1 Karin maganar Sulemanu, ɗan Dawuda, Sarkin Isra'ila.
2 Ga Karin magana da za su taimake ka ka rarrabe da hikima, da kyakkyawar shawara, da fahimtar ma'anar zurfafan karin magana,
3 da yadda za ka karɓi koyarwa ta hanyar hikima, da adalci, da gaskiya, da sanin abin da yake daidai.
4 Sukan sa marar sani ya zama masani, sukan koya wa samari yadda za su zama masu amfani.
5 Waɗannan karin magana sukan ƙara wa masu ilimi hikima, sukan zama jagora ga masana,
6 don su fahimci ɓoyayyiyar ma'anar da take cikin karin magana, da mawuyatan al'amura waɗanda masu hikima suka ƙago.
7 In kana so ilimi dole ne ka fara da tsoron Ubangiji. Jahilai ba su san darajar hikima ba, sun kuwa ƙi su koya.
8 Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, ka mai da hankali ga abin da mahaifiyarka take faɗa.
9 Koyarwarsu za ta inganta halinka, ta zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau.
10 Ɗana sa'ad da masu zunubi suka jarabce ka, kada ka yarda
11 in suka ce maka, “Zo mu tafi mu nemi wani mutum mu kashe, mu je, mu fāɗa wa marasa laifi mu ji daɗi!
12 Ba mu damu da ransu da lafiyarsu ba, mu dai mu tafi mu kashe su, mu hallaka su ɗungum.
13 Za mu sami dukiya iri iri, mu cika gidajenmu da ganima!
14 Ka zo ka haɗa kai da mu, dukanmu kuwa za mu raba abin da muka sato.”
15 Ɗana, kada ka gama kanka da irin waɗannan mutane, ka yi nesa da su.
16 Ba su kasalar aikata mugunta, kullum a shirye suke su yi kisankai.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idon tsuntsun da ake so a kama.
18 Amma waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko. Ba za su kama kome ba, sai rayukansu.
19 Yin fashi yakan zama sanadin mutuwar ɗan fashi a koyaushe. Wannan shi ne abin da yakan sami kowane mutum da ya kama sana'ar sata.
20 Ku kasa kunne! Hikima tana kira a tituna da a kasuwoyi.
21 Tana kira da ƙarfi a ƙofofin birni, a duk inda mutane suke tattaruwa.
22 Ta ce, “Wawayen mutane! Har yaushe za ku yi ta kasancewa haka? Har yaushe za ku daina jin daɗin yi wa mai ilimi ba'a? Faufau ba za ku taɓa koya ba?
23 Ku kasa kunne lokacin da nake tsauta muku, zan ba ku shawara mai kyau, mu yi tarayya cikin ilimina.
24 Ina ta kiranku ina gayyatarku ku zo, amma ba ku kula ba, ba ku mai da hankali gare ni ba.
25 Kun ƙi bin shawarwarina duka, ba ku yarda in gyara kuskurenku ba.
26 Saboda haka, lokacin da kuke shan wahala, zan yi muku dariya. Zan yi muku ba'a lokacin da razana ta auka muku,
27 sa'ad da ta zo muku kamar hadiri mai ƙaƙƙarfar iska mai wahalarwa, sa'ad da kuke shan azaba da damuwa.
28 Sa'an nan za ku kira gare ni, amma ba za ku same ni ba. Za ku neme ni a ko'ina, amma ba za ku same ni ba.
29 Domin ba ku taɓa sanin amfanin ilimi ba, kun ƙi tsoron Ubangiji a kullum.
30 Ba ku taɓa yarda da shawarata ba, ko ku yarda in gyara kuskurenku.
31 Saboda haka za ku karɓi sakayyarku, ayyukanku za su cuce ku.
32 Marasa sani sukan mutu saboda ba su yarda da hikima ba. Wawaye kuwa sukan hallaka saboda rashin kulawarsu.
33 Amma duk wanda ya kasa kunne gare ni, zai zauna lafiya. Ba abin da zai same shi, ba abin da zai tsorata shi.”
1 Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi.
2 Ka kasa kunne ga abin da yake na hikima, ka yi ƙoƙari ka fahimce shi.
3 I, ka roƙi ilimi da tsinkaya.
4 Ka nema da iyakar ƙoƙarinka kamar yadda za ka nemi azurfa, ko kowace irin ɓoyayyiyar dukiya.
5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah.
6 Ubangiji ne yake ba da hikima. Ilimi da fahimi kuwa suna cikin kalmominsa.
7 Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci.
8 Yakan kiyaye waɗanda suke lura da kyau, ya kiyaye waɗanda suke dogara gare shi.
9 Idan ka kasa kunne gare ni za ka san abin da yake daidai, da abin da yake gaskiya, da abin da yake na kirki. Za ka san abin da za ka yi.
10 Za ka zama mai hikima, iliminka zai faranta maka rai.
11 Tsinkayarka da fahiminka za su tsare ka.
12 Za su hana ka aikata mugayen ayyuka, za su nisantar da kai daga mutane masu ta da hargitsi da irin maganganunsu,
13 mutane waɗanda suka bar zaman adalci don su zauna cikin duhun zunubi,
14 waɗanda suke jin daɗin yin laifi, suna nishaɗi cikin mugunta.
15 Ba za a dogara da su ba, ba kuwa za a iya amincewa da su ba.
16 Za a nisantar da kai daga mazinaciya, wadda take ƙoƙari ta lalatar da kai da daɗin bakinta,
17 marar aminci ga mijinta, wadda ta manta da tsarkakan alkawaran da ta ɗauka.
18 Idan ka tafi gidanta ka kama hanyar mutuwa. Tafiya can kama hanyar zuwa lahira ne.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa. Ba zai ƙara komowa ga hanyar rai ba.
20 Saboda haka dole ka bi hanyar da mutanen kirki suka bi, ka bi gurbin adalai.
21 Mutane adalai, masu kamewa, su ne za su zauna ƙasarmu.
22 Amma Allah zai fizge mugaye daga ƙasar, ya kuma tumɓuke masu zunubi kamar yadda ake tumɓuke shuke-shuke daga ƙasa.
1 Ɗana kada ka manta da abin da na koya maka. Kullum ka tuna da abin da na faɗa maka ka yi.
2 Koyarwata za ta ba ka tsawon rai da wadata.
3 Kada ka yarda ka rabu da biyayya da aminci, ka ɗaura su a wuyanka, ka rubuta su kuma a zuciyarka.
4 Idan ka yi wannan kuwa, Allah zai yi murna da kai. Za ka yi nasara cikin hulɗar da kake yi da mutane.
5 Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani.
6 A cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da take daidai.
7 Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata mugunta.
8 Idan ka kiyaye wannan, zai zama maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake sha.
9 Ka girmama Ubangiji ta wurin miƙa masa hadaya daga mafi kyau na amfanin gonarka.
10 Idan ka yi haka rumbunanka za su cika da hatsi. Za ka sami ruwan inabi mai yawa, har ka rasa wurin da za ka zuba shi duka.
11 Ɗana, sa'ad da Ubangiji ya tsauta maka ka mai da hankali sosai, ka kuma yarda da gargaɗinsa.
12 Ubangiji yana tsauta wa waɗanda yake ƙauna. Kamar yadda mahaifi yakan tsauta wa ɗan da yake fāriya da shi.
13 Mai farin ciki ne mutumin da ya zama mai hikima, ya kuma sami fahimi.
14 Yana da riba mai yawan gaske fiye da ta azurfa, tamaninta a gare ka ya fi na zinariya.
15 Tamanin hikima ya fi na lu'ulu'ai, ya kuma fi kowane irin abin da kake so tamani.
16 Hikima takan tsawanta ranka, ta kuma ba ka dukiya da daraja.
17 Hikima takan sa ka ji daɗin zama, ta kuma bi da kai lafiya a zamanka.
18 Masu farin ciki ne waɗanda suka sami hikima, hikima za ta ba su rai kamar yadda itace yakan ba da 'ya'ya.
19 Ubangiji ya halicci duniya ta wurin hikimarsa, Ya shimfiɗa sararin sama a inda yake ta wurin saninsa.
20 Hikimarsa ta sa ruwan koguna ya yi gudu, Gizagizai kuwa su zubo da ruwa bisa duniya.
21 Ɗana ka riƙe hikimarka da basirarka. Ko kusa kada ka bari su rabu da kai.
22 Za su tanada maka rai, rai mai daɗi da farin ciki.
23 Za ka bi hanyarka lafiya lau, ba ko tuntuɓe.
24 Ba za ka ji tsoro, sa'ad da kake kwance a gadonka ba, za ka yi ta sharar barci a dukan dare.
25 Ba za ka damu da masifar da za ta auko farat ɗaya ba, irin wadda takan auka wa mugaye kamar hadiri.
26 Ubangiji zai kiyaye ka. Ba zai bari ka fāɗa cikin tarko ba.
27 Ka yi wa masu bukata alheri a duk lokacin da kake iyawa.
28 Sam, kada ka ce wa maƙwabcinka ya dakata sai gobe, idan dai kana iya taimakonsa yanzu.
29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, gama yana zaune kusa da kai, yana kuwa amincewa da kai.
30 Kada ka yi jayayya ba dalili da wanda bai taɓa cutarka ba.
31 Kada ka ji kishin masu ta da zaune tsaye, ko ka yi sha'awar aikata ayyukansu,
32 gama Ubangiji yana ƙin mutanen da suke aikata mugunta, amma yakan rungumi adalai ya amince da su.
33 Ubangiji yakan la'antar da gidajen masu mugunta, amma yakan sa wa gidajen adalai albarka.
34 Ba ruwansa da masu girmankai, amma masu tawali'u sukan sami tagomashi a wurinsa.
35 Mutane masu hikima za su sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.
1 'Ya'yana ku kasa kunne ga koyarwar mahaifinku. Ku mai da hankali, za ku zama haziƙai.
2 Abin da nake koya muku, abu mai kyau ne, saboda haka ku tuna da shi duka.
3 Sa'ad da nake ɗan yaro tilo a wurin iyayena,
4 mahaifina yakan koya mini, yakan ce, “Ka tuna da abin da nake faɗa maka, kada ka manta. Ka yi abin da na faɗa maka za ka rayu.
5 Ka nemi hikima da basira! Kada ka manta ko ka ƙyale abin da na faɗa.
6 Kada ka rabu da hikima, gama za ta kiyaye ka, ka ƙaunace ta, za ta kiyaye lafiyarka.
7 Samun hikima shi ne mafificin abin da za ka yi. Kome za ka samu dai, ka sami basira.
8 Ka ƙaunaci hikima, za ta girmama ka. Ka rungume ta, za ta kawo maka daraja.
9 Za ta zamar maka rawanin daraja.”
10 Ɗana, ka kasa kunne gare ni. Ka ɗauki abin da nake faɗa maka, muhimmin abu ne, za ka yi tsawon rai.
11 Gama na koya maka hikima da hanyar zama mai kyau.
12 Idan ka yi tafiya da hikima ba abin da zai tsare maka hanya, sa'ad da kake gudu ba za ka yi tuntuɓe ba.
13 Kullum ka tuna da abin da ka koya, iliminka shi ne ranka, ka lura da shi da kyau.
14 Kada ka tafi inda mugaye suke tafiya, kada ka bi gurbin mugaye.
15 Kada ka yi mugunta! Ka nisance ta! Ka ƙi ta, yi tafiyarka.
16 Mugaye ba su iya yin barci, sai sun aikata ɓarna. Ba su barci sai sun cuci wani.
17 Mugunta da ta'adi kamar ci da sha suke a gare su.
18 Hanyar da adalai suke bi kamar fitowar rana ce, sai ta yi ta ƙara haske, har ta take tsaka.
19 Hanyar mugaye kuwa duhu ne baƙi ƙirin, kamar duhun dare. Sukan fāɗi, amma ba su san abin da ya sa suka yi tuntuɓe ba.
20 Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa. Ka kasa kunne ga kalmomina.
21 Kada ka kuskura su rabu da kai, ka tuna da su, ka ƙaunace su.
22 Za su ba da rai da lafiya ga dukan wanda ya fahimce su.
23 Tunane-tunanenka mafarin rai ne kansa, ka kiyaye su abin mallakarka ne mafi daraja.
24 Kada ka faɗi kowane abu da yake ba na gaskiya ba, kada wani abu ya haɗa ka da ƙarya, ko maganganun ruɗawa.
25 Ka duba gaba sosai gabanka gaɗi, ba tsoro.
26 Ka tabbata ka san abin da kake yi, duk abin da kake yi kuma zai zama daidai.
27 Ka rabu da mugunta ka yi tafiyarka sosai, kada ka kauce ko da taki ɗaya daga hanyar da take daidai.
1 Ɗana, ka mai da hankali, ka kasa kunne ga hikimata da basirata.
2 Sa'an nan ne za ka san yadda za ka yi kome daidai, kalmominka za su nuna kana da ilimi.
3 Leɓunan matar wani, mai yiwuwa ne, su yi zaƙi kamar zuma, sumbace-sumbacenta kuma su fi man zaitun taushi.
4 Amma bayan an gama duka, ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba.
5 Za ta gangara da kai zuwa lahira, hanyar da take bi hanyar mutuwa ce.
6 Ba a kan hanyar rai take ba, tana ragaita nesa da hanyar, amma kai ba ka ankara ba.
7 'Ya'yana, ku kasa kunne gare ni yanzu, kada ko kusa ku manta da abin da nake faɗa.
8 Ku yi nesa da irin wannan mace! Kada ku yarda ku yi ko kusa da ƙofarta!
9 Idan kuwa kun yi, girmamawar da ake yi muku za ta zama ta waɗansu. Za ku yi mutuwar ƙuruciya ta hannun mutane marasa imani.
10 Hakika, baƙi za su kwashe dukan dukiyarku, abin da kuka sha wahalar samu kuma zai zama rabon wani dabam.
11 Za ku kwanta kuna nishi a kan gadon mutuwa, namanku da tsokokinku za su zagwanye.
12 Sa'an nan za ku ce, “Me ya sa ban taɓa koyo ba? Me ya sa ban yarda wani ya kwaɓe ni ba?
13 Ban kasa kunne ga malamaina ba. Ban mai da hankalina gare su ba.
14 Farat ɗaya sai aka kunyatar da ni a bainar jama'a.”
15 Ka yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta ita kaɗai.
16 Idan kuma waɗansu mata sun haifa maka 'ya'ya, 'ya'yan nan ba za su yi maka wani amfani ba.
17 'Ya'yanka za su yi girma su taimake ka, ba na baƙi ba.
18 Saboda haka ka yi farin ciki tare da matarka, ka yi murna da budurwa da ka auro,
19 kyakkyawa mai kyan gani kamar barewa. Bari kyanta ya ɗau hankalinka. Bari ƙaunarta ta kewaye ka.
20 Ɗana, don me za ka fi son matar wani? Don me za ka bar matar wani ta lallame ka da daɗin bakinta?
21 Ubangiji yana ganin dukan abin da kake yi. Inda ka shiga duk yana kallonka.
22 Zunuban mutum tarko ne, komar zunubinsa ce take kama shi.
23 Yakan mutu saboda rashin kamewarsa, cikakkiyar wautarsa za ta kai shi kabarinsa.
1 Ɗana, ka taɓa yin alkawari ka ɗaukar wa wani lamuni?
2 Maganganunka sun taɓa kama ka, ko alkawaranka sun taɓa zamar maka tarko?
3 To, ɗana, kana cikin ikon wannan mutum, amma ga yadda za ka yi ka fita, sheƙa zuwa wurinsa, ka roƙe shi ya sake ka.
4 Kada ka yarda ka yi barci ko ka huta.
5 Ka fita daga cikin tarkon kamar tsuntsu ko barewar da ta tsere wa maharbi.
6 Bari ragwaye su yi koyi da tururuwa.
7 Ba su da shugaba, ba su da sarki, ko mai mulki,
8 amma da kaka sukan tanada wa kansu abinci, domin kwanakin bazara.
9 Har yaushe rago zai yi ta ɓalɓalcewa? Yaushe zai farka?
10 Yakan ce, “Bari in ɗan ruruma, in naɗa hannuwana in shaƙata.”
11 Amma lokacin da yake sharar barci, tsiya za ta auka masa kamar ɗan fashi da makamai.
12 Sakarkari, wato mugaye sukan yi ta baza jita-jita.
13 Sukan yi ƙyifce, ko su yi nuni don su yaudare ka.
14 A kowane lokaci suna shirya mugunta a kangararren hankalinsu, suna kuta tashin hankali ko'ina.
15 Saboda wannan masifa za ta fāɗa musu farat ɗaya ba makawa, za a yi musu mummunan raini.
16 Akwai abu shida, i, har bakwai ma, waɗanda Ubangiji yake ƙi, waɗanda ba zai haƙura da su ba, duban raini, harshe mai faɗar ƙarya, hannuwan da suke kashe marasa laifi, kwanyar da take tunane-tunanen mugayen dabaru, mutum mai gaggawar aikata mugunta, mai yawan shaidar zur, mutum mai ta da fitina a tsakanin abokai.
17
18
19
20 Ɗana, ka yi abin da mahaifinka ya faɗa maka, kada ka manta da koyarwar mahaifiyarka.
21 Kullum ka kiyaye abin da suke faɗa maka, ka kulle su kuma a zuciyarka.
22 Koyarwarsu za ta bi da kai sa'ad da kake tafiya, ta kiyaye ka da dare, ta kuma ba ka shawara da rana.
23 Doka da abubuwan da take koyarwa haske ne mai haskakawa. Tsautawa tana iya koya maka zaman duniya.
24 Za ta tsare ka daga mugayen mata, daga kalmomin alfasha da suke fitowa daga bakin matan waɗansu.
25 Kada kyansu ya jarabce ka, kada ka faɗa cikin tarkon feleƙensu.
26 Mutum ta dalilin karuwa zai sha hasarar abin da ya mallaka duka ta wurin zina.
27 Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa'an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba?
28 Ka iya tafiya a kan garwashi sa'an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba?
29 Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani. Duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala.
30 Mutane ba sukan raina wanda ya saci abinci don yana jin yunwa ba,
31 duk da haka in an kama shi, sai ya biya diyya sau bakwai, tilas kuwa ya ba da dukan abin da yake da shi.
32 Amma mazinaci marar hankali ne, gama hallaka kansa yake yi.
33 Zai sha dūka, a wulakanta shi, zai dawwama cikin kunya.
34 Hasalar miji mai kishi babu irinta, ramawarsa ba dama.
35 Ba zai karɓi biya ba, ba kyautar da za a yi masa wadda za ta kwantar da fushinsa.
1 Ɗana, ka tuna da abin da na faɗa, kada ka manta da abin da na ce maka ka yi.
2 Ka yi abin da na faɗa maka, za ka rayu. Ka natsu, ka bi koyarwata, ka tsare ta kamar ƙwayar idonka.
3 Kullayaumi ka riƙe koyarwata tare da kai, ka rubuta ta a zuciyarka.
4 Ka mai da hikima 'yar'uwarka, basira kuwa ta zama ƙawarka ta jikinka.
5 Za su nisanta ka da matan mutane, daga kuma mata masu maganganun alfasha.
6 Wata rana ina leƙawa ta tagar ɗakina,
7 sai na ga waɗansu samari masu yawa waɗanda ba su gogu da duniya ba, musamman sai na lura da wani dolo a cikinsu.
8 Yana tafe a kan titi kusa da kusurwar da take a zaune, yana wucewa kusa da gidanta,
9 da magariba cikin duhu.
10 Sai ta tarye shi, ta ci ado kamar karuwa, tana shirya yadda za ta yaudare shi.
11 (Ba ta jin tsoro, ba ta kuma jin kunya, ko yaushe tana ta gantali a tituna.
12 Takan tsaya tana jira a kowace kusurwa, wani lokaci a tituna, wani lokaci kuma a kasuwa.)
13 Ta rungumi saurayin, ta sumbace shi, ta dubi tsabar idonsa ta ce,
14 “Na miƙa hadayu yau, ina da nama na hadayu.
15 Shi ya sa na fito ina nemanka, ina so in gan ka, ga shi kuwa, na gan ka!
16 Na lulluɓe gadona da zannuwan lilin masu launi iri iri daga Masar.
17 Na yayyafa musu turaren mur da na aloyes da na kirfa.
18 Ka zo mu sha daɗin ƙauna, mu more dukan dare, mu yi farin ciki rungume da juna.
19 Mijina ba ya gida, ya yi tafiya mai nisa.
20 Ya tafi da kuɗi masu yawa, ba zai komo ba sai bayan mako biyu.”
21 Ta jarabce shi da kwarkwasarta, sai ya ba da kai ga daɗin bakinta.
22 Nan da nan ya bi ta kamar sā zuwa mayanka, kamar barewa tana tsalle zuwa cikin tarko,
23 inda kibiya za ta soke zuciyarta. Yana kama da tsuntsun da yake zuwa cikin tarko, bai kuwa sani ransa yana cikin hatsari ba.
24 Yanzu fa 'ya'yana, ku kasa kunne gare ni, ku mai da hankali ga abin da nake faɗa.
25 Kada ku yarda irin wannan mace ta rinjayi zuciyarku, kada ku yi ta yawon nemanta.
26 Ita ce sanadin hallakar mutane da yawa, ta sa mutane da yawa mutuwa, har ba su ƙidayuwa.
27 Tafiya gidanta kuna kan hanya zuwa mutuwa ke nan, gajeruwar hanya ce zuwa lahira.
1 Ku kasa kunne! Hikima tana kira. Tana so a ji ta.
2 Tana tsaye bisa kan tuddai a bakin hanya Da a mararraban hanyoyi.
3 A ƙofofin shiga birni, tana kira,
4 “Ina roƙonku, ya ku, 'yan adam, Ina kiran kowane mutum da yake a duniya.
5 Ba ku balaga ba? To, ku balaga. Ku wawaye ne? Ku koyi hankali.
6 Ku kasa kunne ga jawabina mafi kyau, Dukan abin da na faɗa muku daidai ne.
7 Abin da na faɗa gaskiya ne, Ƙarairayi abin ƙi ne a gare ni.
8 Kowane abu da na faɗa gaskiya ne, Ba wani abu da yake na laifi ko na ruɗawa.
9 Ga mutum mai basira, dukan abu ne a sarari, Ga wanda aka sanar da shi sosai, abu ne a sawwaƙe.
10 Ka zaɓi koyarwata fiye da azurfa, Ka zaɓi ilimi fiye da zinariya tsantsa.
11 “Ni ce hikima, na fi lu'ulu'ai, Cikin dukan abin da kake so, ba kamata.
12 Ni ce hikima, ina da basira, Ina da ilimi da faɗar daidai.
13 Ƙin mugunta shi ne tsoron Ubangiji, Na ƙi girmankai, da fāriya, da mugayen hanyoyi, Da maganganu na ƙarya.
14 Nakan shirya abin da zan yi, in kuwa yi shi. Ina da fahimi, ina da ƙarfi.
15 Nakan taimaki sarakuna su yi mulki, Mahukunta kuma su tsara dokoki masu kyau.
16 Kowane mai mulki a duniya, da taimakona yake mulki, Ƙusoshin hukumomi da dattawan gari duka ɗaya.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, Dukan wanda yake nemana kuma zai same ni.
18 Ina da dukiya da daraja da zan bayar, Da wadata da nasara kuma.
19 Abin da za ka samu daga gare ni Ya fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa.
20 A kan hanyar adalci nake tafiya, Rankai a kan hanyoyin gaskiya.
21 Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata, Ina kuma cika gidajensu da wadata.
22 “Ni ce halittar farko da Ubangiji Ya fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.
23 Da farkon farawa ni aka fara halittawa Kafin a yi duniya.
24 Ni aka fara yi kafin tekuna, A sa'ad da ba maɓuɓɓugan ruwa.
25 Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu, Kafin a kafa tuddai a wurarensu,
26 Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta, Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa.
27 A can nake sa'ad da ya shata sararin sama, Da sa'ad da ya shimfiɗa al'arshi a hayin tekuna,
28 Da sa'ad da ya sa gizagizai a sararin sama, Ya buɗe maɓuɓɓugan teku,
29 Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa. Ina can sa'ad da ya kafa harsashin ginin duniya.
30 Ina kusa da shi kamar mai tsara fasalin gini, Ni ce abar murnarsa kowace rana, A ko yaushe ina farin ciki a gabansa.
31 Ina farin ciki da duniya, Ina murna da 'yan adam.
32 “Yanzu ku matasa, ku kasa kunne gare ni, Ku yi abin da na ce, za ku yi farin ciki.
33 Ku saurari abin da aka koya muku, Ku zama masu hikima, kada ku yi sakaci da ita.
34 Mutumin da ya kasa kunne gare ni, zai yi farin ciki haka nan, Wato yakan tsaya a ƙofata ko yaushe, Yana kuma jira a ƙofar shiga gidana.
35 Mutumin da ya same ni ya sami rai, Ubangiji zai ji daɗinsa.
36 Mutumin da bai same ni ba ya cuci kansa, Duk wanda yake ƙina mutuwa yake ƙauna.”
1 Hikima ta gina gidanta, ta yi masa ginshiƙai bakwai.
2 Ta sa an yanka dabba don biki, ta gauraya ruwan inabi da kayan yaji, ta shirya tebur.
3 Ta aiki barorinta 'yan mata su je su hau wuri mafi tsayi a birni su yi kira.
4 “Ku shigo, ku jahilai!” Ga dolo kuwa ta ce,
5 “Zo ka ci abincina ka sha ruwan inabin da na gauraya.
6 Ka rabu da ƙungiyar jahilai, ka rayu, ka bi hanyar ilimi.”
7 Idan ka kwaɓi mai fāriya, za ka gamu da cin mutunci, idan ka tsauta wa mugu, kai ne za ka cutu.
8 Faufau kada ka kuskura ka kwaɓi mai fāriya, zai ƙi ka saboda wannan, amma idan ka kwaɓi mai hikima zai girmama ka.
9 Dukan abin da ka faɗa wa mutum mai hikima, zai ƙara masa hikima. Dukan abin da ka faɗa wa adali zai ƙara masa ilimi.
10 Domin ka zama mai hikima dole ka fara da tsoron Ubangiji. Idan ka san Mai Tsarki, ka sami ganewa.
11 Hikima za ta ƙara shekarunka.
12 Kai ne da riba in ka sami hikima. Kai za ka sha hasara in ka ƙi ta.
13 Wawanci kamar mace ce mai kwakwazo, jahila, marar kunya.
14 Takan zauna a ƙofar gidanta, ko a wurin da ya fi duka bisa a cikin gari.
15 Takan yi ta kiran masu wucewa waɗanda hankalinsu yake a kan ayyukansu, ta ce,
16 “Ku shigo, ku jahilai!” Takan ce wa dolo,
17 “Ruwan da aka sata ya fi daɗi, haka nan kuma abincin da ake satar ya fi daɗi.”
18 Waɗanda suka fāɗa a hannunta ba su sani mutuwa za su yi ba, waɗanda suka riga sun shiga kuwa suna can sun nutse cikin lahira.
1 Karin maganar Sulemanu ke nan. Ɗa mai hikima abin fāriya ne ga mahaifinsa, amma wawa yakan jawo wa mahaifiyarsa baƙin ciki.
2 Abin da ka samu ta hanyar zamba ba zai yi albarka ba, amma gaskiya za ta cece ka.
3 Ubangiji ba zai bar mutumin kirki da yunwa ba, amma zai hana mugu ya kai ga biyan bukatarsa.
4 Ragwanci zai sa talauci, amma yin aiki sosai zai arzuta ka.
5 Mutum mai hankali yakan tattara amfanin gona da kaka, amma abin kunya ne a yi barci a lokacin girbi.
6 Mutumin kirki yakan karɓi albarka, maganganun mugun kuwa sukan ɓoye mugun halinsa.
7 Tunawa da mutumin kirki albarka ce, amma nan da nan za a manta da mugaye.
8 Mutane masu hankali sukan bi shawarar kirki, masu maganar wauta kuwa za su lalace.
9 Amintaccen mutum zai zauna lafiya ba abin da zai same shi, amma marasa aminci za a kama su.
10 Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, amma wanda ya bayyana gaskiya zai kawo salama.
11 Kalmomin mutumin kirki maɓuɓɓugan rai ne, amma kalmar mugun takan ɓoye makircinsa.
12 Ƙiyayya takan haddasa wahala, amma ƙauna takan ƙyale dukan laifofi.
13 Mutane masu fasaha sukan yi magana mai ma'ana, amma wawaye suna bukatar horo.
14 Mutane masu hikima sukan nemi ilimi iyakar iyawarsu, amma sa'ad da wawa ya yi magana, wahala tana kusa.
15 Wadata takan kiyaye attajiri, amma tsiya takan hallaka matalauci.
16 Sakayyar da za a yi wa mutumin kirki ta rai ce, amma zunubi yakan sa a ƙara yin wani zunubi.
17 Mutumin da yake kasa kunne sa'ad da ake kwaɓarsa zai rayu, amma duk wanda bai yarda da kuskurensa ba yana cikin hatsari.
18 Mutumin da yake faɗar ƙarairayi maƙiyi ne, dukan wanda yake baza jitajita wawa ne.
19 Bisa ga yawan surutunka, mai yiwuwa ne ƙwarai ka yi zunubi, amma idan kai mai la'akari ne, sai ka yi shiru.
20 Kalmomin mutumin kirki suna kama da azurfa tsantsa, amma shawarwarin mugu ba su da wani amfani.
21 Kalmomin mutumin kirki za su amfani mutane da yawa, amma kana iya hallaka kanka da wauta.
22 Albarkar Ubangiji takan arzuta mutum, amma yawan aiki ba shi yake kawo arziki ba.
23 Wawa ne yake jin daɗin aikata mugunta, amma mai fasaha yana jin daɗin hikima.
24 Abin da mugun yake tsoro, shi yakan auko masa, amma adali yakan sami biyan bukatarsa.
25 Hadiri yakan taso ya wargaza mugaye, amma amintattu lafiya lau suke a ko yaushe.
26 Sam, kada ka sa malalaci ya yi maka wani abu, zai sa ka ka yi fushi, idanunka su cika da hawaye mai zafi.
27 Ka yi tsoron Ubangiji za ka rayu, ka yi tsawon rai, amma mugaye sukan mutu tun kwanansu bai ƙare ba.
28 Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.
29 Ubangiji yana kiyaye marasa laifi, amma yakan hallaka masu mugunta.
30 Kullayaumi adalai sukan yi zamansu lafiya, amma mugaye ba za su zauna a ƙasar ba.
31 Maganar adalai ta hikima ce, amma harshen da yake hurta mugunta, za a dakatar da shi.
32 Adalai sun san irin maganar da ta cancanta su faɗa, amma mugaye, kullum sukan faɗi maganar da za ta cutar.
1 Ubangiji yana ƙin masu yin awo da ma'aunin zamba, amma yana farin ciki da masu yin awo da ma'auni na gaskiya.
2 Masu girmankai za a kunyatar da su nan da nan. Hikima ce mutum ya zama mai kamewa.
3 Mutanen kirki su ne gaskiya takan bi da su. Rashin aminci kuwa yana hallaka maciya amana.
4 Dukiya ba ta da wani amfani a ranar mutuwa, amma adalci zai hana ka mutuwa.
5 Gaskiya takan sa zaman mutanen kirki ya zama a sawwaƙe, amma mugun mutum shi yake kā da kansa da kansa.
6 Adalci yakan ceci amintaccen mutum, amma marar aminci, haɗamarsa ce take zamar masa tarko.
7 Mugun mutum yakan mutu da burinsa. Dogara ga dukiya bai amfana kome ba.
8 Akan kiyaye adali daga wahala, amma takan auko wa mugu.
9 Mutane sukan sha hasara ta wurin maganar marasa tsoron Allah, amma hikimar adalai takan yi ceto.
10 Birni yakan yi farin ciki saboda wadatar mutanen kirki, akwai kuma sowa ta farin ciki sa'ad da mugaye suka mutu.
11 Biranen da adalai suke cikinsu sukan ƙasaita, amma maganganun mugaye sukan hallakar da su.
12 Wauta ce a yi wa waɗansu maganar raini, amma mutum mai la'akari yakan kame bakinsa.
13 Ba wanda zai yarda ya faɗi asirinsa ga matsegunci, amma za ka amince wa amintaccen mutum.
14 Al'ummar da ba ta da masu ja mata gora, za ta fāɗi. Yawan mashawarta yake kawo zaman lafiya.
15 Wanda ya ɗaukar wa baƙo lamuni zai yi da na sani, zai fi maka sauƙi idan ba ruwanka.
16 Mace mai mutunci abar girmamawa ce, amma azzalumai za su sami dukiya.
17 In ka yi alheri, kanka ka samar wa tagomashi, in kuwa ka yi mugunta, kanka ka cutar.
18 A ainihi mugaye ba su cin ribar kome, amma idan ka yi abin da yake daidai, ka tabbata za a sāka maka da alheri.
19 Mutumin da ya yi niyyar aikata abin da yake daidai zai rayu, amma mutumin da ya dukufa ga aikata mugunta zai mutu.
20 Ubangiji yana ƙin masu muguwar niyya, amma yana murna da waɗanda suke aikata abin da yake daidai!
21 Ka tabbata fa za a hukunta mugaye, amma ba za a hukunta adalai ba.
22 Kome kyan mace idan ba ta da kangado, tana kamar zoben zinariya a hancin alade.
23 Abin da mutanen kirki suke so kullum yakan jawo alheri, idan mugaye sun sami biyan bukatarsu kowa zai yi ɓacin rai.
24 Waɗansu mutane sukan kashe kuɗinsu hannu sake, duk da haka arzikinsu sai ƙaruwa yake yi. Waɗansu kuwa saboda yawan tsumulmularsu sukan talauce.
25 Ka yi alheri za ka arzuta. Ka taimaki waɗansu, su kuma za su taimake ka.
26 Mutane sukan la'anci mai ɓoye hatsi, yana jira ya yi tsada, amma sukan yabi wanda yake sayar da nasa.
27 Idan nufe-nufenka na kirki ne za a girmama ka, amma idan kai mai neman tashin hankali ne, to, abin da zai same ka ke nan.
28 Adalai za su arzuta, kamar ganyaye da bazara, amma waɗanda suke dogara ga dukiyarsu za su karkaɗe kamar ganyaye da kaka.
29 Mutumin da yake jawo wa iyalinsa wahala, ƙarshensa talaucewa. Wawaye za su zama barorin masu hikima a ko yaushe.
30 Adalci yana rayar da mutum, wanda yake da hikima kuma yakan ceci rayuka.
31 Idan an sāka wa mutumin kirki da alheri a duniya, hakika za a hukunta wa mugaye da masu zunubi.
1 Mutumin da yake ƙaunar ilimi yakan so a faɗa masa kuskurensa, wauta ce mutum ya ƙi yarda a faɗa masa laifinsa.
2 Ubangiji yana murna da mutanen kirki, amma yakan hukunta masu shirya mugunta.
3 Mugunta ba ta kawo zaman lafiya, amma adalai sukan tsaya daram.
4 Matar kirki abar fāriya ce, abar murna ga mijinta, amma idan ta sa shi kunya, ta zama masa kamar ciwo a ƙashinsa.
5 Amintattun mutane za su yi maka abin da yake daidai, amma mugaye za su ruɗe ka.
6 Maganganun mugaye na kisankai ne, amma kalmomin adalai sukan ceci waɗanda ake neman ransu.
7 Mugaye sukan gamu da faɗuwarsu, ba magāda, amma iyalan adalai sukan dawwama.
8 Idan kai haziƙi ne, za a yabe ka, amma idan kai dakiki ne, mutane za su raina ka.
9 Gara kana talakanka, kana neman abinci, da ka mai da kanka kai wani abu ne, alhali kuwa abin da za ka ci ya fi ƙarfinka.
10 Mutumin kirki yakan lura da dabbobinsa, amma mugaye sukan yi wa nasu ƙeta.
11 Manomin da yake aiki ƙwarai yana da isasshen abinci. Wauta ce a ɓatar da lokaci a kan aikin banza.
12 Iyakar abin da mugaye suke so, shi ne su sami muguntar da za su yi, amma adalai suna tsaye daram.
13 Maganganun mugun sukan zamar masa tarko, amma amintacce yakan fid da kansa daga cikin wahala.
14 Sakayyar mutum ta rataya ne a kan maganarsa da aikinsa, zai sami abin da ya cancance shi.
15 Wawa a kullum tsammani yake abin da yake yi daidai ne, amma masu hikima sukan kasa kunne ga shawara.
16 Sa'ad da wawa ya hasala, nan da nan kowa zai sani, amma mai la'akari ba zai nuna ya kula ba.
17 Sa'ad da ka faɗi gaskiya, ka yi adalci, amma ƙarairayi su ne jagorar aikata rashin adalci.
18 Maganganun rashin tunani suke sa rauni mai zurfi kamar saran takobi, amma kalmomin mai hikima sukan warkar da raunuka.
19 Gaskiya dawwamammiya ce, amma ƙarya ƙurarriya ce.
20 Waɗanda suke shawarta mugunta za a auka musu farat ɗaya, amma waɗanda suke aikata alheri za su yi farin ciki.
21 Ba wani mugun abu da zai sami adali, amma mugaye ba za su sami kome ba, sai wahala.
22 Ubangiji yana ƙin maƙaryata, amma yana murna da masu faɗa da cikawa.
23 Mai la'akari zai bar wa cikinsa abin da ya sani, amma wawaye sukan yi ta tallar wautarsu.
24 Mutum mai mai da hankali ga aikinsa zai sami iko, amma ragwanci zai sa mutum ya zama bawa.
25 Damuwa takan hana wa mutum farin ciki, amma kalmomin alheri za su sa shi ya yi murna.
26 A ko yaushe adalin mutum yakan gwada halinsa, amma mugaye sukan ɓata a hanya.
27 Rago ba zai kai ga biyan bukatarsa ba, amma mai ƙwazo zai sami dukiya.
28 Adalci hanyar rai ne, amma wauta hanyar mutuwa ce.
1 Ɗa mai hikima yakan mai da hankali sa'ad da mahaifinsa yake kwaɓarsa, amma mutum mai girmankai ba ya yarda da kuskurensa.
2 Mutanen kirki za a sāka musu da alheri a kan abin da suke faɗa, amma mayaudara sukan ƙosa su ta da zaune tsaye.
3 Ka lura da irin abin da kake faɗa don ka kiyaye ranka. Mutumin da bai kula da maganarsa ba, yakan hallakar da kansa.
4 Rago yakan ƙosa ya sami wani abu ainun, amma sam, ba zai samu ba. Mai mai da hankali ga aikinsa zai sami kowane abu da yake bukata.
5 Masu aminci suna ƙin ƙarairayi, amma maganganun mugun abin kunya ne da ƙasƙanci.
6 Adalci yakan kiyaye marasa laifi, amma mugunta ita ce fāɗuwar masu zunubi.
7 Waɗansu mutane sukan nuna su attajirai ne, alhali kuwa ba su da kome. Waɗansu kuma sukan nuna su matalauta ne, alhali kuwa suna da dukiya.
8 Kuɗin attajiri suna iya ceton ransa, bai kyautu ba a razana matalauci.
9 Adalai suna kama da haske mai haskakawa ƙwarai, mugaye kuwa suna kamar fitilar da take mutuwa.
10 Fāriya ba ta kawo kome sai wahala. Hikima ce a nemi shawara.
11 Dukiyar da aka same ta a sawwaƙe, za ka rasa ta da sauri, amma wanda ya same ta da wahala, za ta yi ta ƙaruwa.
12 Idan ba bege, sai zuciya ta karai, amma muradin da ya tabbata zai cika ka da sa zuciya.
13 Idan ka ƙi shawara mai kyau wahala kake nemar wa kanka, idan ka bi ta kuwa za ka zauna lafiya.
14 Koyarwar masu hikima maɓuɓɓugar rai ce, za ta taimake ka ka kuɓuta sa'ad da ranka yake cikin hatsari.
15 Basira takan sa a girmama ka, amma mutanen da ba za a iya amincewa da su ba, a kan hanyar hallaka suke.
16 Mutum mai hankali a ko yaushe yakan yi tunani kafin ya aikata, amma wawa yakan tallata jahilcinsa.
17 Manzanni marasa aminci sukan haddasa wahala, amma waɗanda suke amintattu sukan kawo salama.
18 Mutumin da ba zai koya ba, zai talauce ya sha kunya, amma wanda ya kasa kunne ga tsautawa za a girmama shi.
19 Abu mai kyau ne mutum ya sami biyan bukatarsa! Wawaye sukan ƙi barin mugunta.
20 Ka koya daga wurin masu hikima, za ka zama mai hikima. Yi abuta da wawaye, za ka kuwa lalace.
21 Wahala tana bin masu zunubi ko'ina, amma za a sāka wa adalai da kyawawan abubuwa.
22 Mutumin kirki zai sami dukiya, har ya bar wa jikokinsa, amma dukiyar masu zunubi za ta zama ta adalai.
23 Saurukan da ba a aikatawa, za su ba da isasshen abinci ga matalauci, amma mutane marasa gaskiya sukan hana albarka.
24 Idan ba ka horon ɗanka, ba ka ƙaunarsa ke nan, amma idan kana ƙaunarsa za ka riƙa kwaɓarsa.
25 Adalai suna da isasshen abinci, amma mugaye fama suke da yunwa ko yaushe.
1 Hikimar mata takan gina gidaje, amma wauta takan rushe su.
2 Ka yi gaskiya, za ka nuna girmamawarka ga Ubangiji, amma idan ka yi rashin gaskiya, ka nuna rashin girmamawa ke nan ga Ubangiji.
3 Kalmomin mai hikima za su kiyaye shi, amma maganganun wawa za su jawo masa hukunci.
4 Idan ba ka da shanun noma ba za ka sami hatsi mai yawa ba, amma idan kana da su za ka sami hatsi mai yawan gaske.
5 Amintaccen mashaidi a ko yaushe yana faɗar gaskiya, amma marar aminci ba ya faɗar kome, sai ƙarairayi.
6 Mutum mai fāriya ba zai taɓa zama mai hikima ba sam, amma mutum mai basira yakan koya a sawwaƙe.
7 Ka nisanci wawaye, gama ba su da abin da za su koya maka.
8 Me ya sa haziƙi yake da hikima? Domin ya san abin da zai yi. Me ya sa dakiki yake wauta? Domin yana ganin kansa masani ne.
9 Idan wawaye sun yi zunubi ba sukan kula ba, amma mutanen kirki sukan nemi gafara.
10 Ɓacin ranka naka ne, murnarka kuwa ba za ka raba da wani ba.
11 Gidan mutumin kirki ba zai rushe ba bayan da an lalatar da gidan mugun mutum.
12 Hanyar da kake tsammani ita ce daidai, za ta kai ka ga hallaka.
13 Dariyar mutum takan ɓoye baƙin cikinsa. Sa'ad da murna ta tafi, ko yaushe baƙin ciki yana nan.
14 Mugu zai sami abin da ya cancance shi, mutumin kirki kuma zai sami sakayyar ayyukansa.
15 Wawa yakan gaskata kowane abu, amma mai la'akari yana lura da takawarsa.
16 Mutum mai hankali yana lura don ya kauce wa wahala, amma wawa rashin kula gare shi, yakan aikata kome da gaggawa.
17 Mutum mai zafin rai yakan yi aikin wauta, mai mugayen dabaru kuma abin ƙi ne.
18 Jahilai sukan sami abin da ya cancanci wautarsu, amma ilimi shi ne sakamakon masu azanci.
19 Tilas mugaye su rusuna wa adalai, su roƙe su tagomashi da tawali'u.
20 Ba wanda yake son matalauci, amma attajiri yana da abokai da yawa.
21 Idan kana so ka zama mai farin ciki, sai ka nuna alheri ga matalauci. Zunubi ne ka raina kowane mutum.
22 Waɗansu za su amince da kai, su girmama ka, idan ka aikata nagarta, idan kuwa ka aikata mugunta, to, ka yi babban kuskure.
23 Idan ka yi aiki za ka sami abin masarufi, idan kuwa ka zauna kana ta surutu kawai za ka zama matalauci.
24 Mutane masu hikima za a sāka musu da wadata, amma za a san wawa ta wurin wautarsa.
25 Sa'ad da mashaidi ya faɗi gaskiya zai ceci rayuka, amma maƙaryacin mashaidi yakan ci amanar mutane sa'ad da ya faɗi ƙarairayi.
26 Tsoron Ubangiji yakan ba da tabbatarwa, da zaman lafiya ga mutum da iyalinsa.
27 Kana so ka kauce wa mutuwa? To, tsoron Ubangiji shi ne maɓuɓɓugar rai.
28 Darajar sarki ta dogara ga irin yawan mutane da ya mallaka, idan ba su, shi ba kome ba ne.
29 Mutum mai kamewa yana da hikima, amma mai zafin rai yana bayyana wautarsa a fili.
30 Kwanciyar rai lafiya ce ga jiki, amma kishi yana kama da ciwon da yake cin ƙashi.
31 Wanda ya zalunci matalauci ya zargi Mahaliccinsa ke nan, amma nuna alheri ga matalauci yin sujada ne.
32 Muguntar mugun takan kawo hallakarsa, amma adalin mutum, an kiyaye shi ta wurin dattakonsa.
33 Hikima tana cikin kowane tunani na haziƙi, wawa bai san kome game da hikima ba.
34 Adalci yakan ɗaukaka al'umma, amma zunubi yakan kunyatar da al'umma.
35 Sarakuna suna jin daɗin ƙwararrun 'yan majalisarsu, amma sukan hukunta waɗanda suka ba su kunya.
1 Amsa magana da tattausan harshe takan kwantar da hasala, amma magana da kakkausan harshe takan kuta fushi.
2 Sa'ad da mai hikima ya yi magana yakan sa ilimi ya yi bansha'awa, amma wawaye sukan yi ta sheƙa rashin hankali.
3 Ubangiji yana ganin abin da yake faruwa a ko'ina, yana lura da mu, ko muna aikata alheri ko mugunta.
4 Kalmomin alheri suna kawo rai, amma maganganun ƙiyayya suna karya zuciyar mutum.
5 Wauta ce mutum ya ƙi kulawa da abin da mahaifinsa ya koya masa, amma hikima ce idan ka karɓi tsautawarsa.
6 Adalai suna adana dukiyarsu, amma mugaye sukan rasa tasu dukiya sa'ad da wahala ta zo.
7 Mutane masu hikima suke yaɗa ilimi, amma banda wawaye.
8 Ubangiji yana murna sa'ad da adalai suke yin addu'a, amma yana ƙin hadayun da mugaye suke miƙa masa.
9 Ubangiji yana ƙin hanyoyin mugaye, amma yana ƙaunar mutumin da yake yin abin da yake daidai.
10 Idan ka yi abin da ba daidai ba, za ka sha hukunci sosai, za ka mutu idan ka ƙi yarda da tsautawa.
11 Ko lahira ba za ta hana Ubangiji ya san abin da yake can ba. Ƙaƙa fa mutum zai iya ɓoye wa Allah tunaninsa?
12 Mai girmankai ba ya so a tsauta masa. Faufau ba zai nemi shawara a wurin masu hikima ba.
13 Sa'ad da mutum yake murna yakan yi murmushi, amma sa'ad da yake baƙin ciki yakan yi nadama.
14 Mutum mai basira yana neman ilimi, amma dakikai, jahilcinsu ya wadace su.
15 Wahaltaccen mutum a ko yaushe, fama yake yi a zamansa, amma masu farin ciki suna zama da daɗin rai.
16 Gara a zauna da talauci da tsoron Ubangiji, da a sami dukiya game da wahala.
17 Gara cin mabunƙusa tare da waɗanda kake ƙauna, da ka ci abinci mai romo a inda ƙiyayya take.
18 Zafin rai yakan kawo jayayya, amma haƙuri yana kawo salama.
19 Idan kai rago ne za ka gamu da wahala a ko'ina, amma idan kai amintacce ne, ba za ka sha wahala ba.
20 Ɗa mai hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa, amma wawa yana raina mahaifiyarsa.
21 Dakikai suna murna da wautarsu, amma mai hikima zai aikata abin da yake daidai.
22 Ka nemi dukan shawarwarin da ka iya ka samu, za ka yi nasara, idan ba tare da shawara ba, za ka fāɗi.
23 Me ya fi wannan zama abin murna? Mutum ya sami maganar da take daidai a lokacin da ya dace!
24 Mutum mai hikima yakan kama hanya ya haura zuwa rai, ba ya bin hanyar da ta gangara zuwa mutuwa.
25 Ubangiji zai rushe gidajen masu girmankai, amma zai kiyaye dukiyar gwauruwa, wato mata wadda mijinta ya mutu.
26 Ubangiji yana ƙin tunanin mugaye, amma yana murna da kalmomi masu daɗi.
27 Mai ƙoƙarin cin ƙazamar riba yana jefa iyalinsa a wahala ke nan. Kada ka karɓi hanci, za ka yi tsawon rai.
28 Mutanen kirki sukan yi tunani kafin su ba da amsa. Mugaye suna da saurin ba da amsa, amma takan jawo wahala.
29 Sa'ad da mutanen kirki sukan yi addu'a, Ubangiji yakan kasa kunne, amma ba ya kulawa da mugaye.
30 Fuska mai fara'a takan sa ka yi murna, labari mai daɗi kuma yakan sa ka ji daɗi.
31 Idan ka mai da hakali sa'ad da ake tsauta maka kai mai hikima ne.
32 Idan ka ƙi koyo kana cutar kanka, idan ka karɓi tsautawa za ka zama mai hikima.
33 Tsoron Ubangiji koyarwa ce domin samun hikima. Sai ka zama mai tawali'u kafin ka sami girmamawa.
1 Mutane sun iya yin shirye-shiryensu, amma cikawa ta Ubangiji ce.
2 Za ka yi tsammani kowane abu da ka yi daidai ne, amma Ubangiji yana auna manufarka.
3 Ka roƙi Ubangiji, ya sa albarka ga shirye-shiryenka, za ka kuwa yi nasara cikin aikata su.
4 Kowane abu da Ubangiji ya yi yana da makoma, makomar mugun kuwa hallaka ce.
5 Ubangiji yana ƙin kowane mutum da yake fariya. Irin wannan mutum ba zai kuɓuta daga hukunci ba.
6 Ka zama mai biyayya da aminci, Allah kuwa zai gafarta maka zunubinka. Ka dogara ga Ubangiji, ba wani mugun abu da zai same ka.
7 Lokacin da ka yi abin da Ubangiji yake so, ka iya mai da maƙiyanka su zama abokai.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar gaskiya, da ka tara abu mai yawa ta hanyar zamba.
9 Kana iya yin shirye-shiryenka, amma Allah ne yake bi da kai cikin ayyukanka.
10 Sarkin da yakan yi magana ta wurin ikon Allah, a ko yaushe yakan yanke shawarar da yake daidai.
11 Ubangiji yana son ma'aunai su zama na gaskiya, kowane abin sayarwa kuma ya zama daidai.
12 Sarakuna ba za su iya jurewa da mugunta ba, gama adalci yake sa hukuma ta yi ƙarfi.
13 Sarki yana so ya ji gaskiya, zai kuwa ƙaunaci mutanen da suke faɗar gaskiya.
14 Mutum mai hikima yakan yi ƙoƙari ya faranta zuciyar sarki. Idan kuwa sarki ya hasala mai yiwuwa ne a kashe wani.
15 Alherin sarki kamar gizagizai ne masu kawo ruwan sama a lokacin bazara, akwai rai a ciki.
16 Yana da kyau, ya kuma fi kyau a sami hikima da ilimi fiye da zinariya da azurfa.
17 Mutumin kirki yana tafiya a hanyar da ta kauce wa mugunta, saboda haka ka kula da inda kake tafiya, za ta ceci ranka.
18 Girmankai jagora ne zuwa ga hallaka, fāriya kuwa zuwa ga fāɗuwa.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu tawali'u, da ka zama ɗaya daga cikin masu girmankai, har da za ka sami rabo daga cikin ganimarsu.
20 Ka mai da hankali ga abin da aka koya maka, za ka yi nasara. Ka dogara ga Ubangiji, za ka yi farin ciki.
21 Mutum mai hikima, wanda ya isa mutum, akan san shi ta wurin haziƙancinsa, kamar yadda kalmominsa suke da daɗi, haka ma rinjayarsa take.
22 Hikima maɓuɓɓugar rai ce ga mai hikima, amma ɓata lokaci ne a yi ƙoƙarin koya wa dakikai.
23 Mai hikima yakan yi tunani kafin ya yi magana, abin da ya faɗa yakan yi rinjaye ƙwarai.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da zuma, suna da daɗin ɗanɗana, suna kuma da amfani domin lafiyarka.
25 Hanyar da kake tsammani ita ce daidai, za ta kai ka ga hallaka.
26 Marmarin cin abinci yakan sa ɗan ƙodago ya yi aiki da ƙwazo, domin yana so ya ci ya ƙoshi.
27 Mutumin da yake jin daɗin yin mugunta yakan tafi yawon nemanta, mugayen maganganunsa ƙuna suke kamar wuta.
28 Mugaye sukan baza jita-jita, suna zuga tashin hankali, suna raba aminai.
29 Mutum mai ta da zaune tsaye yakan ruɗi abokansa, ya kai su ga bala'i.
30 Ka kula da mutane masu murguɗa baki suna kaɗa gira a kanka, sun yi tunanin wani mugun abu ke nan.
31 Furfurar tsufa rawanin daraja ce, sakamako ne ga ran mai adalci.
32 Ya fi kyau ka zama mai haƙuri da ka zama mai ƙarfi. Ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
33 Mutane sukan jefa kuri'a don su san nufin Allah, amma Allah da kansa ne yake ba da amsa.
1 Gara a ci ƙanzo da rai a kwance, da gida cike da liyafa, amma cike da tashin hankali.
2 Bara mai wayo yakan sami iko a kan shashashan ɗan maigidansa, har ya sami rabo a cikin gādon.
3 Zinariya da azurfa da wuta ake gwada su, zuciyar ɗan adam kuwa Ubangiji ne yake gwada ta.
4 Mugaye sukan kasa kunne ga mugayen dabaru, maƙaryata kuma sukan kasa kunne ga ƙarairayi.
5 Wanda ya yi wa matalauci ba'a, Mahaliccinsa yake yi wa zargi. Idan kana murna da hasarar wani, za a hukunta ka.
6 Tsofaffi suna fāriya da jikokinsu, kamar yadda samari suke alfarma da iyayensu maza.
7 Mutumin da yake kamili ba ya faɗar ƙarya, haka ma wawa ba zai faɗi wani abin kirki ba.
8 Waɗansu mutane suna tsammani cin rashawa yakan yi aiki kamar sihiri, sun gaskata zai iya yin kome.
9 Idan kana so mutane su so ka, ka riƙa yafe musu sa'ad da suka yi maka laifi. Mita takan raba abuta.
10 Mutum mai fasaha yakan koyi abu da yawa daga tsautawa ɗaya, fiye da abin da wawa zai koya ko da an dūke shi sau ɗari.
11 Mutuwa za ta zo wa mugaye kamar mugun manzo wanda a ko yaushe yana so ya kuta tashin hankali.
12 Gara mutum ya gamu da beyar ta mata wadda aka kwashe mata kwiyakwiyanta, da ka gamu da waɗansu wawaye suna aikin dakikancinsu.
13 Idan ka sāka alheri da mugunta, ba za ka iya raba gidanka da mugunta ba, faufau.
14 Mafarin jayayya kamar ɓarkewa madatsar ruwa ne, sai a tsai da ita tun ba ta haɓaka ba.
15 Da wanda ya baratar da mugun da wanda ya kā da adali, duk abin ƙi suke ga Ubangiji.
16 Kashe kuɗi saboda ilimi ba shi da amfanin kome ga wawa, domin ba shi da tunani.
17 A ko yaushe abokai sukan nuna ƙaunarsu, 'yan'uwa kuma, ai, don su ɗauki nawayar juna suke.
18 Sai mutum marar tunani ne kaɗai zai ɗauki lamunin basusuwan maƙwabcinsa.
19 Shi wanda yake son zunubi, yana son wahala ke nan, wanda kuma yake yin fāriya a dukan lokaci yana neman tashin hankali ke nan.
20 Mutumin da yakan yi tunanin mugunta, ya kuma hurta ta, kada ya sa zuciya ga samun abin kirki, sai dai bala'i kaɗai.
21 Mahaifi wanda ɗansa yake yin abubuwan wauta, ba shi da kome sai ɓacin rai da baƙin ciki.
22 Kasancewa da murna yakan ba ka lafiya. Zama da baƙin rai dukan lokaci mutuwar tsaye ce.
23 Alƙalai marasa gaskiya suna cin hanci a ɓoye, sa'an nan ba za su aikata adalci ba.
24 Baligi da hikima yake aikinsa, amma wanda bai balaga ba, bai san abin da zai yi ba.
25 Wawan da yakan jawo wa mahaifinsa ɓacin rai, abin baƙin ciki yake ga mahaifiyarsa.
26 Ba daidai ba ne a ci marar laifi tara, yi wa mutumin kirki bulala kuwa rashin adalci ne.
27 Mutumin da ya tabbata yana da gaskiya ba zai cika yawan magana ba, natsattsen mutum yana da basira ƙwarai.
28 Banda haka ma, ko wawa in bai buɗe bakinsa ba, za a zaci shi mai hikima ne, mai basira.
1 Mutumin da ya kula da kansa kaɗai ba ya jituwa da kowa, ko wani ya faɗi maganar da take daidai ba zai yarda ba.
2 Wawa bai kula ba, ko ya fahimci abu, ko bai fahimta ba. Abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya nuna kuzarinsa.
3 Zunubi da kunya a tattare suke. Idan ka yar da mutuncinka za ka sha ba'a a maimakonsa.
4 Harshen ɗan adam yana iya zama shi ne asalin hikima mai zurfi kamar teku, sabo kamar ruwan rafi mai gudu.
5 Ba daidai ba ne a yi wa mugun mutum alheri, sa'an nan a ƙi yi wa marar laifi adalci.
6 Sa'ad da wawa ya fara jayayya, yana neman dūka ne.
7 Sa'ad da wawa ya yi magana yana lalatar da kansa ne, maganarsa tarko ce, da ita ake kama shi.
8 Ɗanɗanar jita-jita daɗi gare ta, mukan ƙosa mu haɗiye ta.
9 Rago yana daidai da mutumin da yake lalatar da abubuwa.
10 Sunan Ubangiji kamar ƙaƙƙarfar hasumiya ne, inda adali yakan shiga ya zauna lafiya.
11 Attajirai suna zato dukiyarsu ita ce za ta kiyaye su kamar garuka masu tsayi da suke kewaye da birni.
12 Ba wanda za a girmama sai mai tawali'u, mutum mai girmankai kuwa yana kan hanyar hallaka.
13 Ka saurara kafin ka amsa, idan kuwa ba ka yi ba, ka zama dakiki mai bankunya.
14 Sa zuciya ga rai yakan taimaki mutum sa'ad da yake ciwo, amma idan ya karai, to, tasa ta ƙare.
15 Mutane masu basira, a ko yaushe suna da himma, a shirye kuma suke domin su koya.
16 Kana so ka sadu da babban mutum? Ka kai masa kyauta, za ka gan shi a sawwaƙe.
17 Wanda ya fara mai da magana a majalisa yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai abokin shari'arsa ya mai da tasa maganar tukuna.
18 Idan mutum biyu ƙarfafa suna jayayya da juna a gaban shari'a, kuri'a a asirce kaɗai take iya daidaita tsakaninsu.
19 Ɗan'uwan da ya ji haushinka zai gagare ka, idan ka yi faɗa da shi zai rufe maka ƙofarsa.
20 Bisa ga sakamakon hurcinka haka za ka rayu.
21 Abin da ka faɗa ya iya cetonka ko ya hallaka ka, saboda haka tilas ne ka karɓi sakamakon maganarka.
22 Idan ka sami mace ka sami abu mai kyau, wannan alheri ne wanda Ubangiji ya yi maka.
23 Matalauci yakan yi roƙo da taushi, maganar matalauci rarrashi ne, amma attajiri yakan yi magana garas.
24 Waɗansu abokai ba su sukan ɗore ba, amma waɗansu abokai sun fi 'yan'uwa aminci.
1 Gara mutum ya zama matalauci amma mai aminci, da a ce ya zama maƙaryaci, wawa.
2 Yin ɗokin da ba ilimi ba shi da amfani, rashin haƙuri kuma zai jawo maka wahala.
3 Waɗansu mutane sukan lalatar da kansu ta wurin ayyukansu na jahilci, sa'an nan su sa wa Ubangiji laifi.
4 Attajirai sukan sami sababbin abokai a ko yaushe, amma matalauta ba zu su iya riƙon 'yan kaɗan da suke da su ba.
5 Idan ka faɗi ƙarya a majalisa, za a hukunta ka, ba za ka kuɓuta ba.
6 Kowa na ƙoƙari ya sami farin jini wurin manyan mutane, kowa na so a ce shi abokin mutumin nan ne, mai yawan alheri.
7 'Yan'uwan matalauci ba su bukatarsa, ba abin mamaki ba ne ya rasa abokai. Kome ƙoƙarin da zai yi ba zai sami ko ɗaya ba.
8 Ka yi wa kanka gatanci, ka koyi dukan abin da kake iyawa, sa'an nan ka tuna da abin da ka koya, za ka arzuta.
9 Ba wanda zai faɗi ƙarya a majalisa ya rasa shan hukunci, maƙaryaci, tasa ta ƙare.
10 Ko kusa wawaye ba za su yi zaman jin daɗi ba, haka nan kuma bayi ba za su yi mulki a kan iyayengijinsu ba.
11 Mutum mai hankali yake danne fushinsa. Lokacin da wani ya cuce ka, abin kirki ne, ka yi kamar ba ka kula da shi ba.
12 Hasalar sarki kamar rurin zaki ne, amma alherinsa kamar saukar ruwan sama ne.
13 Dakikin ɗa yana jawo wa mahaifinsa lalacewa, mace mai mita tana kama da ɗiɗɗigar ruwa.
14 Mutum na iya cin gādon gida da kuɗi daga wurin iyayensa, amma Ubangiji ne kaɗai yake ba shi mace mai hankali.
15 Rago, yi ta ragwancinka ka yi ta sharar barci, amma kai za ka sha yunwa.
16 Ka kiyaye umarnai za ka rayu, in ka ƙi binsu kuwa za ka mutu.
17 Sa'ad da ka bayar ga matalauci kamar ka ba Ubangiji rance ne, gama Ubangiji zai sāka maka.
18 Ka yi wa 'ya'yanka tarbiyya tun suna ƙanana yadda za su iya koyo. Idan ba ka yi haka ba, ka taimaka wajen lalacewarsu ke nan.
19 Idan mutum mai zafin rai ne, ƙyale shi ya sha sakamakonsa. Idan ka fisshe shi daga cikin wahala sau ɗaya, sai ka sāke yi.
20 Ka saurari shawara, ka yarda ka koya, wata rana za ka zama mai hikima.
21 Mutum ya iya shirya dabaru iri iri, amma sai nufin Ubangiji ne zai tabbata.
22 Abin kunya ne mutum ya zama mai haɗama, matalauci kuma ya fi maƙaryaci.
23 Ka yi tsoron Ubangiji za ka yi tsawon rai, ka kuma sami biyan bukata, ba abin da zai cuce ka.
24 Waɗansu mutane sun cika lalaci, ko abincinsu ba su iya taunawa.
25 Za a hukunta mai fāriya saboda ya zama ishara ga mutanen da ba su san kome ba, mutum mai hikima yakan koya sa'ad da aka tsauta masa.
26 Sai marar kunya, marar mutunci suke wulakanta mahaifinsa, ko ya kori mahaifiyarsa daga gidansa.
27 Ɗana idan ka bar yin nazari za ka manta da abin da ka riga ka koya.
28 Ba gaskiya ga mashaidin da ya yi niyyar cutar wani. Mugaye suna ƙaunar yin mugunta.
29 Wawa mai fāriya hakika zai sha dūka.
1 Ruwan inabi da barasa sukan sa ka ka yi ta tā da murya, ka zama wawa. Wauta ce mutum ya bugu.
2 Ka ji tsoron fushin sarki kamar yadda za ka ji tsoron zaki mai ruri, sa shi ya yi fushi kashe kai ne.
3 Kowane wawa yakan fara yin jayayya, abin da ya fi daraja shi ne ka fita ka ware kanka.
4 Manomin da ya cika lalaci, ya kasa nome gonakinsa a kan kari, a lokacin girbi ba zai sami kome ba.
5 Tunanin mutum kamar ruwa yake a rijiya mai zurfi, sai mai basira ya iya ya jawo shi.
6 Kowa gani yake shi mai biyayya ne, mai aminci. Amma ina? Ko ka yi ƙoƙari ka sami amintacce ɗaya daga cikinsu, ba za ka samu ba.
7 'Ya'yan da mahaifinsu amintacce ne, wanda yake aikata abin da yake daidai, sun yi sa'a.
8 Sarkin da yake yin shari'a ta gaskiya, da ganin mugunta ya san ta.
9 Wane ne zai iya cewa lamirinsa garau yake, har da zai ce ya rabu da zunubinsa?
10 Allah yana ƙin masu ma'aunin algus.
11 Ayyukan da saurayi yake yi suke bayyana yadda yake, kana iya sani ko shi amintacce ne, mai nagarta.
12 Ubangiji ya ba mu ido don mu gani, ya ba mu kunne don mu ji.
13 Idan barci ne sana'arka za ka talauce. Ka yi ta aiki za ka sami wadataccen abinci.
14 Mai saye yakan yi kukan tsada a kullum, amma yakan tafi ya yi ta fāriya a kan ya iya ciniki.
15 In ka san abin da kake faɗa, kana da wani abu wanda ya fi zinariya da lu'ulu'ai tamani.
16 Sai wawa kaɗai yake ɗaukar lamunin biyan basusuwan da baƙo ya ci, ya kamata a karɓi dukiyarsa jingina.
17 Abin da ka samu ta hanyar zamba kakan ji daɗinsa kamar abinci mai kyau, amma ko ba jima ko ba daɗe zai zama kamar yashi cike da bakinka.
18 Ka nemi kyakkyawar shawara za ka yi nasara, kada ka jefa kanka cikin yaƙi ba tare da shiri ba.
19 Mai baza jita-jita ba shi da asiri, ka yi nesa da mai yawan surutu.
20 Idan ka zagi iyayenka, za ka mutu kamar fitilar da ta mutu cikin duhu.
21 Dukiyar da aka same ta a sawwaƙe, amfaninta kaɗan ne.
22 Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako.
23 Ubangiji yana ƙin waɗanda suke awo da ma'aunin algus.
24 Ubangiji ya ƙayyade hanyoyinmu, ta ƙaƙa wani zai ce ya fahimci rai?
25 Ka yi tunani a hankali kafin ka yi wa'adi za ka miƙa wa Allah wani abu, mai yiwuwa ne ka yi da na sani nan gaba.
26 Sarki mai hikima zai bincika ya gane waɗanda suke aikata mugunta, ya hukunta su ba tausayi.
27 Ubangiji ne ya ba mu hankali da lamiri, ba za mu iya ɓoye masa ba.
28 Sarki zai zauna dafa'an cikin mulkinsa muddin yana mulki da aminci, da adalci, da daidaita.
29 Ƙarfin samari abin darajantawa ne, furfurar tsofaffi abar girmamawa ce.
30 Wani lokaci sai mun sha wuya muke sāke hanyoyinmu.
1 Ubangiji ne yake mallakar tunanin sarki a sawwaƙe kamar yadda yake yi da ruwan rafi.
2 Ko da a ce dukan abin da kake yi daidai ne, ka tuna fa Ubangiji ya san manufarka.
3 Ubangiji ya fi so ka yi abin da yake daidai, mai kyau kuma, fiye da ka miƙa masa hadayu.
4 Girmankai da fāriya suke bi da mugaye, wannan kuwa zunubi ne.
5 Yin shiri a tsanaki zai kai ka ga biyan bukatarka, idan kuwa ka cika gaggawa ba za ka sami abin da zai ishe ka ba.
6 Dukiyar da aka tara ta hanyar rashin gaskiya takan ƙare nan da nan, takan kuma kai ga mutuwa.
7 Mugaye, tasu ta ƙare saboda muguntarsu, gama sun ƙi yin abin da yake daidai.
8 Mutane masu laifi sukan bi ta karkatacciyar hanya, marasa laifi kuwa suna aikata abin da yake daidai.
9 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mace mai mita.
10 Mugaye sun zaƙu su aikata mugunta, ba su yi wa kowa jinƙai.
11 Sa'ad da aka hukunta mai girmankai, ko marar tunani yakan koyi wani abu, mutum mai hikima yakan koyi abin da ake koya masa.
12 Adali ya san tunanin mugaye, yakan kuwa zama sanadin lalacewarsu.
13 Idan ka ƙi jin kukan matalauci, naka kukan da kake yi na neman taimako, ba za a ji ba.
14 Kyauta a asirce takan kwantar da zuciyar wanda yake fushi da kai.
15 Sa'ad da aka yi adalci mutanen kirki sukan yi murna, amma mugaye sukan yi baƙin ciki.
16 Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.
17 Sa kai cikin nishaɗi, wato shan ruwan inabi, da cin abinci mai tsada, ba zai bar ka ka tara dukiya ba.
18 Wahalar da mugaye suke so su jawo wa mutanen kirki, za ta koma kansu.
19 Gara ka zauna a hamada, da ka zauna tare da mace mai mita, mai yawan kai ƙara.
20 Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan.
21 Ka yi alheri ka yi aminci, za ka yi tsawon rai waɗansu kuma za su girmama ka, su yi maka abin da yake daidai.
22 Sarkin yaƙi mai wayo yakan ci birnin da jarumawa suke tsaro, ya rushe garun da suke taƙama da shi.
23 Idan ba ka so ka shiga wahala, ka lura da abin da kake faɗa.
24 Ba kalmar da ta fi “fāɗin rai” dacewa ga mutum mai girmankai, mai fāriya marar tunani.
25 Malalacin mutumin da ya ƙi yin aiki, kansa yake kashewa.
26 Duk abin da yake tunani dukan yini, shi ne a kan abin da yake so ya samu. Amma adali ko ta ƙaƙa yakan bayar da hannu sake.
27 Ubangiji yana ƙin hadayar da mugaye suka miƙa masa, tun ba wadda suka miƙa ta da mugun nufi ba.
28 Ba a gaskata shaidar maƙaryaci, amma mutumin da yakan yi tunani a kan al'amura, akan karɓi tasa.
29 Adali ya tabbatar da kansa, haka ma mugun mutum yakan yi da'awa, cewa shi ma ya tabbatar da kansa.
30 Hikima, da haziƙanci, da basira, ba kome suke ba gāba da Ubangiji.
31 Kana iya shirya dawakai don zuwa yaƙi, amma nasara ta Ubangiji ce.
1 Idan ya zama dole ne ka zaɓa tsakanin kyakkyawan suna ko dukiya, to, ka zaɓi kyakkyawan suna, tagomashi kuma ya fi azurfa da zinariya.
2 Ba bambanci tsakanin mawadaci da matalauci, gama Ubangiji ne ya halicce su duka.
3 Mutum mai hankali, in ya ga wahala tana zuwa yakan kauce mata, amma shashasha yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.
4 Kana da tsoron Ubangiji, ka yi tawali'u, za ka arzuta, ka ɗaukaka, ka sami tsawon rai.
5 Idan kana ƙaunar ranka ka nisanci tarkunan da aka kafa a hanya don su kama mugaye.
6 Ka koya wa yaro yadda zai yi zamansa, zai kuwa tuna da ita dukan kwanakinsa.
7 Matalauta su ne bayin attajirai, bawa ne kai ga wanda ka ci bashi a gare shi.
8 In ka shuka rashin gaskiya masifa ce za ta tsiro, wato hukunci mai tsanani wanda zai hallakar da kai.
9 Ka zama mai hannu sake, ka riƙa ba matalauta abincinka, za a sa maka albarka saboda haka.
10 Ka rabu da mutum mai fāriya, mai gardama, mafaɗaci, hatsaniya za ta ƙare.
11 In ka yi ladabi za ka zama aminin sarki, gama yana ƙaunar amintaccen mutum.
12 Ubangiji yana lura ya ga an riƙe gaskiya sosai ta wurin ƙin yarda da maganganun ƙarya.
13 Malalaci yakan yi zamansa a gida, yakan ce, “Zaki zai kama ni in na fita waje.”
14 Zina tarko ce, takan kama waɗannan waɗanda Ubangiji yake fushi da su.
15 Halin yara ne su yi wauta da waɗansu abubuwa na rashin kula, amma tsumagiya za ta koya musu abin da ya fi kyau.
16 Idan attajirai kake yi wa kyauta, kana kuma zaluntar matalauta don ka arzuta, kai kanka za ka talauce.
17 Ka kasa kunne zan koya maka abin da masu hikima suka faɗa, yi nazari a kan koyarwarsu.
18 Za ka yi murna in ka tuna da su, ka iya faɗarsu.
19 Ina so ka dogara ga Ubangiji, don haka zan faɗa maka su yanzu.
20 Na rubuta maka karin magana, suna ƙunshe da ilimi da kyakkyawar shawara.
21 Zan koya maka ainihin gaskiya, domin sa'ad da aka aike ka ka nemo ta, za ka iya kawo amsa daidai.
22 Kada ka ƙwari matalauci don ka fi shi, kada ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari'a.
23 Ubangiji zai yi magana dominsu a kan shari'ar da suke yi, ya nemi ran duk wanda yake neman rayukansu.
24 Kada ka yi abuta da mutane masu zafin fushi, ko masu zafin rai.
25 Mai yiwuwa ne ka koyi irin ɗabi'unsu, har ka kasa sākewa.
26 Kada ka yi alkawarin ɗaukar wa wani lamuni,
27 gama idan ka kāsa biya har gadonka ma za su ɗauke.
28 Kada ka kawar da shidar kan iyaka wadda kakanninka suka kafa.
29 Ka nuna mini mutumin da yake aiki mai kyau, ni kuwa in nuna maka mutumin da ya fi duka, wanda ya cancanci ya zauna tare da sarakuna.
1 Sa'ad da ka zauna cin abinci tare da babban mutum, ka tuna da yadda yake.
2 Idan kai mai son ci da yawa ne sai ka kanne.
3 Kada ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da yake gabanku, zai yiwu wayo yake so ya yi maka.
4 Ka zama mai isasshiyar hikima, kada ka gajiyar da kanka garin ƙoƙarin neman dukiya.
5 Kuɗinka sun iya ƙarewa kamar ƙyiftawar ido, kamar suna da fikafikai su tashi kamar gaggafa.
6 Kada ka ci abincin marowaci, ko ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da ya sa a gabanka.
7 Zai ce, “Bari a ƙara maka,” amma ba haka yake nufi ba. Kamar gashi yake a cikin maƙogwaronka.
8 Za ka harar da abin da ka ci, dukan daɗin bakinka zai tafi a banza.
9 Kada ka yi wa wawa magana irin ta haziƙai, gama ba zai yaba da maganarka ba.
10 Kada ka kuskura ka kawar da shaidar iyaka, ko ka ƙwace gonar marayu.
11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.
12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa.
13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba.
14 Lalle ne za ka ceci ransa.
15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.
16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima.
17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba.
18 Idan haka ta samu za ka yi farin ciki nan gaba.
19 Ka saurara, ya ɗana, ka zama mai hikima. Ka yi tunani mai zurfi a kan hanyarka.
20 Kada ka zauna da mashayan ruwan inabi, ko masu haɗama.
21 Gama bugaggu da ruwan inabi da masu zarin ci za su zama matalauta. Idan iyakar abin da kake yi daga ci sai barci ne, nan da nan za ka ga kana saye da tsummoki.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, gama da ba dominsa ba, da ba ka, sa'ad da mahaifiyarka ta tsufa ka nuna mata godiyarka.
23 Gaskiya, da hikima, da ilimi, da hankali, sun cancanta a saye su, kome tamaninsu.
24 Mahaifin adali yana da dalilin yin murna. Zai yi fāriya a kan ɗa mai hikima.
25 Ka sa mahaifinka da mahaifiyarka su yi fāriya da kai, ka sa mahaifiyarka farin ciki.
26 Ɗana ka mai da hankali sosai, irin zamana ya zamar maka kyakkyawan misali.
27 Karuwa, da mata mazinata, tarkon mutuwa ne su.
28 Sukan laɓe su jira ka kamar mafasa, suna sa mutane da yawa su zama marasa aminci.
29 Wa ake yi wa kaito? Wa yake da baƙin ciki? Wane ne mafaɗaci? Wa yake yin gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan ido?
30 Sai riƙaƙƙen mashayi wanda yake gaurayar ruwan inabi.
31 Kada ka bar ruwan inabi ya jarabce ka, ko da yake ja wur yake, har kana iya ganin kanka a cikin ƙoƙon, yana kuwa da kyan gani sa'ad da kake motsa shi.
32 Kashegari za ka ji kamar maciji mai dafi ne ya sare ka.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, ba za ka iya tunani ko ka faɗi magana sosai ba.
34 Za ka ji kamar kana can cikin teku, jirin teku na ɗibarka kana lilo a kan rufin jirgin ruwa da yake tangaɗi.
35 Za ka ce, “Lalle an doke ni, sosai an daddoke ni amma ban san lokacin ba, me ya sa ban farka ba? Ina bukatar in ƙara sha.”
1 Kada ka ji ƙyashin mugaye, kada ka yi ƙoƙarin yin abuta da su.
2 Duk tunaninsu na yin mugunta ne, a duk lokacin da suka buɗe bakinsu sai sun cuci wani.
3 An gina gidaje a kan harsashin hikima da fahimi.
4 Ta wurin ilimi a kan ƙawata ɗakuna da kyawawan kayayyaki masu tamani.
5 Mai hikima ƙaƙƙarfa ne, i, mai ilimi yana daɗa ƙarfi.
6 Banda wannan ma, dole ne ka shisshirya a natse kafin ka kama yaƙi. Bisa ga shawarwarin da za ka samu ne za ka yi nasara.
7 Kalmomi masu hikima sun yi wa wawa zurfin ganewa ƙwarai, ba shi da ta cewa sa'ad da ake magana a kan muhimman abubuwa.
8 Idan a ko yaushe shirye-shiryen mugunta kake, za ka yi suna a kan kuta tashin hankali.
9 Kowace irin dabarar da wawa yake tunani a kanta zunubi ne. Jama'a suna ƙin mutum mai rainako.
10 Idan ba ka da ƙarfi a lokacin hargitsi, hakika ka tabbata marar ƙarfi.
11 Kada ka ji nauyin ceton wanda ake janye da shi zuwa inda za a kashe shi.
12 Mai yiwuwa ne ka ce kai ba ruwanka, amma Allah ya sani, yana kuwa auna manufofinka. Yana lura da kai, ya kuwa sani. Yakan sāka wa mutane a kan abin da suke aikatawa.
13 Ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau. Kamar yadda kakin zuma yake da zaƙi a harshenka,
14 haka ilimi da hikima suke da amfani ga ranka. Ka same su, a gaba za ka yi farin ciki.
15 Kada ka shirya dabarun yi wa amintacce ƙwace, ko ka ƙwace masa gidansa, wannan mugunta ce.
16 Ko sau nawa amintaccen mutum ya faɗi, ba abin damuwa ba ne, gama a ko yaushe zai sāke tashi, amma masifa takan hallaka mugaye.
17 Kada ka yi murna sa'ad da bala'i ya aukar wa maƙiyinka.
18 Ubangiji zai sani in kana murna, ba kuwa zai so haka ba, mai yiwuwa ne ba zai hukunta shi ba.
19 Kada ka damu saboda mugaye, kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.
20 Gama mugun mutum ba shi da sa zuciya, ba abin da zai sa zuciya a kansa nan gaba.
21 Ɗana, ka yi tsoron Ubangiji, ka kuma ji tsoron sarki, kada ka yi harkar kome da mutanen da suka tayar musu.
22 Irin waɗannan mutane sukan hallaka farat ɗaya. Ka taɓa yin tunani a kan bala'in da Allah ko sarki sukan aukar?
23 Masu hikima kuma sun faɗi waɗannan abu. Kuskure ne alƙali ya yi son zuciya.
24 Idan ya kuɓutar da mugu, kowane mutum da yake a duniya zai la'anta shi ya ƙi shi.
25 Alƙalan da suke hukunta wa mai laifi kuwa, za su arzuta, su ji daɗin kyakkyawan suna.
26 Amsar gaskiya ita ce alamar abuta ta ainihi.
27 Kada ka gina gidanka ka kafa shi, sai ka gyara gonakinka, ka tabbata za ka sami abin zaman gari.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isasshen dalili ba, ko ka faɗi ƙarya a kansa.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa daidai da yadda ya yi mini, zan rama masa!”
30 Na ratsa ta gonakin inabin wani malalaci, dakiki,
31 suna cike da ƙayayuwa, ciyayi sun sha kansu, katangar dutse da take kewaye da su ta faɗi.
32 Da na dubi wannan, na yi tunani a kansa, ya zamar mini ishara.
33 “Yi ta ruruminka, ci gaba da barcinka, rungume hannuwanka don ka shaƙata.”
34 Amma sa'ad da kake ta sharar barci fatara za ta auka maka kamar ƙungiyar 'yan fashi.
1 Ga waɗansu sauran karin maganar Sulemanu waɗanda magatakardan Hezekiya Sarkin Yahuza suka juya.
2 Muna girmama Allah saboda abin da ya rufe, muna girmama sarakuna saboda abin da suka ba da bayaninsa.
3 Ba ku taɓa sanin abin da sarki yake tunani ba, gama tunaninsa sun fi ƙarfinmu. Kamar nisan sararin sama suke ko zurfafan teku.
4 Ka tace azurfa, gwani kuwa zai yi wani kyakkyawan abu da ita.
5 A kawar da mugayen mashawarta daga gaban sarki, hukumarsa za ta shahara a kan adalci.
6 Sa'ad da kake tsaye a gaban sarki, kada ka nuna kai wani abu ne, kana kai kanka inda Allah bai kai ka ba.
7 Gara a roƙe ka ka hau zuwa babban matsayi, da a faɗa maka ka ba da wurin da kake ga wanda ya fi ka maƙami.
8 Kada ka yi garajen kai ƙara a majalisa. Idan wani mashaidi ya nuna kai kake da kuskure, me za ka yi?
9 Idan kai da maƙwabcinka kun saɓa, ku daidaita a tsakaninku, kada a tona asiri.
10 Mai yiwuwa ne wani ya ji ya zarge ku, ba za ku taɓa rabuwa da wannan kunya ba.
11 Manufar da aka bayyana sosai kamar zubin zinariya take wanda aka yi a kan azurfa.
12 Faɗakarwar da mutumin da ya gogu da al'amuran duniya ya yi ga wanda yake da niyya ya kasa kunne, tamaninta ya fi na zoben zinariya, ko kayan ado da aka yi da zinariya tsantsa.
13 Amintaccen manzo yakan wartsakar da wanda ya aike shi, kamar ruwan sanyi yake a lokacin zafi.
14 Mutanen da suke yin alkawari, ba su cikawa, kamar holoƙo suke, hadirin kaka.
15 Rinjayen da aka yi cikin haƙuri yakan rushe ƙaƙƙarfar tsayayya, har ma yakan i wa masu ƙarfin gaske.
16 Kada ka kuskura ka sha zuma gaba da kima, in ya yi maka yawa za ka yi hararwa.
17 Kada ka cika ziyartar maƙwabcinka, ko zai gaji da kai har ya ƙi ka.
18 Mutumin da yakan faɗi ƙarairayi a kan maƙwabcinsa, shi kamar kakkaifan takobi ne, ko kulki, ko kibiya mai tsini.
19 Dogara ga marar aminci a lokacin hargitsi, kamar ƙoƙarin yin tauna da ruɓaɓɓun haƙora ne, ko yin tafiya da mai gurguwar ƙafa,
20 ko kuma ka yi ƙoƙarin jin ɗumi ta wurin tuɓe tufafinka a ranar da ake sanyi. Raira waƙa ga mai baƙin ciki kamar marmasa gishiri a kan rauni ne.
21 Idan maƙiyinka yana jin yunwa ka cishe shi, idan yana jin ƙishi ka ba shi abin sha.
22 Za ka sa ya sha kunya, Ubangiji kuma zai sāka maka.
23 Iskar arewa takan kawo ruwan sama, haka kuma jita-jita takan kawo fushi.
24 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mata mai mita.
25 Jin labari mai daɗi wanda ba ka zato, yana kamar shan ruwan sanyi ne a sa'ad da ka sha rana kana jin ƙishi.
26 Mutumin kirki wanda yakan yarda da mugun yana tunasshe ka da ƙazantattun maɓuɓɓuga ko rijiya mai dafi.
27 Kamar yadda shan zuma da yawa ba shi da kyau a gare ka, haka kuma ƙoƙarin neman yabo mai yawa yake.
28 Idan ba ka iya danne fushinka ba, ka zama mai kasala kamar birnin da ba shi da garuka, yana buɗe don a faɗa masa.
1 Yabo bai dace da wawa ba, kamar yadda dusar ƙanƙara ba ta dace da lokacin zafi ba, ko ruwan sama a lokacin girbi.
2 La'ana ba za ta kama ka ba, sai dai in ka cancance ta. Tana kamar tsuntsayen da suke firiya da dare ba za su sauka ba.
3 Sai ka fyaɗi doki, ka sa wa jaki linzami, wawa kuma sai ka doke shi.
4 Idan ka amsa tambayar wauta, ka zama wawa daidai da mutumin da ya yi tambayar.
5 Ka amsa wauta ga tambayar wauta, wanda ya yi tambayar zai gane wawancinsa.
6 Mutumin da ya sa wawa ya isar masa da saƙo ya datse ƙafafunsa, yana nemar wa kansa wahala.
7 Wawa yakan yi amfani da karin magana kamar yadda tauyayyen mutum yake amfani da ƙafafunsa.
8 Wanda ya yabi wawa yana kama da wanda ya ɗaura dutse a majajjawa.
9 Karin magana a bakin wawa kamar sukar ƙaya ce a hannun mai maye.
10 Wanda ya ɗauki wawa aiki yana cutar duk wanda aikin ya shafa.
11 Wawan da yake maimaita aikin wautarsa yana kama da kare mai yin amai ya koma ya tanɗe.
12 Gwamma riƙaƙƙen wawa da mutum mai ganin kansa mai hikima ne.
13 Don me malalaci yakan kasa fita daga gida? Zaki yake tsoro?
14 Malalaci yana ta jujjuyawa a gadonsa kamar yadda ƙyauren ƙofa take juyawa.
15 Malalaci yana sa hannu cikin ƙwaryar abinci, amma ya kāsa kaiwa bakinsa.
16 Malalaci yana ganin kansa mai hikima ne fiye da mutum bakwai waɗanda suke da dalilai a kan ra'ayinsu.
17 Mutumin da ya tsoma baki cikin jayayyar da ba ta shafe shi ba sa'ad da yake wucewa, yana kama da mutum wanda yake kama kare a kunne.
18 Mutum wanda yakan ruɗi maƙwabcinsa sa'an nan ya ce, wasa yake yi kawai, yana kama da mahaukaci wanda yake wasa da wuta, da kibau, da mutuwa.
19
20 Idan ba itace wuta takan mutu, haka kuma idan ba mai gulma ba za a yi jayayya ba.
21 Kamar yadda gawayi yake ga garwashin wuta, itace kuma ga wuta, haka mai gardama yake ga jayayya.
22 Kamar yadda lomar abinci mai daɗi takan gangara can cikin ciki haka maganar mai gulma take.
23 Bakin da ba ya faɗar gaskiya, da zuciya mai ƙiyayya suna kama da kaskon da aka dalaye da azurfar da ba a tace ba.
24 Mai yin ƙiyayya yakan ɓoye ta da maganar bakinsa, yana kuma ƙunshe da munafunci.
25 Sa'ad da yake magana mai kyau kada ka gaskata shi, domin zuciyarsa tana cike da mugunta.
26 Ko da yake kila zai ɓoye ƙiyayyarsa, duk da haka muguntarsa za ta bayyana ga mutane.
27 Wanda ya haƙa ramin mugunta shi zai faɗa ciki, wanda kuma ya mirgino dutse, zai fāɗo a kansa.
28 Maƙaryaci yana ƙin wanda ya yi wa ƙarya, mai daɗin baki kuma yakan aikata ɓarna.
1 Kada ka yi fāriya a kan abin da za ka yi gobe domin ba ka san abin da zai faru daga yanzu zuwa gobe ba.
2 Bari waɗansu su yabe ka ko da baƙi ne, faufau kada ka yabi kanka.
3 Dutse da yashi suna da nauyi ƙwarai, amma nauyin wahalar da wawa zai haddasa ya fi nasu duka.
4 Fushi mugun abu ne mai hallakarwa, amma duk da haka bai kai ga kishi ba.
5 Gara ka tsauta wa mutum a fili da ka bar shi ya zaci ba ka kula da shi ba sam.
6 Aboki aboki ne ko da ya cuce ka, amma maƙiyi ko ya rungume ka kada ka sake!
7 Wanda ya ƙoshi ba zai ko kula da zuma ba, amma wanda yake jin yunwa abinci mai ɗaci zaƙinsa yake ji.
8 Mutumin da ya bar gida yana kama da tsuntsun da ya bar sheƙarsa.
9 Turare da man ƙanshi sukan sa ka ji daɗi, haka abuta ta ainihi takan ƙara maka ƙarfi.
10 Kada ka manta da abokanka, ko abokan mahaifinka. Idan kana shan wahala kada ka nemi taimako wurin ɗan'uwanka. Maƙwabci na kusa yana iya taimakonka fiye da ɗan'uwan da yake nesa.
11 Ɗana, ka zama mai hikima, ni kuwa zan yi farin ciki, zan iya amsa kowace irin sūkar da wani zai yi mini.
12 Mutum mai hankali yakan hango hatsari ya kauce masa, amma mutumin da ba shi da kula, yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.
13 Ka karɓe tufar wanda ya zamar wa baƙo lamuni, da kuma wanda ya zama lamunin karuwa.
14 In ka farkar da abokinka da babbar murya tun da sassafe, daidai ne da zaginsa.
15 Mace mai mita kamar ɗiɗɗigar ruwa take ba ƙaƙƙautawa.
16 Kaƙa za ka iya sa ta ta kame bakinta? Ka taɓa ƙoƙarin tsai da iska? Ko kuwa ka taɓa ƙoƙarin dintsi mai a tafin hannunka?
17 Daga wurin mutane mutane suke koyo, kamar yadda a kan wasa ƙarfe da ƙarfe.
18 Ka lura da itacen ɓaure, zai yi 'ya'ya ka ci. Baran da ya lura da maigidansa za a girmama shi.
19 Yadda kake ganin fuskarka a ruwa, haka kake ganin kanka a zuciyarka.
20 Muradin mutum kamar lahira yake, a kullum ba ya ƙoshi.
21 Da wuta ake gwada azurfa da zinariya, amma yabon da ake yi wa mutum shi ne magwajinsa.
22 Ko da za ka doki wawa ka bar shi tsakanin rai da mutuwa, duk da haka yana nan da wautarsa kamar yadda yake.
23 Ka lura da garkunan tumakinka da na shanunka da kyau iyakar iyawarka,
24 domin dukiya ba ta tabbata har abada, al'ummai ma haka ne.
25 Ka yanki ingirici, lokacin da yake toho kana iya yankar ciyawa a gefen tuddai.
26 Kana iya yin tufafi da ulun tumakinka, kana iya sayen gona da kuɗin awakinka.
27 Madarar awakinka za ta zama abincinka kai da iyalinka, da kuma barorinka 'yan mata.
1 Mugun mutum yakan gudu, alhali kuwa ba mai korarsa, amma amintaccen mutum kamar zaki yake, ba shi da tsoro.
2 Al'umma za ta ƙarfafa ta jure idan shugabanninta masu basira ne, masu hankali. Amma idan ƙasar mai aikata zunubi ce za ta sami shugabanni da yawa.
3 Mai mulki wanda yake zaluntar talakawa, ya zama kamar ruwa mai lalatar da amfanin gona.
4 Wanda ba ya bin doka tare da mugaye yake, amma idan kana bin doka kai abokin gāban mugaye ne.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada sun san ta sosai.
6 Gara ka zama matalauci mai aminci da ka zama mawadaci, marar aminci.
7 Saurayi wanda ya kiyaye doka mai basira ne shi, amma wanda yake abuta da 'yan iska zai zama mai jawo wa mahaifinsa kunya.
8 Idan kana tara dukiya ta wurin ba da bashi da ruwa kana kuma ƙwarar jama'a, dukiyarka za ta koma ga wanda yake yi wa talakawa alheri.
9 Idan ka ƙi biyayya ga doka, Allah zai ƙi jin addu'o'inka.
10 Idan ka yaudari mutumin kirki don ya faɗa cikin mugunta, kai kanka ne za ka fāɗa cikin tarkon da ka haƙa. Marar laifi kuwa zai sami babban sakamako.
11 Attajirai, a ko yaushe, zato suke su masu hikima ne, amma matalauci mai tunani ya fi sanin abin da yake daidai.
12 Sa'ad da mutanen kirki suke sarauta, kowa da kowa yakan yi biki, amma sa'ad da mugaye suka kama mulki mutane sukan riƙa ɓuya.
13 Ba za ka taɓa cin nasara a zamanka ba muddin kana ɓoye laifofinka. Ka hurta zunubanka ka tuba, sa'an nan Allah zai yi maka jinƙai.
14 Mutumin da yake tsoron Ubangiji ko yaushe, zai yi farin ciki, amma idan ya taurare zai lalace.
15 Talakawa ba su da wani taimako sa'ad da suke ƙarƙashin mulkin mugun. Abin tsoro ne shi kamar zaki mai ruri, ko beyar mai sanɗa.
16 Mai mulki wanda ba shi da basira yakan zama mai mugun tsanani. Amma wanda yake ƙin rashin aminci, ko ta ƙaƙa zai daɗe yana mulki.
17 Mutumin da yake da laifin kisankai, yana haƙa wa kansa kabari da gaggawa. Kada ka yi ƙoƙarin hana shi.
18 Ka yi aminci za ka zauna lafiya, idan kuwa ka yi rashin aminci za ka fāɗi.
19 Manomin da yake aiki sosai, zai sami wadataccen abinci, amma mutanen da suke zaman banza ko yaushe, za su zama matalauta.
20 Amintaccen mutum zai cika kwanakinsa lafiya, amma idan kana so ka sami dukiya dare ɗaya, za a hukunta ka.
21 Nuna sonkai mugun abu ne, waɗansu alƙalai sukan aikata mugunta saboda 'yar ƙaramar rashawa.
22 Mutum mai haɗama yana gaggawar samun dukiya, bai kuwa sani ba, ashe, fatara ce za ta same shi.
23 Wanda ya tsauta wa mutum zai sami yabo daga baya, fiye da wanda ya yi masa daɗin baki.
24 Wanda yake yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa sata, yana kuwa tsammani ba laifi ba ne, daidai da ɓarawo yake.
25 Mutum mai haɗama yana haddasa tashin hankali, amma wanda ya dogara ga Ubangiji zai sami wadar zuci.
26 Wanda yake dogara ga son zuciyarsa, wawa ne, amma wanda yake tafiya cikin hikima zai kuɓuta.
27 Wanda yake bayarwa ga matalauta, ba zai talauce ba, amma wanda bai kula da su ba, mutane da yawa za su la'ance shi.
28 Mutane sukan ɓuya sa'ad da mugaye suka sami iko, amma sa'ad da iko ya fita daga hannunsu adalai sukan ƙaru.
1 Wanda ake ta tsauta wa a kai a kai, amma ya taurare, ba makawa tasa ta ƙare farat ɗaya.
2 Sa'ad da masu adalci suke mulki, jama'a sukan yi murna, amma sa'ad da mugaye suke mulki, jama'a sukan yi nishi.
3 Wanda yake ƙaunar hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa. Amma wanda yake abuta da karuwai zai lalatar da dukiyarsa.
4 Sarkin da yake aikata adalci ƙasarsa za ta yi ƙarƙo, amma wanda yake karɓar rashawa zai lalatar da ƙasar.
5 Mutum wanda yake yi wa maƙwabcinsa daɗin baƙi yana kafa wa kansa tarko.
6 Laifin mugun zai zama tarko a gare shi, amma adali zai raira waƙa, ya yi farin ciki.
7 Adali yana sane da hakkin matalauta, amma mugun bai san wannan ba.
8 Ashararai sukan sa wa birni wuta, amma masu hikima sukan kwantar da hasala.
9 Idan gardama ta shiga tsakanin mai hikima da wawa, sai wawa ya yi ta fushi, ko kuwa ya yi ta dariya, gardamar dai ba za ta ƙare ba.
10 Mutane masu kisankai suna ƙin amintaccen mutum, amma adalai za su kiyaye ransa.
11 Wawa yakan nuna fushinsa ko yaushe, amma mutum mai hikima yakan kanne fushinsa.
12 Idan mai mulki yana kasa kunne ga maganganun ƙarya, dukan ma'aikatansa za su zama maƙaryata.
13 Matalauci da azzalumi suna tarayya a abu ɗaya, wato dukansu Ubangiji ne yake ba su ganin gari.
14 Idan sarki yana yi wa talakawa shari'ar gaskiya, zai daɗe yana mulki.
15 Horo da tsautawa suna ba da hikima, amma yaron da aka sangarta zai jawo wa mahaifiyarsa kunya.
16 Sa'ad da mugaye suke mulki, laifofi suka ƙaru, amma adalai za su ga faɗuwar waɗannan mutane.
17 Ka hori ɗanka zai daɗaɗa maka rai, ya kuma faranta maka zuciya.
18 Inda ba a bin faɗar Allah, jama'a za su kangare, amma mai farin ciki ne wanda yake kiyaye dokar Allah.
19 Bara ba ya horuwa ta wurin magana kawai, gama ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
20 Ka ga mutum mai garajen yin magana? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
21 Baran da aka shagwaɓa tun yana yaro, a ƙarshe zai ɗauki kansa tankar magājin gida.
22 Mutum mai saurin fushi yakan ta da faɗa, mai zafin rai kuma yakan aikata laifi da yawa.
23 Girmankan mutum zai jawo masa ƙasƙanci, amma za a girmama mai tawali'u.
24 Abokin ɓarawo mugun maƙiyin kansa ne, yana jinsa yana ta rantsuwa, amma ba zai ce kome ba.
25 Jin tsoron mutane tarko ne, amma wanda ya dogara ga Ubangiji za a ɗaukaka shi.
26 Mutane da yawa sukan nemi farin jini daga wurin mai mulki, amma Ubangiji ne yake yi wa mutum adalci.
27 Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga adali, adali kuma abin ƙyama ne ga mugun.
1 Waɗannan su ne maganar Agur ɗan Yake, da ya yi wa Etiyel da Yukal,
2 “Hakika wautata ta sa na zama kamar dabba ba mutum ba, Ba ni kuwa da fahimi irin na mutum.
3 Ban koyi hikima ba, Ban kuwa san kome game da Allah ba.
4 Wa ya taɓa hawa cikin Sama ya sauko? Wa ya taɓa kama iska cikin tafin hannunsa? Wa ya taɓa ƙunshe ruwa cikin rigarsa? Wa kuma ya kafa iyakar duniya? Ina sunansa, ina kuma sunan ɗansa? Hakika ka sani!
5 “Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa.
6 Kada ka yi ƙari a kan maganarsa, don kada ya tsauta maka, a kuma bayyana kai maƙaryaci ne.”
7 Abu biyu na roƙe ka, kada ka hana mini su kafin in mutu.
8 Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,
9 don kada in wadata, har in yi musunka, in ce, “Wane ne Ubangiji?” Kada kuwa in yi talauci har in yi sata in saɓi sunan Allahna.
10 Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la'ance ka.
11 Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba.
12 Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.
13 Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira.
14 Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya.
15 Matsattsaku tana da 'ya'ya mata biyu, ana kiransu, “Ba ni, Ba ni.” Akwai abu uku da ba su ƙoshi, i, har huɗu ma da ba su cewa, “Ya isa,” wato lahira, macen da ba ta haihuwa, ƙasa wadda ba ta ƙoshi da ruwa, wuta wadda ba ta cewa, “Ya isa.”
16
17 Idan ɗa ya raina mahaifi, ya kuma yi wa mahaifiya ba'a hankakin kwari za su ƙwaƙule masa idanu, 'ya'yan mikiya za su cinye.
18 Akwai abu uku, i, har huɗu ma, waɗanda ban iya fahimtar su ba, wato yadda gaggafa take tashi a sararin sama, yadda maciji yake jan ciki a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, Sha'anin namiji da 'ya mace.
19
20 Ga yadda al'amarin mazinaciya yake, takan yi sha'aninta sa'an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!”
21 Akwai abu uku, i, har huɗu ma waɗanda duniya ba ta jurewa da su, wato bara da ya zama sarki, wawa da ya ƙoshi da abinci, mummunar mace da ta sami miji, baiwar da ta gāji uwargijiyarta.
22
23
24 Akwai ƙananan abubuwa huɗu a duniya, amma suna da hikima ƙwarai, wato tururuwa talikai ne marasa ƙarfi, amma duk da haka sukan tanadi abincinsu da rani, remaye ba ƙarfafa ba ne, duk da haka suna yi wa kansu gidaje a cikin duwatsu, fara ba su da sarki, amma duk da haka suna tafiya sahu-sahu. ƙadangare ma wanda ka iya kama shi a hannu, amma yana zama a cikin fādodin sarakuna.
25
26
27
28
29 Akwai abu uku, i, har huɗu ma da suke da kwarjini da taƙama a tafiyarsu, wato Zaki wanda ya fi dukan dabbobi ƙarfi, ba ya ratse wa kowa daga cikinsu, bunsuru da zakara mai taƙama, sarkin da yake tafiya gaban jama'arsa.
30
31
32 Idan ka yi wauta kana ta ɗaukaka kanka, ko kuwa kana shirya mugunta, ka tsaya ka yi tunani!
33 Gama kaɗa madara takan kawo mai, murɗa hanci takan sa a yi haɓo, tsokanar fushi takan kawo jayayya.
1 Wannan ita ce maganar sarki Lamuwel wadda uwarsa ta koya masa.
2 “Mene ne, ɗana? Mene ne, ya ɗana ne cikina? Mene ne, ɗana na wa'adi?
3 Kada ka ba da ƙarfinka ga mata, kada kuwa ka mai da hankali gare su, waɗanda suke hallaka sarakuna.
4 Bai dace ba, ya Lamuwel, bai dace ba ko kaɗan, sarakuna su sha ruwan inabi, ko masu mulki su yi marmarin barasa,
5 don kada su sha su manta da doka, su kuma kauce wa gaskiya a shari'ar waɗanda aka zalunta.
6 A ba da barasa ga wanda yake cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi kuma ga waɗanda suke cikin ɓacin rai.
7 Bari ya sha don ya manta da talaucinsa, don kada kuma ya ƙara tunawa da ɓacin ransa.
8 “Ka yi magana domin bebaye, domin kuma hakkin dukan waɗanda ba su da wani mataimaki.(1Sam 19.4; Ayu 29.12-17)
9 Ka yi magana dominsu, ka yi shari'ar adalci, ka kiyaye hakkin matalauta da masu bukata.”
10 Wa yake iya samun cikakkiyar mace? Darajarta ta fi ta lu'ulu'ai.
11 Mijinta yakan amince da ita, ba kuwa zai yi hasara ba.
12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakinta.
13 Takan samo ulu da lilin, ta yi saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 Takan kawo abincinta daga nesa, kamar fatake.
15 Takan yi asubanci ta shirya wa iyalinta abinci, ta kuma shirya wa 'yan matan gidanta aike-aiken da za su yi.
16 Takan lura da gona sosai kafin ta saya, da ribar da ta ci take dasa gonar inabi.
17 Takan himmantu ta yi aiki tuƙuru.
18 Ta sani akwai riba a cikin kasuwancinta. Fitilarta na ci dare farai.
19 Da hannunta take kaɗi, tana kuma saƙa da hannuwanta.
20 Takan yi wa matalauta da masu fatara karamci.
21 Ba ta jin tsoron lokacin sanyi gama 'ya'yanta duka suna da tufafi masu ƙauri.
22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa, tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Mijinta sananne ne a dandali, sa'ad da yake zaune tare da dattawan gari.
24 Takan yi riguna na lilin ta sayar, takan kuma sayar wa fatake da abin ɗamara.
25 Wadata da mutunci su ne suturarta. Ba ta jin tsoron tsufa.
26 Tana magana da hikima. Koyarwarta ta alheri ce.
27 Tana lura da al'amuran 'ya'yanta da kyau. Ba ruwanta da ƙyuya.
28 'Ya'yanta sukan tashi su gode mata, mijinta kuma yana yabonta.
29 Ya ce, “Mata da yawa sun yi abin yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Kayan tsari da jamali duk banza ne, amma mace mai tsoron Ubangiji, ita ce abar yabo.
31 A yi mata cikakken yabo saboda ayyukanta, za a yabi ayyukanta a dandali.