini.
4 Sa'an nan sai na yi kira ga Ubangiji, na ce, “Ina roƙonka, ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 Ubangiji mai jinƙai ne, mai alheri, Allahnmu mai rahama ne.
6 Ubangiji yakan kiyaye kāsassu, Sa'ad da na shiga hatsari ya cece ni.
7 Kada ki yi shakka, ya zuciyata, Gama Ubangiji yana yi mini alheri.
8 Ubangiji ya cece ni daga mutuwa, Ya share hawayena, Bai bari a kāshe ni ba.
9 Don haka nake tafiya a gaban Ubangiji A duniyar masu rai.
10 Na dai yi ta gaskatawa, ko da yake Na ce, “An ragargaza ni sarai.”
11 Sa'ad da na ji tsoro na ce, “Ba wanda za a iya dogara gare shi.”
12 Me zan bayar ga Ubangiji Saboda dukan alheransa gare ni?
13 Zan miƙa hadaya ta sha ga Ubangiji, Ina gode masa domin dā ya cece ni.
14 Zan ba shi abin da na alkawarta A taron dukan jama'arsa.
15 Mutuwar ɗaya daga cikin tsarkakansa, Abu mai daraja ne!
16 Ni bawanka ne, ya Ubangiji, Ina bauta maka yadda mahaifiyata ta yi, Ka 'yantar da ni.
17 Zan miƙa maka hadaya ta godiya, Zan yi addu'ata a gare ka.
18 A taron dukan jama'arka, A shirayun Haikalinka, A Urushalima, zan ba ka abin da na alkawarta. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Ku yabi Ubangiji, ku dukan sauran al'ummai! Ku yabe shi, ku dukan kabilai!
2 Madawwamiyar ƙaunarsa, da ƙarfi take, Amincinsa kuma tabbatacce ne har abada. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Ku gode wa Ubangiji, Domin shi mai alheri ne, Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.
2 Bari jama'ar Isra'ila su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”
3 Bari dukan firistoci na Allah su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”
4 Bari dukan waɗanda suke tsoronsa su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”
5 A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji Ya kuwa amsa mini, ya kuɓutar da ni.
6 Ubangiji yana tare da ni, ba zan ji tsoro ba. Me mutane za su iya yi mini?
7 Ubangiji ne yake taimakona, Zan kuwa ga fāɗuwar maƙiyana da idona.
8 Gwamma a dogara ga Ubangiji, Da a dogara ga mutane.
9 Gwamma a dogara ga Ubangiji, Da a dogara ga shugabanni na mutane kawai.
10 Ma ƙiya da yawa sun kewaye ni, Amma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji!
11 Suka kewaye ni a kowane gefe Amma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji!
12 Suka rufe ni kamar ƙudan zuma, Amma suka ƙone nan da nan kamar wutar jeji, Ta wurin ikon Ubangiji na hallaka su!
13 Aka auko mini da tsanani, Har aka kore ni, Amma Ubangiji ya taimake ni.
14 Ubangiji yakan ba ni iko, ya ƙarfafa ni, Shi ne Mai Cetona!
15 Ku kasa kunne ga sowar murna ta nasara A cikin alfarwan jama'ar Allah. “Ikon Ubangiji mai girma ne ya aikata wannan!
16 Ikonsa ne ya kawo mana nasara, Babban ikonsa a wurin yaƙi!”
17 Ba zan mutu ba, amma rayuwa zan yi, Don in ba da labarin abin da Ubangiji ya yi.
18 Ya hukunta ni da hukunci mai tsanani, Amma bai kashe ni ba.
19 A buɗe mini ƙofofin Haikali, Zan shiga ciki in yabi Ubangiji!
20 Wannan ƙofar Ubangiji ce, Sai adalai kaɗai suke shiga ciki!
21 Ina yabonka, ya Ubangiji, domin ka ji ni, Domin ka ba ni nasara!
22 Dutsen da magina suka ƙi, wai ba shi da amfani, Sai ya zama shi ya fi duka amfani.
23 Ubangiji ne ya yi haka, Wannan kuwa abin banmamaki ne!
24 Wace irin rana ce haka da Ubangiji ya ba mu! Bari mu yi farin ciki, mu yi biki!
25 Ka cece mu, ya Ubangiji, ka cece mu! Ka ba mu nasara, ya Ubangiji!
26 Allah yakan sa wa wanda ya zo da sunan Ubangiji albarka! Daga Haikalin Ubangiji muke yabonka!
27 Ubangiji shi ne Allah, yana yi mana alheri, Ku ɗauki hadayunku ku yi ta idi, Ku ɗaura su a zankayen bagade.
28 Kai ne Allahna, kai nake yi wa godiya, Zan yi shelar girmanka.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne, Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.
1 Masu farin ciki ne, marasa laifi cikin zamansu, Waɗanda suke zamansu bisa ga dokar Ubangiji.
2 Masu farin ciki ne waɗanda suke bin umarnansa, Waɗanda suke yi masa biyayya da zuciya ɗaya.
3 Hakika ba su yin laifi, Sukan yi tafiya a hanyoyin Ubangiji.
4 Kai ka ba mu dokokinka, Ka kuwa faɗa mana mu kiyaye su da aminci.
5 Na sa zuciya zan yi aminci, Game da kiyaye dokokinka!
6 Idan na kula da dukan umarnanka, To, ba zan kasa kaiwa ga burina ba.
7 Zan yabe ka da tsattsarkar zuciya, A sa'ad da na fahimci ka'idodinka masu adalci.
8 Zan yi biyayya da dokokinka, Ko kusa kada ka kashe ni!
9 Ƙaƙa saurayi zai kiyaye ransa da tsarki? Sai ta wurin biyayya da umarnanka.
10 Da zuciya ɗaya nake ƙoƙarin bauta maka, Ka kiyaye ni daga rashin biyayya da umarnanka!
11 Na riƙe maganarka a zuciyata, Don kada in yi maka zunubi.
12 Ina yabonka, Ya Ubangiji, Ka koya mini ka'idodinka!
13 Zan ta da murya, In maimaita dukan dokokin da ka bayar.
14 Ina murna da bin umarnanka, Fiye da samun dukiya mai yawa.
15 Nakan yi nazarin umarnanka, Nakan kuma yi bimbinin koyarwarka.
16 Ina murna da dokokinka, Ba zan manta da umarnanka ba.
17 Ka yi mini alheri, ni bawanka, Domin in rayu in yi biyayya da koyarwarka.
18 Ka buɗe idona Domin in ga gaskiyar shari'arka mai banmamaki.
19 Zamana a nan duniya na ɗan lokaci kaɗan ne. Kada ka ɓoye mini umarnanka!
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari, A kowane lokaci ina so in san hukuntanka.
21 Kakan tsauta wa masu girmankai, La'anannu ne waɗanda suka ƙi bin umarnanka.
22 Ka kuɓutar da ni daga cin mutuncinsu da raininsu, Domin na kiyaye dokokinka.
23 Ko da sarakuna za su taru Su shirya mini maƙarƙashiya, Duka da haka, ni bawanka, Zan yi nazarin ka'idodinka.
24 Umarnanka suna faranta mini rai, Su ne mashawartana.
25 Ina kwance cikin ƙura, an yi nasara da ni, Ka wartsakar da ni kamar yadda ka alkawarta!
26 Na hurta dukan abin da na aikata, ka kuwa amsa mini, Ka koya mini ka'idodinka!
27 Ka koya mini yadda zan yi biyayya da dokokinka, In kuma yi nazarin koyarwarka mai banmamaki.
28 Ɓacin rai ya ci ƙarfina, Ka ƙarfafa ni, kamar yadda ka alkawarta.
29 Ka kiyaye ni daga bin muguwar hanya, Ta wurin alherinka, ka koya mini dokarka.
30 Na yi niyya in yi biyayya, Na mai da hankali ga ka'idodinka.
31 Na bi umarnanka, ya Ubangiji, Kada ka sa in kasa ci wa burina!
32 Ina ɗokin yin biyayya da umarnanka, Gama za ka ƙara mini fahimi.
33 Ka koya mini ma'anar dokokinka, ya Ubangiji, Zan kuwa yi biyayya da su a kowane lokaci.
34 Ka fassara mini dokarka, ni kuwa zan yi biyayya da ita, Zan kiyaye ta da zuciya ɗaya.
35 Ka bishe ni a hanyar umarnanka, Domin a cikinsu nakan sami farin ciki
36 Ka sa ni in so yin biyayya da ka'idodinka, Fiye da samun dukiya.
37 Ka kiyaye ni daga mai da hankali ga abin da yake marar amfani, Ka yi mini alheri kamar yadda ka alkawarta.
38 Ka tabbatar da alkawarin da ka yi mini, ni bawanka, Irin wanda kakan yi wa waɗanda suke tsoronka.
39 Ka kiyaye ni daga cin mutuncin da nake tsoro, Ka'idodinka suna da amfani ƙwarai!
40 Ina so in yi biyayya da umarnanka, Gama kai mai adalci ne, Ka yi mini alheri!
41 Ka nuna mini yawan ƙaunar da kake yi mini, ya Ubangiji, Ka cece ni bisa ga alkawarinka.
42 Sa'an nan zan amsa wa waɗanda suke cin mutuncina, Domin na dogara ga maganarka.
43 Ka ba ni iko in iyar da saƙonka na gaskiya a kowane lokaci, Gama sa zuciyata tana ga hukuntanka.
44 Kullum zan yi biyayya da dokarka har abada abadin!
45 Zan rayu da cikakken 'yanci, Gama na yi ƙoƙari in kiyaye ka'idodinka.
46 Zan hurta umarnanka ga sarakuna, Ba kuwa zan ji kunya ba.
47 Ina murna in yi biyayya da umarnanka, Saboda in ƙaunarsu.
48 Ina girmama umarnanka, ina kuwa ƙaunarsu, Zan yi ta tunani a kan koyarwarka.
49 Ka tuna da alkawarin da ka yi mini, ni bawanka, Ka ƙarfafa zuciyata.
50 Ko ina shan wahala, ana ta'azantar da ni, Saboda alkawarinka yana rayar da ni.
51 Masu girmankai suna raina ni, Amma ban rabu da dokarka ba.
52 Na tuna da koyarwar da ka yi mini a dā, Sukan kuwa ta'azantar da ni, ya Ubangiji.
53 Haushi ya kama ni sosai, Sa'ad da na ga mugaye suna keta dokarka.
54 Ina zaune can nesa da gidana na ainihi, Sai na ƙago waƙoƙi a kan umarnanka.
55 Da dare nakan tuna da kai, ya Ubangiji, Ina kuwa kiyaye dokarka.
56 Wannan shi ne farin cikina, In yi biyayya da umarnanka.
57 Kai kaɗai nake so, ya Ubangiji, Na yi alkawari in yi biyayya da dokokinka.
58 Ina roƙonka da zuciya ɗaya, Ka yi mini jinƙai kamar yadda ka alkawarta!
59 Na yi tunani a kan ayyukana, Na yi alkawari in bi ka'idodinka.
60 Ba tare da ɓata lokaci ba, Zan gaggauta in kiyaye umarnanka.
61 Mugaye sun ɗaure ni tam da igiyoyi, Amma ba zan manta da dokarka ba.
62 Da tsakar dare nakan farka, In yabe ka saboda hukuntanka masu adalci.
63 Ina abuta da duk waɗanda suke bauta maka, Da duk waɗanda suke kiyaye dokokinka.
64 Ya Ubangiji, duniya ta cika da madawwamiyar ƙaunarka, Ka koya mini umarnanka!
65 Kana cika alkawarinka, ya Ubangiji, Kana kuwa yi mini alheri, ni bawanka.
66 Ka ba ni hikima da ilimi Domin ina dogara ga umarnanka.
67 Kafin ka hore ni nakan yi kuskure, Amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Managarci ne kai, mai alheri ne kuma, Ka koya mini umarnanka!
69 Masu girmankai sun faɗi ƙarairayi a kaina, Amma da zuciya ɗaya nake biyayya da ka'idodinka.
70 Waɗannan mutane ba su da ganewa, Amma ni ina murna da dokarka.
71 Horon da aka yi mini ya yi kyau, Domin ya sa na koyi umarnanka.
72 Dokar da ka yi Muhimmiya ce a gare ni, Fiye da dukan dukiyar duniya.
73 Kai ne ka halicce ni, ka kuma kiyaye ni lafiya, Ka ba ni ganewa, don in koyi dokokinka.
74 Waɗanda suke tsoronka za su yi murna sa'ad da suka gan ni, Saboda ina dogara ga alkawarinka.
75 Na sani ka'idodinka na adalci ne, ya Ubangiji, Ka hore ni, domin kai mai aminci ne.
76 Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta ta'azantar da ni, Kamar yadda ka alkawarta mini, ni bawanka.
77 Ka yi mini jinƙai, zan rayu, Saboda ina murna da dokarka.
78 Ka kunyatar da masu girmankai Saboda sun ba da shaidar zur a kaina, Amma ni, zan yi tunani a kan ka'idodinka.
79 Ka sa waɗanda suke tsoronka su zo gare ni, Da waɗanda suka san umarnanka.
80 Ka sa in yi cikakkiyar biyayya da umarnanka, Sa'an nan zan tsere wa shan kunyar faɗuwa.
81 Na tafke, ya Ubangiji, jira nake ka cece ni, Na dogara ga maganarka.
82 Idanuna sun gaji da zuba ido ga alkawarinka. Roƙo nake, “Sai yaushe za ka taimake ni?”
83 Na zama marar amfani kamar salkar ruwan inabi wanda aka jefar da ita, Duk da haka ban manta da umarnanka ba.
84 Har yaushe zan yi ta jira? Yaushe za ka yi wa waɗanda suke tsananta mini hukunci?
85 Masu girmankai, waɗanda ba su biyayya da dokarka, Sun haƙa wushefe don su kama ni.
86 Umarnanka duka, abin dogara ne, Mutane suna tsananta mini da ƙarairayi, Ka taimake ni!
87 Sun kusa ci wa burinsu na su kashe ni, Amma ban raina ka'idodinka ba.
88 Saboda madawwamiyar ƙaunarka, ka yi mini alheri, Domin in yi biyayya da dokokinka.
89 Maganarka tabbatacciya ce, ya Ubangiji, A kafe take a Sama.
90 Amincinka ya tabbata har abada, Ka kafa duniya a inda take, tana nan kuwa a wurin.
91 Dukan abubuwa suna nan har wa yau saboda umarninka, Domin su duka bayinka ne.
92 Da ba domin dokarka ita ce sanadin farin cikina ba, Da na mutu saboda hukuncin da na sha.
93 Faufau ba zan raina ka'idodinka ba, Gama saboda su ka bar ni da rai.
94 Ni naka ne, ka cece ni! Na yi ƙoƙari in yi biyayya da umarnanka.
95 Mugaye suna jira su kashe ni, Amma zan yi ta tunani a kan dokokinka.
96 Na koya cewa ba wani abu da yake cikakke, Amma umarninka ba shi da iyaka.
97 Ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina ta tunani a kanta dukan yini.
98 Umarninka yana tare da ni a kowane lokaci, Ya sa ni in yi hikima fiye da dukan maƙiyana.
99 Ganewata ta fi ta dukan malamaina, Saboda ina ta tunani a kan koyarwarka.
100 Na fi tsofaffi hikima, Saboda ina biyayya da umarnanka.
101 Nakan guje wa halin mugunta Saboda ina so in yi biyayya da maganarka.
102 Ban raina koyarwarka ba Saboda kai ne ka koya mini.
103 Ɗanɗanon ka'idodinka akwai zaƙi, Har sun fi zuma zaƙi!
104 Na ƙaru da hikima daga dokokinka, Saboda haka ina ƙin dukan halin da yake ba daidai ba.
105 Maganarka fitila ce wadda za ta bi da ni, Haske ne kuma a kan hanyata.
106 Zan cika muhimmin alkawarina, In yi biyayya da koyarwarka mai adalci.
107 Azabaina, ya Ubangiji, suna da yawa, Ka rayar da ni kamar yadda ka alkawarta!
108 Ka karɓi addu'ata ta godiya, ya Ubangiji, Ka koya mini umarnanka.
109 Kullum a shirye nake in kasai da raina, Ban manta da umarninka ba.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, Amma ban yi rashin biyayya da umarnanka ba.
111 Umarnanka nawa ne har abada, Su ne murnar zuciyata.
112 Na ƙudura zan yi biyayya da ka'idodinka, Har ranar mutuwata.
113 Ina ƙin waɗanda ba su yi maka aminci, Amma ina ƙaunar dokarka.
114 Kai ne kake kāre ni, kake kuma kiyaye ni, Ina sa zuciya ga alkawarinka.
115 Ku rabu da ni, ku masu zunubi! Zan yi biyayya da umarnan Allahna.
116 Ka ƙarfafa ni kamar yadda ka alkawarta, zan kuwa rayu, Kada ka bar ni in kasa ci wa burina!
117 Ka riƙe ni, sai in zauna lafiya, Koyaushe zan mai da hankali ga umarnanka.
118 Ka rabu da dukan waɗanda ba su biyayya da dokokinka, Dabarunsu na yaudara banza ne.
119 Kakan yi banza da duk mai mugunta, Don haka ina ƙaunar koyarwarka.
120 Saboda kai, nake jin tsoro, Na cika da tsoro saboda shari'unka.
121 Na yi abin da yake daidai mai kyau, Kada ka bar ni a hannun maƙiyana!
122 Sai ka yi alkawari za ka taimaki bawanka, Kada ka bar masu girmankai su wahalshe ni!
123 Idanuna sun gaji da duban hanyar cetonka, Ceton da ka alkawarta.
124 Ka bi da ni bisa ga tabbatacciyar ƙaunarka, Ka koya mini umarnanka.
125 Ni bawanka ne, don haka ka ba ni ganewa, Don in san koyarwarka.
126 Ya Ubangiji, lokaci ya yi da za ka yi wani abu, Saboda mutane sun ƙi yin biyayya da dokarka!
127 Ina ƙaunar umarnanka, fiye da zinariya, Fiye da zinariya tsantsa.
128 Saboda haka ina bin dukan koyarwarka, Ina kuwa ƙin dukan mugayen al'amura.
129 Koyarwarka tana da ban al'ajabi, Da zuciya ɗaya nake biyayya da su.
130 Fassarar koyarwarka takan ba da haske, Takan ba da hikima ga wanda bai ƙware ba.
131 Ina haki da baki a buɗe, Saboda marmarin da nake yi wa umarnanka.
132 Ka juyo wurina ka yi mini jinƙai, Kamar yadda kakan yi wa masu ƙaunarka.
133 Kada ka bar ni in fāɗi kamar yadda ka alkawarta, Kada ka bar mugunta ta rinjaye ni.
134 Ka cece ni daga waɗanda suke zaluntata, Domin in yi biyayya da umarnanka.
135 Ka sa mini albarka da kasancewarka tare da ni, Ka koya mini dokokinka.
136 Hawayena suna malalowa kamar kogi, Saboda jama'a ba su biyayya da shari'arka ba.
137 Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, Dokokinka kuma daidai ne,
138 Ka'idodin da ka bayar kuwa dukansu masu kyau ne, Daidai ne kuwa.
139 Fushi yana cina kamar wuta, Saboda maƙiyana ba su kula da umarnanka ba.
140 Alkawarinka ba ya tashi! Bawanka yana ƙaunar alkawarinka ƙwarai!
141 Ni ba kome ba ne, rainanne ne, Amma ban ƙi kula da ka'idodinka ba.
142 Adalcinka zai tabbata har abada, Dokarka gaskiya ce koyaushe.
143 A cike nake da wahala da damuwa, Amma umarnanka suna faranta zuciyata.
144 Koyarwarka masu adalci ne har abada, Ka ba ni ganewa domin in rayu.
145 Ina kira gare ka da zuciya ɗaya, Ka amsa mini, ya Ubangiji, Zan yi biyayya da umarnanka!
146 Ina kira gare ka, Ka cece ni, zan bi ka'idodinka!
147 Tun kafin fitowar rana ina kira gare ka neman taimako, Na sa zuciya ga alkawarinka.
148 Dare farai ban yi barci ba, Ina ta bimbini a kan koyarwarka.
149 Ka ji ni, ya Ubangiji, bisa ga madawwamiyar ƙaunarka, Ka kiyaye raina bisa ga alherinka!
150 Mugayen nan waɗanda suke tsananta mini sun matso kusa, Mutanen da ba su taɓa kiyaye dokarka ba.
151 Amma kana kusa da ni, ya Ubangiji, Dukan alkawaranka gaskiya ne.
152 Tuntuni na ji labarin koyarwarka, Ka sa su tabbata har abada.
153 Ka dubi wahalata, ka cece ni, Gama ban ƙi kulawa da dokarka ba.
154 Ka kāre manufata, ka kuɓutar da ni, Ka cece ni kamar yadda ka alkawarta!
155 Ba za a ceci mugaye ba, Saboda ba su yi biyayya da dokokinka ba.
156 Amma juyayinka yana da girma, ya Ubangiji, Saboda haka ka cece ni yadda ka yi niyya.
157 Maƙiyana da masu zaluntata, suna da yawa, Amma ban fasa yin biyayya da dokokinka ba.
158 Sa'ad da na dubi waɗannan maciya amana, Sai in ji ƙyama ƙwarai, Domin ba su yi biyayya da umarninka ba.
159 Ka dubi yadda nake ƙaunar koyarwarka, ya Ubangiji! Ka cece ni bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
160 Cibiyar dokarka gaskiya ce, Dukan ka'idodinka na adalci tabbatattu ne.
161 Ƙarfafan mutane sun auka mini ba dalili, Amma maganarka ce nake girmamawa.
162 In farin ciki ƙwarai saboda alkawaranka, Farin cikina kamar na wanda ya sami dukiya mai yawa ne.
163 Ina ƙin ƙarairayi, ba na jin daɗinsu, Amma ina ƙaunar dokarka.
164 A kowace rana nakan gode maka sau bakwai, Saboda shari'unka masu adalci ne.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka sun sami cikakken zaman lafiya, Ba wani abin da zai sa su fāɗi.
166 Ina jiranka ka cece ni, ya Ubangiji, Ina aikata abin da ka umarta.
167 Ina biyayya da ka'idodinka, Ina ƙaunarsu da zuciya ɗaya.
168 Ina biyayya da umarnanka da koyarwarka, Kana kuwa ganin dukan abin da nake yi.
169 Bari kukana yă kai gare ka, ya Ubangiji! Ka ganar da ni kamar yadda ka alkawarta.
170 Bari addu'ata ta zo gare ka, Ka cece ni kamar yadda ka alkawarta!
171 Zan yabe ka kullayaumin Domin ka koya mini ka'idodinka.
172 Zan raira waƙa a kan alkawarinka, Domin umarnanka a gaskiya ne.
173 Kullum a shirye kake domin ka taimake ni, Saboda ina bin umarnanka.
174 Ina sa zuciya ga cetonka ƙwarai, ya Ubangiji! Ina samun farin ciki ga dokarka.
175 Ka rayar da ni don in yabe ka, Ka sa koyarwarka su taimake ni!
176 Ina kai da kawowa kamar ɓatacciyar tunkiya, Ka zo ka neme ni, ni bawanka, Saboda ban ƙi kulawa da dokokinka ba.
1 Sa'ad da nake shan wahala, Na yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa amsa mini.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, Daga maƙaryata da masu ruɗi!
3 Ku maƙaryata, me Allah zai yi da ku? Yaya zai hukunta ku?
4 Da kibau masu tsini na mayaƙa, Da garwashin wuta zai hukunta ku!
5 Zama tare da ku mugun abu ne, kamar zama a Meshek, Ko tare da mutanen Kedar!
6 Na daɗe ƙwarai ina zama tare da mutane marasa son salama!
7 Sa'ad da nake maganar salama, Su sai su yi ta yaƙi.
1 Na duba wajen duwatsu, Daga ina taimakona zai zo?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
3 Ba zai bar ka ka fāɗi ba, Makiyayinka, ba zai yi barci ba!
4 Makiyayin Isra'ila, Ba ya gyangyaɗi ko barci!
5 Ubangiji zai lura da kai, Yana kusa da kai domin ya kiyaye ka.
6 Ba za ka sha rana ba, Ko farin wata da dare.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan hatsari, Zai sa ka zauna lafiya.
8 Zai kiyaye shigarka da fitarka, Tun daga yanzu har abada.
1 Na yi murna sa'ad da suka ce mini, “Tashi mu tafi Haikalin Ubangiji!”
2 Ga shi kuwa, mun iso, Muna tsaye a ƙofofin Urushalima!
3 Urushalima birni ce wadda aka maido ta yadda take dā, Da kyakkyawan tsari, a shirye!
4 A nan kabilai sukan zo, Kabilan Isra'ila, Domin su yi godiya ga Ubangiji, Kamar yadda ya umarce su.
5 A nan majalisu suke, Wurin da sarki yake yi wa jama'arsa shari'a.
6 Ku yi wa Urushalima addu'ar salama! “Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!
7 Salama ta samu a garukanki, Da zaman lafiya kuma a fādodinki.”
8 Saboda abokaina da aminaina, Na ce wa Urushalima, “Salama a gare ki!”
9 Saboda Haikalin Ubangiji, Allahnmu, Ina addu'a domin ki arzuta.
1 Ya Ubangiji, ina zuba ido gare ka, A Sama inda kake mulki.
2 Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa, Baranya kuma ga uwargijiyarta, Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu, Har mu sami jinƙanka.
3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, An gwada mana wulakanci matuƙa!
4 Attajirai sun daɗe suna ta yi mana ba'a, Azzalumai masu girmankai sun raina mu!
1 Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu, Da me zai faru? Ba da amsa, ya Isra'ila!
2 “Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu, A lokacin da abokan gābanmu suka auka mana,
3 Da sun haɗiye mu da rai a lokacin nan, Saboda zafin fushi da suke yi da mu,
4 Da rigyawa ta kwashe mu, Da ruwa yi ci mu,
5 Kwararowar ruwa ya nutsar da mu.”
6 Sai mu gode wa Ubangiji, Da bai bar abokan gābanmu su hallaka mu ba.
7 Mun kuɓuta kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta, Tarkon ya tsinke, mun 'yantu!
8 Taimakonmu daga wurin Ubangiji yake zuwa, Shi wanda ya yi sama da duniya.
1 Waɗanda suke dogara ga Ubangiji, Suna kama da Dutsen Sihiyona, Wanda ba zai jijjigu ba, faufau. Faufau kuma ba za a kawar da shi ba.
2 Kamar yadda duwatsu suka kewaye Urushalima, Haka nan Ubangiji zai kewaye jama'arsa, Daga yanzu har abada.
3 Ba a koyaushe mugaye za su yi mulki a ƙasar jama'ar Allah ba, Idan kuwa suka yi, to, ya yiwu jama'ar Allah su yi laifi.
4 Ya Ubangiji, ka yi wa mutanen kirki alheri, Su waɗanda suke biyayya da umarnanka!
5 Amma ka hukunta waɗanda suke bin mugayen al'amuransu, Sa'ad da kake hukunta wa masu aikata mugunta! Salama ta kasance tare da Isra'ila!
1 Sa'ad da Ubangiji ya komar da mu cikin Sihiyona, Sai abin ya zama kamar mafarki!
2 Muka kece da dariya, muka raira waƙa don farin ciki, Sa'an nan sai sauran al'umma suka ambace mu, suka ce, “Ubangiji ya yi manyan al'amura masu girma, sabili da su!”
3 Hakika ya aikata manyan al'amura sabili da mu, Mun kuwa yi farin ciki ƙwarai!
4 Ya Ubangiji, ka komar da mu ƙasarmu Kamar yadda ruwan da kake yi yakan koma cikin busassun koguna,
5 Ka sa waɗanda suke kuka a lokacin da suke dashe, Su tattara albarkar kaka da farin ciki!
6 Su waɗanda suka yi kuka a sa'ad da suka fita suna ɗauke da iri, Za su komo ɗauke da albarkar kaka, Suna raira waƙa don farin ciki!
1 Idan ba Ubangiji ne ya gina gidan ba, Aikin magina banza ne. Idan ba Ubangiji ne ya tsare birnin ba, Ba wani amfani a sa matsara su yi tsaro.
2 Ba wani amfani a sha wahalar aiki saboda abinci, A yi asubancin tashi, a yi makarar kwanciya, Gama Ubangiji yakan hutar da waɗanda yake ƙauna.
3 'Ya'ya kyauta ne daga wurin Ubangiji, Albarka ce ta musamman.
4 'Ya'ya maza da mutum ya haifa a lokacin ƙuruciyarsa Kamar kibau suke a hannun mayaƙi.
5 Mai farin ciki ne mutumin da yake da irin waɗannan kibau da yawa! Faufau ba za a ci nasara a kansa ba, Sa'ad da ya kara da maƙiyansa a wurin shari'a.
1 Mai farin ciki ne wanda yake tsoron Ubangiji, Wanda yake zamansa bisa ga umarnansa!
2 Za ka sami isasshen abin biyan bukatarka, Za ka yi farin ciki ka arzuta.
3 Matarka za ta zama kamar kurangar inabi Mai 'ya'ya a gidanka, 'Ya'yanka maza kuma kamar dashen zaitun Suna kewaye da teburinka.
4 Mutumin da yake yi wa Ubangiji biyayya, Hakika za a sa masa albarka kamar haka.
5 Ubangiji ya sa maka albarka daga Sihiyona! Ya sa ka ga Urushalima ta arzuta Dukan kwanakinka!
6 Ya kuma sa ka ka ga jikokinka! Salama ta kasance ga Isra'ila!
1 Isra'ila, sai ka faɗi irin muguntar Da maƙiyanka suka tsananta maka da ita, Tun kana ƙarami!
2 “Maƙiyana suka tsananta mini da mugunta, Tun ina ƙarami, Amma ba su yi nasara da ni ba.
3 Suka sa mini raunuka masu zurfi a bayana, Suka mai da shi kamar gonar da aka nome.
4 Amma Ubangiji mai adalci, Ya 'yantar da ni daga bauta.”
5 Allah ya sa duk waɗanda suke ƙin Sihiyona, A yi nasara da su a kuma kore su!
6 Allah ya sa su zama kamar ciyawar da take girma a kan soraye, Ta kuwa bushe kafin ta isa yanka.
7 Ba wanda zai tattara ta, Ya ɗaure ta dami dami.
8 Duk waɗanda suke wucewa a hanya ba za su ce, “Ubangiji ya sa maka albarka!” ba, Ko su ce, “Muna sa maka albarka da sunan Ubangiji!”
1 A cikin fid da zuciyata, Na yi kira gare ka, ya Ubangiji.
2 Ka ji kukana, ya Ubangiji, Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!
3 Idan kana yin lissafin zunubanmu, Wa zai kuɓuta daga hukunci?
4 Amma kakan gafarta mana, Domin mu zama masu tsoronka.
5 Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji, Ga maganarsa na dogara.
6 Ina jiran Ubangiji, Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir, I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir.
7 Ya Isra'ila, ki dogara ga Ubangiji, Saboda ƙaunarsa madawwamiya ce, A koyaushe yana da nufin yin gafara.
8 Zai fanshi jama'arsa Isra'ila Daga dukan zunubansu.
1 'Ya Ubangiji, na rabu da girmankai, Na bar yin fariya, Ba ruwana da manyan al'amura, Ba ruwana kuma da zantuttukan da suka fi ƙarfina.
2 Amma na haƙura, raina a kwance, Kamar jinjirin da yake kwance jalisan a hannun mahaifiyarsa, Haka zuciyata take kwance.
3 Ya Isra'ila, ka dogara ga Ubangiji, Daga yanzu har abada!
1 Ya Ubangiji, kada ka manta da Dawuda Da dukan irin aikin da ya yi.
2 Ka tuna, ya Ubangiji, da alkawarin da ya yi, Da rantsuwar da ya yi maka, ya Maɗaukaki, Allah na Isra'ila,
3 “Ba zan tafi gida ko in kwanta ba,
4 Ba zan huta, ko in yi barci ba,
5 Sai sa'ad da na shirya wa Ubangiji wuri, Wato Haikali domin Maɗaukaki, Allah na Isra'ila.”
6 Mun ji labari akwatin alkawari yana Baitalami, Amma muka same shi a kurmi.
7 Muka ce, “Bari mu tafi Haikalin Ubangiji, Mu yi sujada a gaban kursiyinsa!”
8 Ka zo wurin hutawarka, ya Ubangiji, Tare da akwatin alkawari, Alama ce ta ikonka.
9 Ka suturta firistoci da adalci, Ka sa dukan jama'arka su yi sowa ta farin ciki!
10 Ka yi wa bawanka Dawuda alkawari, Kada ka rabu da zaɓaɓɓen sarkinka, ya Ubangiji!
11 Ka yi wa Dawuda muhimmin alkawari, Ba kuwa za ka ta da alkawarin ba. Ka ce, “Za naɗa ɗaya daga cikin 'ya'yanka maza yă zama sarki, Zai yi mulki a bayanka.
12 Idan 'ya'yanka maza za su amince da alkawarina, Da umarnan da na yi musu, 'Ya'yansu maza kuma za su bi bayanka su zama sarakuna, A dukan lokaci.”
13 Ubangiji ya yaɓi Sihiyona, A can yake so ya gina Haikalinsa, ya ce,
14 “A nan zan zauna har abada. A nan kuma nake so in yi mulki.
15 Zan tanada wa Sihiyona dukan abin da take bukata a yalwace, Zan ƙosar da matalautanta da abinci.
16 Zan sa firistocinta su yi shela, Cewa ina yin ceto, Jama'ata kuma za su raira waƙa, Suna sowa don farin ciki.
17 A nan ne zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyar Dawuda Yake zama babban sarki, A nan ne kuma zan wanzar da Mulkin zaɓaɓɓen sarkina.
18 Zan sa maƙiyansa su sha kunya, Amma mulkinsa zai arzuta. Ya kuma kahu.”
1 Abu mai kyau ne, mai daɗi kuma, Ga jama'ar Allah su zauna tare kamar 'yan'uwa!
2 Yana kama da man zaitun mai daraja, Wanda yake naso daga bisa kan Haruna zuwa gemunsa, Har zuwa wuyan riganunsa.
3 Kamar raɓa a bisa Dutsen Harmon, Wadda take zubowa a bisa tuddan Sihiyona. A can ne Ubangiji ya alkawarta albarkarsa, Rai na har abada.
1 Ku zo mu yabi Ubangiji, Dukanku bayinsa, Dukanku waɗanda kuke yi masa hidima, A cikin Haikalinsa da dare.
2 Ku ɗaga hannuwanku sama, ku yi addu'a a Haikali, Ku yabi Ubangiji!
3 Ubangiji wanda ya yi sama da duniya, Ya sa muku albarka daga Sihiyona.
1 Ku yabi Ubangiji! Ku yabi sunansa, ku bayin Ubangiji,
2 Ku da kuke tsaye a Haikalin Ubangiji, A wuri mai tsarki na Allahnmu.
3 Ku yabi Ubangiji, domin nagari ne shi, Ku raira yabbai ga sunansa, domin shi mai alheri ne.
4 Ya zaɓar wa kansa Yakubu, Jama'ar Isra'ila kuwa tasa ce.
5 Na sani Ubangijinmu mai girma ne, Ya fi dukan alloli girma.
6 Yana aikata dukan abin da ya ga dama a Sama ko a duniya, A tekuna, da kuma zurfafan da suke ƙarƙas.
7 Yakan kawo gizagizan hadiri daga bangayen duniya, Yakan yi walƙiya domin hadura, Yakan fito da iska daga cikin taskarsa.
8 A Masar ne ya karkashe 'ya'yan fari na mutane da na dabbobi.
9 A can ne ya aikata mu'ujizai da al'ajabai, Domin ya hukunta Fir'auna da dukan hukumar ƙasarsa.
10 Ya hallakar da sauran al'umma masu yawa, Ya karkashe sarakuna masu iko, wato
11 Sihon, Sarkin Amoriyawa, da Og, Sarkin Bashan, Da dukan sarakunan Kan'ana.
12 Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa, Ya ba da ita ga Isra'ila.
13 Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah, Dukan tsararraki za su tuna da kai.
14 Ubangiji zai ji juyayin mutanensa, Zai 'yantar da bayinsa.
15 Gumakan al'ummai, da azurfa da zinariya aka yi su, Hannuwan mutane ne suka siffata su.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, Da idanu, amma ba sa gani.
17 Suna da kunnuwa, amma ba sa ji, Ba kuma numfashi a bakinsu.
18 Ka sa su waɗanda suka yi su, Da dukan waɗanda suke dogara gare su, Su zama kamar gumakan da suka yi!
19 Ku yabi Ubangiji, ya jama'ar Isra'ila, Ku yabe shi, ya ku firistocin Allah!
20 Ku yabi Ubangiji, ya ku Lawiyawa, Ku yabe shi, dukanku da kuke tsoronsa!
21 Ku yabi Ubangiji a Sihiyona da a Urushalima, wato a Haikalinsa. Ku yabi Ubangiji!
1 Ku gode wa Ubangiji domin shi mai alheri ne, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
2 Ku gode wa Allahn da ya fi dukan alloli girma, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
3 Ku gode wa Ubangijin dukan iyayengiji, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
4 Shi kaɗai ne yake aikata mu'ujizai masu girma, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
5 Ta wurin hikimarsa ya halicci sammai, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
6 Ya kafa duniya a bisa kan ruwa mai zurfi, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
7 Shi ne ya halicci rana da wata, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce,
8 Rana don ta yi mulkin yini, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce,
9 Wata da taurari kuwa don su yi mulkin dare, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
10 Shi ya karkashe 'ya'yan fari maza, na Masarawa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
11 Shi ya fito da jama'ar Isra'ila daga cikin Masar, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
12 Da ƙarfinsa da ikonsa ya fito da su, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
13 Shi ne ya keta Bahar Maliya biyu, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
14 Shi ya bi da jama'arsa ta cikin tekun, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
15 Shi ne ya sa ruwa ya ci Fir'auna da rundunarsa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
16 Ya bi da jama'arsa cikin hamada, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
17 Ya karkashe sarakuna masu iko, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
18 Ya karkashe shahararrun sarakuna, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
19 Ya kashe Sihon, Sarkin Amoriyawa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
20 Ya kashe Og, Sarkin Bashan, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
21 Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
22 Ya ba da ita ga bawansa Isra'ila, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
23 Bai manta da mu sa'ad da aka yi nasara da mu ba, Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.
24 Ya 'yantar da mu daga abokan gābanmu, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
25 Yana ba da abinci ga dukan mutane da dabbobi, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.
26 Ku yi wa Allah sa Sama godiya, Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.
1 A bakin kogunan Babila Muka zauna muka yi ta kuka, Sa'ad da muka tuna da Sihiyona.
2 A rassan itatuwan wardi da suke kusa da mu Muka rataye garayunmu.
3 Waɗanda suka kama mu suka sa mu mu yi waƙa, Suka ce mana, “Ku yi mana shagali Da waƙar da aka raira wa Sihiyona!”
4 Kaƙa za mu raira waƙar Ubangiji A baƙuwar ƙasa?
5 Da ma kada in ƙara iya kaɗa garaya, Idan na manta da ke, Urushalima!
6 Da ma kada in ƙara iya raira waƙa, Idan na manta da ke, Idan ban tuna ke ce Babbar abar farin ciki ba!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, da abin da Edomawa suka yi, A ranar da aka ci Urushalima. Ka tuna da yadda suka ce, “A ragargaza ta har ƙasa!”
8 Babila, za a hallaka ki! Mai farin ciki ne shi wanda ya sāka miki Bisa ga abin da kika yi mana.
9 Mai farin ciki ne shi wanda zai kwashi jariranki Yă fyaɗa su a kan duwatsu!
1 Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji, Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli.
2 Na durƙusa a gaban tsattsarkan Haikalinka Ina yabon sunanka. Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka, Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka.
3 Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka, Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.
4 Dukan sarakunan duniyar nan za su yabe ka, ya Ubangiji, Gama sun riga sun ji alkawaranka.
5 Za su raira waƙa a kan abin da Ubangiji ya yi, Za su raira waƙa kuma a kan ɗaukakarsa mai girma.
6 Ko da yake Ubangiji yana can Sama, Duk da haka yana kulawa da masu kaɗaici. Masu girmankai kuwa ba za su iya ɓoye kansu daga gare shi ba.
7 Ko lokacin da nake tsakiyar wahala, Za ka kiyaye ni lafiya, Ka yi gāba da abokan gābana, waɗanda suka husata, Za ka kuwa cece ni da ikonka.
8 Za ka aikata kowane abu da ka alkawarta mini, Ya Ubangiji, ƙaunarka madawwamiya ce har abada. Ka cikasa aikin da ka fara.
1 Ya Ubangiji, ka jarraba ni, ka san ni.
2 Ka sa dukan abin da nake yi, Tun daga can nesa ka gane dukan tunanina.
3 Kana ganina, ko ina aiki, ko ina hutawa, Ka san dukan ayyukana.
4 Tun kafin in yi magana Ka riga ka san abin da zan faɗa.
5 Kana kewaye da ni a kowane sashe, Ka kiyaye ni da ikonka.
6 Yadda ka san ni ya fi ƙarfin magana, Ya yi mini zurfi, ya fi ƙarfin ganewata.
7 Ina zan tafi in tsere wa Ruhunka? Ina zan gudu in tsere maka?
8 Idan na hau cikin samaniya kana can, In na kwanta a lahira kana can,
9 In na tashi sama, na tafi, na wuce gabas, Ko kuma na zauna a can yamma da nisa,
10 Kana can domin ka bi da ni, Kana can domin ka taimake ni.
11 Da na iya roƙon duhu ya ɓoye ni, Ko haske da yake kewaye da ni Ya zama dare,
12 Amma har duhun ma, ba duhu ba ne a gare ka, Dare kuwa haskensa kamar na rana ne. Duhu da haske, duk ɗaya ne gare ka.
13 Kai ne ka halicci kowace gaɓa ta jikina, Kai ne ka harhaɗa ni a cikin mahaifiyata.
14 Ina yabonka gama kai abin tsoro ne, Dukan abin da ka yi sabo ne, mai banmamaki. Da zuciya ɗaya na san haka ne.
15 Ka ga lokacin da ƙasusuwana suke siffatuwa, Sa'ad da kuma ake harhaɗa su a hankali A cikin mahaifiyata, Lokacin da nake girma a asirce.
16 Ka gan ni kafin a haife ni. Ka ƙididdige kwanakin da ka ƙaddara mini, Duka an rubuta su a littafinka, Tun kafin faruwar kowannensu.
17 Ya Allah, tunaninka suna da wuyar ganewa a gare ni, Ba su da iyaka!
18 In na ƙirga su, za su fi tsabar yashi, Sa'ad da na farka, har yanzu ina tare da kai.
19 Ya Allah, da yadda nake so ne, da sai ka karkashe mugaye! 'Yan ta da zaune tsaye kuma sai su rabu da ni!
20 Suna ambaton mugayen abubuwa a kanka, Suna faɗar mugayen abubuwa gāba da sunanka.
21 Ya Ubangiji, ga yadda nake ƙin waɗanda suke ƙinka, Da yadda nake raina waɗanda suke tayar maka!
22 Ƙiyayyar da nake yi musu ta kai intaha, Na ɗauke su, su abokan gābana ne.
23 Jarraba ni, ya Allah, ka san tunanina, Gwada ni, ka gane damuwata.
24 Ka bincike, ko akwai wani rashin gaskiya a gare ni, Ka bi da ni a madawwamiyar hanya.
1 Ka cece ni daga mugaye, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga mutane masu hargitsi.
2 Kullum suna shirya mugunta, Kullum suna kawo tashin hankali.
3 Harsunansu kamar macizai masu zafin dafi, Kalmominsu kuwa kamar dafin gamsheƙa ne.
4 Ka tsare ni daga ikon masu mugunta, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga masu tashin hankali, Waɗanda suke shirya fāɗuwata.
5 Masu girmankai sun kafa mini tarko, Sun shimfiɗa ragar igiya, Sun kuma kakkafa tarkuna a hanya don su kama ni.
6 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Allahna. Ka ji kukana na neman taimako, ya Ubangiji!
7 Ya Ubangiji, Allahna, Mai Cetona, mai ƙarfi, Kā kiyaye ni cikin yaƙi.
8 Ya Ubangiji, kada ka biya wa mugaye burinsu, Kada ka bar mugayen dabaru su yi nasara!
9 “Kada ka bar maƙiyana su sami nasara, Ka sa kashedin da suke yi mini yă koma kansu.
10 Ka sa garwashin wuta yă zubo a kansu, Ka sa a jefa su a rami, kada su ƙara fita.
11 Ka sa waɗanda suke saran waɗansu a ƙaryace, Kada su yi nasara. Ka sa mugunta ta hallaka mutumin da yake ta da zaune tsaye.”
12 Na sani kai, ya Ubangiji, kana kāre matsalar talakawa, Da hakkin matalauta.
13 Hakika adalai za su yabe ka, Za su zauna a gabanka.
1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Ka taimake ni yanzu! Ka saurare ni sa'ad da na kira gare ka.
2 Ka karɓi addu'ata kamar turaren ƙonawa, Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice.
3 Ya Ubangiji, ka sa a yi tsaron bakina, Ka sa mai tsaro a leɓunana.
4 Ka tsare ni daga son yin mugunta, Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu, Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu!
5 Nagarin mutum ya iya hukunta ni, ya tsauta mini da alheri, Zai zamar mini kamar an shafe kaina da mai, Domin kullayaumi ina addu'a gāba da mugayen ayyuka.
6 Mutane za su yarda, cewa maganata gaskiya ce, Sa'ad da aka jefo da masu mulkinsu ƙasa, daga ƙwanƙolin dutse,
7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse, Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari.
8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka, Ina neman kiyayewarka, Kada ka bar ni in halaka!
9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini, Daga ashiftar masu aikata mugunta.
10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu, Ni kuwa in zo in wuce lafiya.
1 Ina kira ga Ubangiji don neman taimako, Ina roƙonsa.
2 Na kawo masa dukan koke-kokena, Na faɗa masa dukan wahalaina.
3 Sa'ad da na yi niyyar fid da zuciya, Ya san abin da zan yi. A kan hanyar da zan bi Maƙiyana sun kafa mini tarko a ɓoye.
4 Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni, Ba wanda zai kiyaye ni, Ba kuwa wanda ya kula da ni.
5 Ya Ubangiji, na kawo kuka gare ka na neman taimako, Ya Ubangiji, kai ne mai kiyaye ni, Kai kaɗai nake so a rayuwata duka.
6 Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako, Gama na nutsa cikin fid da zuciya. Ka cece ni daga maƙiyana Waɗanda suka fi ƙarfina.
7 Ka cece ni daga cikin wahalata, Sa'an nan zan yabe ka cikin taron jama'arka, Domin ka yi mini alheri.
1 Ya Ubangiji ka ji addu'ata, Ka kasa kunne ga roƙona! Kai adali ne mai aminci, Don haka ka amsa mini!
2 Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari'a, Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka.
3 Maƙiyina ya tsananta mini, Ya kore ni fata-fata. Ya sa ni a kurkuku mai duhu, Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa,
4 Don haka ina niyya in fid da zuciya, Ina cikin damuwa mai zurfi.
5 Na tuna kwanakin baya, Na tuna da dukan abin da ka yi, Na tuna da dukan ayyukanka.
6 Na ɗaga hannuwana sama, ina addu'a gare ka, Kamar busasshiyar ƙasa, raina yana jin ƙishinka.
7 Yanzu ka amsa mini, ya Ubangiji! Na fid da zuciya duka! Kada ka ɓuya mini, Don kada in zama cikin waɗanda suke gangarawa zuwa lahira.
8 A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi.
9 Na tafi wurinka don ka kiyaye ni, ya Ubangiji, Ka cece ni daga maƙiyana.
10 Kai ne Allahna, Ka koya mini in aikata nufinka. Ka sa in sami alherin Ruhunka. Ka bi da ni a hanyar lafiya.
11 Ka cece ni, ya Ubangiji, kamar yadda ka alkawarta. Saboda alherinka ka tsamo ni daga wahalaina!
12 Saboda ƙaunar da kake yi mini, Ka kashe maƙiyana. Ka hallakar da dukan waɗanda suke zaluntata. Gama ni bawanka ne.
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, mai kiyaye ni, Ya hore ni don yaƙi, Ya kuwa shirya ni don yaƙi.
2 Shi yake kiyaye ni, Shi yake kāre ni, Shi ne mafakata da Mai Cetona, Wanda nake dogara gare shi Don samun zaman lafiya. Shi ne ya ɗora ni a kan al'ummai.
3 Ya Ubangiji wane ne mutum, har da kake lura da shi? Wane ne ɗan adam kurum, har da kake kulawa da shi?
4 Shi kamar hucin iska yake, Kwanakinsa kuwa kamar inuwa mai wucewa ne.
5 Ya Ubangiji, ka kware sararin sama, ka sauko, Ka taɓa duwatsu, don su tuƙaƙo da hayaƙi.
6 Ka aiko da walƙiyar tsawa ta warwatsa maƙiyanka, Ka harba kibanka, ka sa su sheƙa a guje!
7 Ka sunkuyo daga Sama, Ka tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi, ka cece ni, Ka cece ni daga ikon baƙi,
8 Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya.
9 Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah, Zan kaɗa garaya in raira maka waƙa.
10 Ka ba sarakuna nasara, Ka kuma ceci bawanka Dawuda.
11 Ka cece ni daga mugayen abokan gābana, Ka ƙwato ni daga ikon baƙi, Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya.
12 Ka sa 'ya'yanmu maza waɗanda suke cikin samartaka, Su zama kamar itatuwan da yake girma da ƙarfi. Ka sa 'ya'yanmu mata Su zama kamar al'amudai, Waɗanda suke adanta kusurwoyin fāda.
13 Ka sa rumbunanmu su cika Da kowane irin amfanin gona. Ka sa tumakin da suke cikin saurukanmu Su hayayyafa dubu dubu har sau goma,
14 Ka sa shanunmu su hayayyafa, Kada su yi ɓari ko su ɓace. Ka sa kada a ji kukan damuwa a kan titunanmu!
15 Mai farin ciki ce al'ummar Da abin nan da aka faɗa ya zama gaskiya a gare ta. Masu farin ciki ne jama'ar da Allahnsu shi ne Ubangiji!
1 Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina, Zan yi maka godiya har abada abadin.
2 Kowace rana zan yi maka godiya, Zan yabe ka har abada abadin.
3 Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa, Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.
4 Za a yabi abin da ka aikata daga tsara zuwa tsara, Za su yi shelar manya manyan ayyukanka.
5 Mutane za su yi magana a kan darajarka da ɗaukakarka, Ni kuwa zan yi ta tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 Mutane za su yi magana a kan manya manyan ayyukanka, Ni kuwa zan yi shelar girmanka.
7 Za su ba da labarin girmanka duka, Su kuma raira waƙa a kan alherinka.
8 Ubangiji mai ƙauna ne, mai jinƙai, mai jinkirin fushi, Cike da madawwamiyar ƙauna.
9 Shi mai alheri ne ga kowa, Yana juyayin dukan abin da ya halitta.
10 Ya Ubangiji, talikanka duka za su yabe ka, Jama'arka kuma za su yi maka godiya!
11 Za su yi maganar darajar mulkinka, Su ba da labarin ikonka,
12 Domin haka dukan mutane za su san manyan ayyukanka, Da kuma darajar ɗaukakar mulkinka.
13 Mulkinka, madawwamin mulki ne, Sarki ne kai har abada.
14 Ubangiji, yakan taimaki dukan waɗanda yake shan wahala, Yakan ta da waɗanda aka wulakanta.
15 Dukan masu rai suna sa zuciya gare shi, Yana ba su abinci a lokacin da suke bukata,
16 Yana kuwa ba su isasshe, Yakan biya bukatarsu duka.
17 Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka, Mai jinƙai ne a ayyukansa duka.
18 Yana kusa da dukan waɗanda suke kira gare shi, Waɗanda suke kiransa da zuciya ɗaya.
19 Yakan biya bukatar dukan waɗanda suke tsoronsa, Yakan ji kukansu, ya cece su.
20 Yakan kiyaye dukan waɗanda suke ƙaunarsa, Amma zai hallaka mugaye duka.
21 A kullum zan yabi Ubangiji, Bari talikai duka su yabi sunansa mai tsarki har abada!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ka yabi Ubanigji, ya raina!
2 Zan yabe shi muddin raina. Zan raira waƙa ga Allahna dukan kwanakina.
3 Kada ka dogara ga shugabanni, Ko kowane mutum da ba zai iya cetonka ba.
4 Sa'ad da suka mutu sai su koma turɓaya, A wannan rana dukan shirye-shiryensu sun ƙare.
5 Mai farin ciki ne mutumin da Allah na Yakubu ne yake taimakonsa, Yana kuma dogara ga Ubangiji Allahnsa,
6 Wanda ya halicci sama, da duniya, da teku, Da dukan abin da yake cikinsu. Kullum yakan cika alkawaransa.
7 A yanke shari'arsa yakan ba wanda aka zalunta gaskiya. Yana ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan kuɓutar da ɗaurarru.
8 Yakan ba makafi ganin gari. Yakan ɗaukaka waɗanda aka wulakanta. Yana ƙaunar jama'arsa, adalai.
9 Yakan kiyaye baƙi waɗanda suke zaune a ƙasar. Yakan taimaki gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu. Yakan lalatar da dabarun mugaye.
10 Ubangiji Sarki ne har abada! Ya Sihiyona, Allahnki zai yi mulki har dukan zamanai! Yabo Ya tabbata ga Ubangiji!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Abu mai kyau ne mu yabi Allahnmu, Abu mai daɗi ne, daidai ne kuma, a yabe shi.
2 Ubangiji yana rayar da Urushalima, Yana komo da waɗanda aka kai su baƙunci a wata ƙasa.
3 Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya, Yakan ɗaure raunukansu.
4 Ya ƙididdige yawan taurari, Yakan kira kowanne da sunansa.
5 Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka, Saninsa ya fi gaban aunawa.
6 Yakan ɗaukaka masu tawali'u, Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa.
7 Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji, Ku yabi Allah da garaya.
8 Ya shimfiɗa gajimare a sararin al'arshi. Ya tanada wa duniya ruwan sama, Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.
9 Yakan ba dabbobi abincinsu, Yakan ciyar da 'ya'yan hankaki sa'ad da suka yi kuka gare shi.
10 Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai, Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.
11 Amma yana jin daɗin waɗanda suke tsoronsa, Yana jin daɗin waɗanda suke dogara da madawwamiyar ƙaunarsa.
12 Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji, Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki.
13 Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi, Yakan sa wa jama'arki albarka.
14 Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya, Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Yakan ba da umarni, Nan da nan umarnin yakan iso duniya.
16 Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu, Ya watsa jaura kamar ƙura.
17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu, Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko!
18 Sa'an nan yakan ba da umarni, Ƙanƙara kuwa ta narke, Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu.
19 Yana ba Yakubu saƙonsa, Koyarwarsa da dokokinsa kuma ga Isra'ila.
20 Bai yi wa sauran al'umma wannan ba, Domin ba su san dokokinsa ba. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji daga sama, Ku da kuke zaune a tuddan sama.
2 Ku yabe shi dukanku mala'ikunsa, Ku yabe shi, ku dukan rundunansa na sama!
3 Ku yabe shi, ku rana da wata, Ku yabe shi, ku taurari masu haskakawa!
4 Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi duka! Ku yabe shi, ku ruwayen da kuke bisa sararin sama!
5 Bari su duka su yabi sunan Ubangiji! Ya umarta, sai suka kasance.
6 Ta wurin umarninsa aka kafa su A wurarensu har abada, Ba su kuwa da ikon ƙi.
7 Ku yabi Ubangiji daga duniya, Ku yabi Ubangiji, ku dodanin ruwa da dukan zurfafan teku.
8 Ku yabe shi, ku walƙiya, da ƙanƙara, da dusar ƙanƙara, Da gizagizai, da ƙarfafan iska waɗanda suke biyayya da umarnansa!
9 Ku yabe shi, ku tuddai da duwatsu, Da itatuwa 'ya'ya da kurama.
10 Ku yabe shi dukanku dabbobi, na gida da na jeji, Masu rarrafe da tsuntsaye!
11 Ku yabe shi, ku sarakuna da dukan kabilai, Ku yabe shi, ku shugabanni da dukan hukumomi.
12 Ku yabe shi ku samari da 'yan mata! Ku yabe shi, ku tsoffafi da yara!
13 Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji, Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma, Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!
14 Ya sa al'ummarsa ta yi ƙarfi, Domin dukan jama'arsa su yabe shi Jama'arsa Isra'ila, wadda yake ƙauna ƙwarai! Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji Ku yabe shi cikin taron jama'arsa masu aminci!
2 Ki yi murna, ke Isra'ila, sabili da Mahaliccinki, Ku yi farin ciki, ku jama'ar Sihiyona, sabili da Sarkinku!
3 Ku yabi sunansa, kuna taka rawa, Ku kaɗa bandiri da garayu, kuna yabonsa.
4 Ubangiji yana jin daɗin jama'arsa, Yakan girmama mai tawali'u ya sa ya ci nasara.
5 Bari jama'ar Allah su yi farin ciki saboda cin nasararsu, Su raira waƙa don farin ciki.
6 Bari su yi sowa da ƙarfi Sa'ad da suke yabon Allah, da takubansu masu kaifi.
7 Don su ci nasara bisa al'ummai, Su kuma hukunta wa jama'a,
8 Su ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi, Su ɗaure shugabanninsu da sarƙoƙin baƙin ƙarfe,
9 Su hukunta wa al'ummai, kamar yadda Allah ya umarta. Wannan shi ne cin nasarar jama'ar Allah! Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku yabi Allah a cikin Haikalinsa! Ku yabi ƙarfinsa a sama!
2 Ku yabe shi saboda manyan abubuwa Waɗanda ya aikata! Ku yabi mafificin girmansa!
3 Ku yabe shi da kakaki! Ku yabe shi da garayu da molaye!
4 Ku yabe shi da bandiri kuna taka rawa! Ku yabe shi da garayu da sarewa!
5 Ku yabe shi da kuge! Ku yabe shi da kuge masu amo!
6 Ku yabi Ubangiji dukanku rayayyun talikai. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!