1

1 Akwai wani mutum a ƙasar Uz, mai suna Ayuba, amintacce ne, mai tsoron Allah. Shi mutumin kirki ne, natsattse, yana ƙin aikata kowace irin mugunta.

2 Yana da 'ya'ya bakwai maza, uku mata.

3 Yana da tumaki dubu bakwai (7,000), da raƙuma dubu uku (3,000), da shanu dubu guda (1,000), da jakuna ɗari biyar. Yana kuma da barori masu yawan gaske, don haka ya fi kowa a ƙasar gabas arziki nesa.

4 'Ya'yansa maza sukan yi liyafa bi da bi a gidajen junansu, inda su duka sukan taru koyaushe, sukan gayyaci 'yan'uwan nan nasu mata su halarci liyafar.

5 A kowane lokacin da aka gama da liyafar, Ayuba yakan tashi da sassafe, kashegarin liyafar, yă miƙa hadayu don yă tsarkake 'ya'yansa. Haka yake yi kullum, don yana zaton mai yiwuwa ne ɗaya daga cikin 'ya'yan ya yi zunubi, ya saɓi Allah a ɓoye.

6 Sa'ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta yi, Shaiɗan ma ya zo tare da su.

7 Sai Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Kai fa me kake yi?” Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, a ko'ina a duniya.”

8 Ubangiji ya ce masa, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta.”

9 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “A banza Ayuba yake yi maka sujada?

10 Ai, don ka kiyaye shi ne, shi da iyalinsa, da dukan abin da yake da shi. Ka kuma sa wa duk abin da yake yi albarka, ka kuwa ba shi shanun da suka isa su cika dukan ƙasan nan.

11 Amma da a ce za ka raba shi da dukan abin hannunsa, to, da zai fito fili yă zage ka ƙiri ƙiri.”

12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, dukan abin hannunsa yana cikin ikonka, amma shi kansa kada ka cuce shi.” Sai Shaiɗan ya tafi.

13 Wata rana 'ya'yan Ayuba suna shagali a gidan wansu,

14 sai ga jakada ya zo wurin Ayuba a guje, ya ce, “Muna huɗar gona da shanu, jakuna suna kiwo a makiyayar da suke kusa da wurin,

15 sai Sabiyawa suka auka musu farat ɗaya, suka sace su duka, suka kuma karkashe duk barorinka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

16 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Tsawa ta kashe tumaki da makiyayansu duka, ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

17 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa suka auka mana, suka kwashe raƙuma duka, suka kuma karkashe barorinka duka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.”

18 Kafin yă gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Sa'ad da 'ya'yanka suke liyafa a gidan wansu,

19 sai hadiri ya taso daga hamada, ya rushe gidan, ya kashe 'ya'yanka duka, ni kaɗai na tsira na zo in faɗa maka.”

20 Sai Ayuba ya tashi, ya kyakkece tufafinsa don baƙin ciki. Ya aske kansa, ya fāɗi ƙasa,

21 ya ce, “Ban shigo duniya da kome ba, ba kuma zan fita cikinta da kome ba. Ubangiji ya bayar, shi ne kuma ya karɓe, yabo ya tabbata ga sunansa.”

22 Ko da yake waɗannan al'amura duka sun faru, duk da haka Ayuba bai sa wa Allah laifi ba.

2

1 Sa'ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta sāke yi, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.

2 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ina ka fito?” Sai Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, ko'ina a duniya.”

3 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta. Kai ka sa na yardar maka ka far masa, ba tare da wani dalili ba. Amma duk da haka Ayuba yana nan da amincinsa kamar yadda yake.”

4 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Mutum ya iya rabuwa da dukan abin da yake da shi don yă ceci ransa.

5 Amma yanzu da a ce za ka taɓa lafiyar jikinsa, da sai yă fito fili yă zage ka.”

6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Shi ke nan, yana cikin ikonka, amma fa, kada ka kashe shi.”

7 Sa'an nan Shaiɗan ya rabu da Ubangiji, ya je ya sa ƙuraje su fito ko'ina a jikin Ayuba.

8 Ayuba ya je ya zauna kusa da juji ya ɗauki tsingaro ya yi ta sosa ƙurajen.

9 Sai matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana da amincin nan naka? Don me ba za ka zagi Allah ka mutu ba?”

10 Ayuba ya amsa, ya ce mata, “Wace irin maganar gāɓanci ce haka? Lokacin da Allah ya aiko mana da alheri, mukan yi na'am da shi, to, me zai sa sa'ad da ya aiko mana da wahala za mu yi gunaguni?” Cikin dukan wahalar da Ayuba ya sha, bai sa wa Allah laifi ba.

11 Sa'ad da uku daga cikin abokan Ayuba, wato Elifaz daga birnin Teman, da Bildad daga ƙasar Shuwa, da Zofar daga ƙasar Na'ama, suka ji labarin irin yawan wahalar da Ayuba yake sha, sai suka kama hanya suka tafi su ziyarce shi, su ta'azantar da shi.

12 Suka hango Ayuba tun daga nesa, amma ba su gane shi ba. Da suka gane shi sai suka fara kuka da murya mai ƙarfi. Suka kyakkece tufafinsu saboda baƙin ciki, suka ɗibi ƙura suka watsa a kawunansu.

13 Sa'an nan suka zauna a ƙasa tare da shi, har kwana bakwai, amma ba wanda ya ce uffan, saboda ganin irin yawan wahalar da yake sha.

3

1 Ayuba ya yi magana ya la'anci ranar da aka haife shi.

2 Ya ce, “Ya Ubangiji, ka la'anci ranan nan da aka haife ni.

3 Ka la'anci daren nan da aka yi cikina.

4 Ka mai da ranan nan ta zama duhu, ya Allah. Kada a ƙara tunawa da wannan rana, Kada haske ya ƙara haskakata.

5 Ka sa ta zama ranar duhu baƙi ƙirin. Ka rufe ta da gizagizai, kada hasken rana ya haskaka ta.

6 Ka shafe wannan dare daga cikin shekara, Kada kuma a ƙara lasafta shi.

7 Ka sa daren ya zama marar amfani, daren baƙin ciki.

8 Ka faɗa wa masu sihiri su la'anci wannan rana, Su waɗanda suke umartar dodon ruwa.

9 Ka hana gamzaki haskakawa, Kada ka bar daren nan ya sa zuciya ga wayewar gari,

10 Ka la'anci daren nan da aka haife ni, Da ya jefa ni a baƙin ciki da wahala.

11 “Da ma na mutu tun a cikin cikin uwata, Ko kuwa da haihuwata in mutu.

12 Me ma ya sa uwata ta rungume ni a ƙirjinta, Ta shayar da ni kuma da mamanta?

13 Da a ce na mutu a lokacin, da yanzu ina huce,

14 Da ina ta barcina kamar sarakuna da masu mulki Waɗanda suka sāke gina fādodi na dā,

15 Da ina ta sharar barcina kamar shugabanni Waɗanda suka cika gidajensu da zinariya da azurfa,

16 In yi ta sharar barci kamar jariran da aka haifa matattu.

17 Mugaye za su daina muguntarsu a kabari, Ma'aikatan da suka gaji da aiki su ma za su huta,

18 Har 'yan sarƙa ma za su ji daɗin salama, Su huta daga tsautawa da umarnai masu tsanani.

19 Kowa da kowa yana wurin, babba da ƙarami duk ɗaya ne, Bayi ma sun sami 'yanci.

20 “Me ya sa ake barin mutane su yi ta zama cikin damuwa? Me ya sa ake ba da haske ga waɗanda suke baƙin ciki?

21 Sun jira mutuwa, amma ta ƙi samuwa, Sun fi son kabari da kowace irin dukiya.

22 Ba su da farin ciki, sai sun mutu an binne su tukuna.

23 Allah ya ɓoye musu sanin abin da zai faru nan gaba, Ya kalmashe su kowane gefe.

24 A maimakon cin abinci, sai baƙin ciki nake yi, Ba kuma zan daina yin nishi ba,

25 Dukan abin da nake jin tsoro ko fargaba ya faru.

26 Ba ni da salama, ba ni da hutawa, Wahala ba za ta taɓa ƙarewa ba.”

4

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Ayuba, za ka ji haushi in na yi magana? Ba zan iya kannewa, in yi shiru ba.

3 Ka koya wa mutane da yawa, Ka kuma ƙarfafa hannuwan marasa ƙarfi.

4 Idan wani ya yi tuntuɓe, Ya gaji, ya rasa ƙarfi, Kalmominka suka ƙarfafa zuciyarsa, Har ya iya tsayawa kyam.

5 Yanzu naka lokacin wahala ya zo, Kai kuwa ka rikice, ka kasa ɗaurewa,

6 Kana yi wa Allah sujada, Ba wani laifi a zamanka, Ya kamata ka amince ka sa zuciya.

7 “Yanzu fa sai ka yi tunani. Ka faɗi bala'i ɗaya wanda ya taɓa fāɗa wa adalin mutum.

8 Na taɓa ganin mutane suna huɗe gonar mugunta, Suna shuka mugunta, Suka kuwa girbe mugunta.

9 A cikin fushinsa Allah yakan hallaka su kamar hadiri.

10 Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki, Amma Allah yakan sa su yi tsit, Ya kakkarya haƙoransu.

11 Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci, Haka nan za su mutu, 'ya'yansu kuwa su warwatse duka.

12 “Wata rana wani saƙo ya zo a hankali, Har da ƙyar nake iya ji,

13 Kamar wani irin mafarki mai razanarwa yake, Wanda ya hana ni jin daɗin barcina.

14 Na yi rawar jiki ina makyarkyata, Duk jikina yana ta ɓare-ɓare don tsoro.

15 Wata iska marar ƙarfi ta taɓa fuskata, Sai fatar jikina ta yanƙwane saboda fargaba.

16 Na ga wani abu can yana tsaye, Na zura ido, amma ban san kowane irin abu ba ne, Ina cikin wannan hali sai na ji murya,

17 Ta ce, ‘Mutum yana iya zama adali a gaban Allah? Akwai kuma wanda yake mai tsarki a gaban Mahaliccinsa?

18 Allah ba ya amince wa barorinsa na cikin sammai, Yakan sami laifi a wurin mala'ikunsa.

19 Ta ƙaƙa zai amince da talikinsa wanda aka yi da ƙasa, Abin da yake na ƙura, ana kuwa iya murƙushe shi kamar asu.

20 Mai yiwuwa ne mutum yana raye da safe Amma ya mutu ba a sani ba kafin maraice.

21 Duk abin da ya mallaka an ɗauke, Duk da haka ya mutu cikin rashin hikima.’ ”

5

1 “Ka yi kira, ya Ayuba, ka gani, ko wani zai amsa! Akwai wani mala'ika da za ka juya zuwa gare shi?

2 Ba shi da amfani ka dami kanka Har ka mutu, saboda tsarguwa, gama wannan wawanci ne, Da aikin rashin hankali.

3 Na ga waɗansu wawaye waɗanda ake gani kamar suna zaune lafiya, Amma nan da nan sai na la'anci gidajensu.

4 Ko kaɗan, 'ya'yansu maza ba za su taɓa zama lafiya ba. Ba wanda zai tsaya musu a ɗakin shari'a.

5 Mayunwata za su ci amfanin gonar wawa, Har da hatsin da yake girma cikin ƙayayuwa, Waɗanda suke jin ƙishirwa za su ji ƙyashin dukiyarsa.

6 Zunubi ba ya tsirowa daga ƙasa, Haka ma wahala ba ta tsirowa daga ƙasa.

7 Ai, an haifi mutum domin wahala ne, Tabbatacce ne kamar yadda tartsatsin wuta suke tashi.

8 “In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah, In kai ƙarata a wurinsa.

9 Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba, Al'ajabansa kuwa ba su da iyaka.

10 Yakan aiko da ruwan sama, Ya shayar da gonaki.

11 I, Allah ne yake ɗaukaka masu tawali'u, Shi yake kuɓutar da dukan waɗanda suke makoki.

12 Yakan birkitar da shirye-shiryen masu wayo.

13 Yakan sa wa masu wayo tarko cikin dabarunsu, Har ba za su yi nasara a dukan abin da suke yi ba.

14 Da rana sukan yi karo da duhu, Ko da tsakar rana ma lalube suke kamar ana duhu.

15 Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa, Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci.

16 Yakan sa matalauta su sa zuciya, Ya sa mugaye su yi shiru.

17 “Mai farin ciki ne mutumin da Allah ya hora, Kada ka tsargu sa'ad da ya tsauta maka.

18 Allah yakan yi maganin raunin da ya yi maka, Ciwon da ya ji maka da hannunsa, Da hannunsa yakan warkar.

19 Yakan tsare ka daga cuta sau shida har sau bakwai, Ba muguntar da za ta taɓa ka.

20 Yakan kiyaye ka da rai a lokacin yunwa, A yaƙi kuma yakan tsare ka daga mutuwa.

21 Allah yakan kuɓutar da kai daga ƙarairayi da ɓata suna, Yakan cece ka daga hallaka.

22 Aikin kama-karya da yunwa za su zama abin dariya a gare ka, Ba kuwa za ka ji tsoron namomin jeji ba.

23 Ba za a sami duwatsu a gonakin da kake nomawa ba, Mugayen namomin jeji ba za su far maka ba.

24 Sa'an nan za ka zauna lafiya a alfarwanka, A sa'ad da ka dubi tumakinka, za ka tarar suna nan lafiya.

25 'Ya'yanka za su yi yawa kamar ciyawa, Kamar yadda alkama take a lokacin kakarta.

26 Haka kai ma za ka rayu, har ka tsufa da kyakkyawan tsufa.

27 Kai, Ayuba, mun koyi wannan don mun daɗe muna nazari, Gaskiya ce, don haka ka yarda da wannan.”

6

1 Ayuba ya amsa.

2 “In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma'auni,

3 Da sun fi yashin teku nauyi. Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi.

4 Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau, Dafinsu kuwa ya ratsa jikina. Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.

5 “Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya, In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne.

6 Amma wane ne zai iya cin abinci ba gishiri? Akwai daɗin ɗanɗano ga farin ruwan ƙwai?

7 Ba na jin marmarin cin abinci irin haka, Kowane irin abu da na ci yakan sa mini cuta.

8 “Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo? Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?

9 Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni, Ko ya sake ikonsa ya datse ni!

10 Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna, Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba. Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.

11 Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa? Wane sa zuciya kuma nake da ita, tun da na tabbata mutuwa zan yi?

12 Da dutse aka yi ni? Ko da tagulla aka yi jikina?

13 Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina, Ba inda zan juya in nemi taimako.

14 “A cikin irin wannan wahala Ina bukatar amintattun abokai, Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.

15 Amma ku abokaina,kun ruɗe ni, Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani.

16 Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara, Amma lokacin zafi sai su ɓace, Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.

17

18 Ayari sukan ɓata garin neman ruwa, Su yi ta gilo, har su marmace a hamada.

19 Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema,

20 Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka,

21 Kamar rafuffukan nan kuke a gare ni, Kun ga abin da ya same ni, kun gigita.

22 Na roƙe ku ku ba ni kyauta ne? Ko kuwa na roƙe ku ku ba wani rashawa domina?

23 Ko kuma na roƙe ku ku cece ni daga maƙiyi ko azzalumi ne?

24 “To, sai ku koya mini, ku bayyana mini laifofina, Zan yi shiru in kasa kunne gare ku.

25 Kila muhawara mai ma'ana ta rinjaye ni, Amma yanzu duk maganar shirme kuke yi.

26 Kuna so ku amsa maganganuna? Don me? Mutumin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi, Ba wata maganar da zai yi in ba shirme ba.

27 Kukan jefa wa bayi da marayu kuri'a, Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa.

28 Ku dubi fuskata, Lalle ba zan faɗi ƙarya ba.

29 Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci, Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya.

30 Amma duk da haka kuna tsammani ƙarya nake yi. Kuna tsammani ba zan iya rarrabe tsakanin gaskiya da ƙarya ba.”

7

1 “Kamar kamen soja na tilas, Haka zaman 'yan adam take, Kamar zaman mai aikin bauta.

2 Kamar bawa ne wanda yake sa zuciya ga inuwa mai sanyi, Kamar ma'aikaci wanda yake sa zuciya ga lokacin biya.

3 Wata da watanni ina ta aikin banza, Kowane dare ɓacin rai yake kawo mini.

4 Sa'ad da na kwanta barci, sai daren ya daɗa tsawo In yi ta jujjuyawa duk dare, in ƙosa gari ya waye.

5 Jikina cike yake da tsutsotsi, Ƙuraje duka sun rufe shi, Daga miyakuna mugunya tana ta zuba.

6 Kwanakina sun wuce ba sa zuciya, Sun wuce da sauri kamar ƙoshiyar saƙa.

7 “Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai, Farin cikina ya riga ya ƙare.

8 Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba. Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan.

9 Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi, Haka nan mutum yake mutuwa.

10 Ba kuwa zai ƙara komowa ba, Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.

11 A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba! Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci, Dole ne in yi magana.

12 “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi? Kana tsammani ni dodon ruwa ne?

13 Na kwanta ina ƙoƙari in huta, Ina neman taimako don azabar da nake sha.

14 Amma kai kana firgita ni da mafarkai, Kana aiko mini da wahayi da ganegane,

15 Har nakan fi so a rataye ni, Gara in mutu da in rayu a wannan hali.

16 Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa. Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.

17 “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka? Me ya sa kake lura da abin da yake yi?

18 Kakan dube shi kowace safiya. Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.

19 Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba, Don in samu in haɗiye yau?

20 Ko na yi zunubi ina ruwanka, Kai mai ɗaure mutane? Me ya sa ka maishe ni abin bārata? Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?

21 Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba? Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba? Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura, Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”

8

1 Sai Bildad ya yi magana.

2 “Ka gama maganganunka marasa kan gado duka?

3 Allah bai taɓa yin danniya ba, Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba.

4 Lalle 'ya'yanka sun yi wa Allah zunubi, Don haka ya hukunta su yadda ya cancanta.

5 Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki.

6 Idan kana da tsarki da aminci, Allah zai taimake ka, Ya maido da iyalin gidanka, ya yi maka sakayya.

7 Duk hasarar dukiyan nan da ka yi, ba kome ba ne In aka gwada da abin da Allah zai ba ka nan gaba.

8 “Ka tsai da zuciyarka a kan hikima irin ta zamanin dā. Ka kuma yi ta yin tunani a kan gaskiyar da kakanninmu suka koya.

9 Kwanakinmu 'yan kaɗan ne kawai, Ba mu san kome ba, Mu inuwa ne kawai a fuskar duniya.

10 Amma ka yarda masu hikima na zamanin dā su koya maka, Ka kasa kunne ga abin da za su faɗa.

11 “Iwa ba ta tsirowa inda ba ruwa, Ba a taɓa samunta a ko'ina ba sai a fadama.

12 In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa, Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.

13 Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke, Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah.

14 Suna dogara ga silin zare, murjin gizo-gizo.

15 Idan suka jingina ga saƙar gizo-gizo, za ta iya tokare su? Idan sun kama ta, za ta taimake su tsayawa?

16 “Mugaye sukan tsiro kamar ciyayi a hasken rana, Ciyayin da sukan yaɗu su cinye gona duka.

17 Saiwoyinsu sukan nannaɗe duwatsu, Su riƙe kowane dutse da ƙarfi.

18 Amma idan aka tumɓuke su, Ba wanda zai taɓa cewa sun kasance a wurin.

19 Hakika matuƙar murnar da mugaye suke da ita ke nan, Yanzu waɗansu ne za su zo su gāje wurarensu.

20 “Amma daɗai Allah ba zai rabu da amintattu ba, Ba kuwa zai taɓa taimakon mugun mutum ba.

21 Zai sāke barinka ka yi dariya ka ƙyalƙyata kamar dā, Ka kuma yi sowa da murna matuƙa.

22 Amma zai sa maƙiyanka su sha kunya, Za a shafe gidajen mugaye.”

9

1 Ayuba ya amsa.

2 “Ai, na taɓa jin waɗannan duka, Amma ta ƙaƙa mutum zai yi jayayya da Allah har ya yi nasara?

3 Ta ƙaƙa za ka iya jayayya da shi? Yana yiwuwa ya yi maka tambayoyi guda dubu Waɗanda ba wanda zai iya ba da amsarsu.

4 Allah mai hikima ne, mai iko, Ba wanda zai iya ja in ja da shi.

5 Yakan kawar da manyan duwatsu farat ɗaya, Ya hallaka su da fushinsa,

6 Allah yakan aiko da girgizar ƙasa, ya girgiza duniya, Yakan jijjiga ginshiƙan da duniya take zaune a kansu.

7 Allah yana da iko ya hana rana fitowa, Ko kuma ya hana taurari haskakawa da dare.

8 Ba wanda ya taimaki Allah shimfiɗa sammai, Wanda yake taka raƙuman ruwan teku, ya kuma kwantar da su.

9 Allah ya rataye taurari a sararin sama, Wato su mafarauci da kare da zomo, Da kaza da 'ya'yanta da taurarin kudu.

10 Ba shi yiwuwa mu gane manyan abubuwa da yake yi. Ayyukan al'ajabansa ba su da iyaka.

11 “Allah yana wucewa kusa da ni, Amma ba na ganinsa.

12 Yakan ɗauki abin da yake so, ba wanda yake hana shi, Ba wanda yake tambayarsa cewa, ‘Me kake yi?’

13 “Allah ba zai huce fushinsa ba. Ya murƙushe maƙiyansa waɗanda suka taimaki dodon ruwan nan da ake kira Rahab, wanda ya tayar masa.

14 To, ƙaƙa zan yi in samo kalmomin da zan amsa wa Allah?

15 Ko da yake ba ni da laifi, Duk da haka iyakar abin da zan iya yi ke nan, In roƙi Allah ya yi mini jinƙai, Shi da yake alƙalina.

16 Amma duk da haka ko ya yardar mini in yi magana ma, Ban yi tsammani zai saurare ni ba.

17 Shi ya aiko da hadura, suka yi kacakaca da ni, Suka ƙuƙƙuje ni, ga shi kuwa, ba wani dalilin da ya sa ya yi mini rauni.

18 Ya hana ni in ko shaƙata, Ina jin haushin dukan abin da yake yi mini.

19 In gwada ƙarfi ne? To, a iya gwada wa Allah ƙarfi? In kai shi ƙara ne? Wa zai sa shi ya je?

20 Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni, A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne. Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi.

21 Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa.

22 Don haka ban damu da kome ba. Da marar laifin da mai laifin duk, Allah zai hallaka mu.

23 Sa'ad da marar laifi ya mutu farat ɗaya, Allah yakan yi dariya.

24 Allah ya ba da duniya ga mugaye, Ya makantar da dukan alƙalai, Idan ba Allah ne ya yi haka nan ba, to, wa ya yi?

25 “Kwanakina suna shuɗewa da sauri, ba mai kyau ko ɗaya.

26 Raina na wucewa kamar jirgin ruwa mafi sauri, Da sauri ƙwarai kamar juhurma ya kai wa zomo sura.

27 Idan an yi murmushi, Ina ƙoƙari in manta da azabata,

28 Sai dukan wahalar da nake sha ta yi ta firgita ni, Na sani Allah ya ɗauke ni mai laifi.

29 Tun da yake Allah ya ɗauka, ni mai laifi ne, To, me zai sa in damu?

30 Ba sabulun da zai iya wanke zunubaina.

31 Allah ya jefa ni a kwatami, Har tufafina ma suna jin kunyata.

32 Da a ce Allah mutum ne, Da sai in mayar masa da magana, Da sai mun je ɗakin shari'a a yanka mana shari'a.

33 Amma ga shi, ba wanda zai shiga tsakaninmu, Ba wanda zai shara'anta tsakanina da Allah.

34 Ka daina hukunta ni, ya Allah! Ka daina razanar da ni.

35 Ba na jin tsoro, Zan yi magana, domin na san zuciyata.”

10

1 “Na gaji da rayuwa, Ku ji ina fama da baƙin ciki.

2 Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.

3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta? Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi? Sa'an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye?

4 Yadda mutane suke duban abu, haka kake duba?

5 Kai ma ranka gajere ne kamar namu?

6 In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina, Kana farautar dukan abin da na yi?

7 Ka sani, ba ni da laifi, Ka kuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka.

8 “Da ikonka ne ka yi ni, ka siffata ni, Yanzu kuma da ikon nan naka ne za ka hallaka ni.

9 Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni. Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?

10 Kai ne ka ba mahaifina ƙarfin da zai haife ni, Kai ne ka sa na yi girma a cikin cikin mahaifiyata.

11 Kai ne ka siffata jikina da ƙasusuwa da jijiyoyi, Ka rufe ƙasusuwan da nama, naman kuma ka rufe da fata.

12 Kai ne ka ba ni rai da madawwamiyar ƙauna, Kulawarka ce ta sa ni rayuwa.

13 Amma yanzu na sani, Dukan lokacin nan kana da wani nufi a ɓoye game da ni.

14 Jira kake ka ga ko zan yi zunubi, Don ka ƙi gafarta mini.

15 Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka. Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo. Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.

16 Da zan ci nasara a kan kowane abu, Da sai ka yi ta farautata kamar zaki, Kana aikata al'ajabai don ka cuce ni.

17 A koyaushe kakan karɓi shaida gāba da ni, Fushinka sai gaba gaba yake yi a kaina, Kakan yi mini farmaki a koyaushe.

18 “Ya Allah, me ya sa ka bari aka haife ni? Da ma na mutu tun kafin wani ya gan ni!

19 Da a ce daga cikin cikin mahaifiyata an wuce da ni zuwa kabari Da ya fi mini kyau bisa ga kasancewata.

20 Raina bai kusa ƙarewa ba? A bar ni kawai! Bari in ci moriyar lokacin da ya rage mini.

21 An jima kaɗan zan tafi, ba kuwa zan komo ba faufau, Zan tafi ƙasa mai duhu, inda ba haske,

22 Ƙasa mai duhu, da inuwoyi da ɗimuwa Inda ko haske ma kansa duhu ne.”

11

1 Zofar ya amsa.

2 “Ba wanda zai amsa dukan wannan surutu? Yawan magana yakan sa mutum ya zama daidai?

3 Ayuba,kana tsammani ba za mu iya ba ka amsa ba? Kana tsammani maganganunka na ba'a Za su sa mu rasa abin da za mu mayar maka?

4 Ka ɗauka duk abin da kake faɗa gaskiya ne, Ka kuma mai da kanka kai mai tsarki ne a gaban Allah.

5 Da ma Allah zai amsa maka, Ya yi magana gāba da kai,

6 Da ya faɗa maka hikima tana da fannoni da yawa. Akwai abubuwa waɗanda suka fi ƙarfin ganewar ɗan adam. Duba, Allah ya ƙyale wani ɓangare na laifinka.

7 “Kana iya gane matuƙa da iyakar Girman Allah da na ikonsa?

8 Sararin sama ba shi ne matuƙa a wurin Allah ba, Amma ga shi, yana can nesa da kai, Allah ya san lahira, Amma kai ba ka sani ba.

9 Fāɗin girman Allah ya fi duniya Ya kuma fi teku fāɗi.

10 Idan Allah ya kama ka ya gurfanar da kai gaban shari'a, Wa zai iya hana shi?

11 Allah ya san irin mutanen da ba su da amfani, Domin yana ganin dukan mugayen ayyukansu.

12 Idan dakikan mutane sa yi hikima, To, jakunan jeji ma sa yi irin hali na gida.

13 “Ayuba, ka shirya zuciyarka, Ka ɗaga hannuwanka zuwa wurin Allah.

14 Ka kawar da mugunta da kuskure daga gidanka.

15 Sa'an nan ka sāke shan ɗamarar zaman duniya, Da ƙarfi da rashin tsoro.

16 Duk wahalarka za ta gushe daga tunaninka, Kamar yadda rigyawa takan wuce, ba a ƙara tunawa da ita.

17 Ranka zai yi haske fiye da hasken rana da tsakar rana. Kwanakin ranka mafiya duhu Za su yi haske kamar ketowar alfijir.

18 Za ka yi zaman lafiya, cike da sa zuciya, Allah zai kiyaye ka, ya ba ka hutawa.

19 Ba za ka ji tsoron kowane maƙiyi ba, Mutane da yawa za su nemi taimako daga gare ka.

20 Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”

12

1 Ayuba ya amsa.

2 “Aha! Ashe, kai ne muryar jama'a, Idan ka mutu hikima ta mutu ke nan tare da kai.

3 Amma ni ma ina da hankali gwargwado, kamar yadda kake da shi, Ban ga yadda ka fi ni ba. Kowa ya san sukan abin da ka faɗa.

4 Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu, Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi, Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina.

5 Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya. Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa.

6 Amma ɓarayi da marasa tsoron Allah suna zaune cikin salama, Ko da yake ƙarfinsu ne kaɗai allahnsu.

7 “Don haka tsuntsaye da dabbobi sun fi ka sani, Suna da abu mai yawa da za su koya maka.

8 Ka roƙi talikan da suke a duniya, da cikin teku, hikimar da suke da ita.

9 Dukansu sun sani ikon Ubangiji ne ya yi su.

10 Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa. Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake.

11 Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci, Haka nan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi.

12 “Tsofaffi suna da hikima, Amma Allah yana da hikima da iko. Tsofaffi suna da tsinkaya, Amma Allah yana da tsinkaya da ikon aikatawa.

13

14 Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa? Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku?

15 Akan yi fari sa'ad da Allah ya hana ruwan sama, Rigyawa takan zo sa'ad da ya kwararo ruwa.

16 Allah mai iko ne a kullum kuwa cikin nasara yake Da macuci, da wanda aka cutar, duk ƙarƙashin ikon Allah suke.

17 Yakan mai da hikimar masu mulki wauta, Yakan mai da shugabanni marasa tunani.

18 Yakan tuɓe sarakuna ya sa su kurkuku.

19 Yakan ƙasƙantar da firistoci da mutane masu iko.

20 Yakan rufe bakin waɗanda aka amince da su. Yakan kawar da hikimar tsofaffi.

21 Yakan kunyatar da masu iko, Ya hana wa masu mulki ƙarfi.

22 Yakan aika da haske a wuraren da suke da duhu kamar mutuwa.

23 Yakan sa sauran al'ummai su yi ƙarfi su ƙasaita, Sa'an nan ya fatattaka su, ya hallaka su.

24 Yakan sa shugabanninsu su zama wawaye, Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata,

25 Su yi ta lalube cikin duhu, su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.”

13

1 “Duk abin da ka hurta, na taɓa jinsa, Na gane da shi sarai. Iyakar abin da kuka sani, ni ma na sani. Ba ku fi ni da kome ba.

2

3 Amma da Allah nake jayayya, ba da ku ba, Ina so in yi muhawara da shi a kan ƙarar da nake da ita.

4 Kun ɓoye jahilcinku da ƙarairayi. Kun zama kamar likitoci waɗanda ba su iya warkar da kowa ba.

5 Kada ku faɗi kome, Wani sai ya ce kuna da hikima!

6 “Ku saurara mini, zan faɗi ƙarata.

7 Me ya sa kuke yin ƙarya? Kuna tsammani ƙarairayinku za su taimaki Allah?

8 Son zuciya kuke yi, ko ba haka ba? Kuna goyon bayan Allah? Za ku goyi bayan Allah sa'ad da aka gurfanar da ni gaban shari'a?

9 Da Allah ya bincike ku sosai, Zai iske wani abin kirki ne a cikinku? Kuna tsammani za ku ruɗi Allah, kamar yadda kuke ruɗin mutane?

10 Ko da yake kun ɓoye son zuciyarku, Duk da haka zai tsauta muku,

11 Ikonsa kuwa zai razana ku.

12 Karin maganarku da muhawararku ba su da ƙarfi ƙwarai.

13 “Ku yi shiru ku ba ni zarafi in yi magana. Duk abin da zai faru, ya faru.

14 A shirye nake in yi kasai da raina.

15 Na fid da zuciya ɗungum. To, in Allah ya kashe ni, sai me? Zan faɗa masa ƙarata.

16 Mai yiwuwa ne ƙarfin halina ya cece ni, Tun da yake ba wani mugun mutumin da zai iya zuwa gaban Allah.

17 Sai a saurari bayanin da zan yi.

18 A shirye nake in faɗi ƙarata, Domin na sani ina da gaskiya.

19 “Ya Allah, za ka yi ƙarata? Idan kuwa ka yi, to, a shirye nake in yi shiru in mutu.

20 Ina da abu biyu da zan yi maka roƙo, Ka yarda da su, sa'an nan ba zan yi ƙoƙari in ɓoye ba.

21 Wato ka daina hukuncin da kake yi mini, Kada ka sa razanarka ta ragargaza ni.

22 “Ka fara yin magana, ya Allah, ni kuwa zan amsa. Ko kuma ka bari in yi magana, sa'an nan ka amsa mini.

23 Kuskure da laifi guda nawa na yi? Waɗanne irin laifofi ake tuhumata da su?

24 Me ya sa kake guduna? Me ya sa ka maishe ni kamar maƙiyi?

25 Ƙoƙari kake ka firgita ni? Ni ba wani abu ba ne, ganye ne kawai, Ka fāɗa wa tattaka da yaƙi ne kawai.

26 Ka kawo mugayen ƙararraki a kaina, Har da laifofin da na yi na ƙuruciya.

27 Ka ɗaure ƙafata da sarƙoƙi, Kakan lura da kowace takawata, Har kana bin diddigin sawayena.

28 Saboda wannan na zama abin kallo, ni kuwa kamar ragargazajjen itace ne, ko diddigaggiyar riga.”

14

1 “Mutum duka kwanakin ransa gajere ne, kwanakin wahala kuwa.

2 Sukan yi girma su bushe nan da nan kamar furanni, Sukan shuɗe kamar inuwa.

3 Na ma isa ka dube ni ne, ya Allah? Ko ka gabatar da ni a gabanka, Ka yi mini shari'a?

4 Ba wani abu tsarkakakke Da zai fito daga cikin kowane marar tsarki, kamar mutum.

5 Tsawon kwanakin ransa, an ƙayyade su tun can, An ƙayyade yawan watannin da zai yi, Ka riga ka yanke haka ya Allah, ba su sākuwa.

6 Ka kawar da fuska daga gare shi, ka rabu da shi, Ka bar shi ya ji daɗin kwanakinsa na fama da aiki idan zai iya.

7 “Akwai sa zuciya ga itacen da aka sare, Yana iya sāke rayuwa ya yi toho.

8 Ko da yake saiwoyinsa sun tsufa, Kututturensa kuma ya ruɓe a ƙasa,

9 In aka zuba ruwa, sai ya toho kamar sabon tsiro.

10 Amma ɗan mutum ya mutu, ƙarshensa ke nan, Ya mutu, a ina yake a lokacin nan?

11 “Mai yiwuwa ne koguna za su daina gudu, Har tekuna kuma su ƙafe.

12 Amma matattu ba za su tashi ba daɗai, Ba za su ƙara tashi ba sam, muddin sararin sama na nan. Sam, ba za a dame su cikin barcinsu ba.

13 “Ya Allah, da ma a ce ka ɓoye ni a lahira, Ka bar ni a ɓoye, har fushinka ya huce, Sa'an nan ka sa lokacin da za ka tuna da ni!

14 Idan mutum ya mutu, zai sāke rayuwa kuma? Amma zan jira lokaci mafi kyau, In jira sai lokacin wahala ya wuce.

15 Sa'an nan za ka yi kira, ni kuwa zan amsa, Za ka yi murna da ni, ni talikinka.

16 Sa'an nan za ka lura da kowace takawata Amma ba za ka bi diddigin zunubaina ba.

17 Za ka soke zunubaina ka kawar da su, Za ka shafe dukan kurakuran da na taɓa yi.

18 “Lokaci na zuwa sa'ad da duwatsu za su fāɗi, Har ma za a kawar da duwatsun bakin teku.

19 Ruwa zai zozaye duwatsu, su ragu, Ruwan sama mai ƙarfi zai kwashe jigawa, Kai ma ka bar mutane, ba su da sauran sa zuciya ko kaɗan.

20 Ka fi ƙarfin mutum, ka kore shi har abada, Fuskarsa ta rikiɗe sa'ad da ya mutu.

21 'Ya'yansa maza za su sami girma, amma sam, ba zai sani ba, Sam, ba wanda zai faɗa masa sa'ad da aka kunyatar da su.

22 Ciwon jikinsa da ɓacin zuciyarsa kaɗai yake ji.”

15

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Surutai, Ayuba! Surutai!

3 Ba wani mai hikima wanda zai yi magana irin taka, Ko kuma ya kāre kansa da irin maganganun da ba su da ma'ana.

4 Kana karya jama'a, kana hana su jin tsoron Allah, Kana hana su yin addu'a gare shi.

5 Mugun lamirinka shi ne yake magana yanzu, Kana ƙoƙari ka ɓuya a bayan maganganunka na wayo.

6 Ba na bukata in kā da kai, Kowace kalma da ka hurta ta kā da ka.

7 “Kana tsammani kai ne mutumin da aka haifa na farko? Sa'ad da Allah ya yi duwatsu kana nan?

8 Ko ka taɓa jin shirye-shiryen da Allah ya yi? Ko kai kaɗai kake da hikima a cikin mutane?

9 Ba wani abu da ka sani da mu ba mu sani ba.

10 Daga wurin mutanen da suka yi furfura muka koyi hikimarmu. Mun koyi hikimarmu daga mutane waɗanda aka haife su Tun kafin a haifi mahaifinka.

11 “Allah yana ta'azantar da kai, Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi? Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi.

12 Amma ka ta da hankalinka, Kana ta zazzare mana ido da fushi.

13 Fushi kake yi da Allah, kana ƙinsa.

14 Akwai mutumin da yake tsarkakakke sarai? Akwai mutumin da yake cikakke a wurin Allah?

15 Me ya sa Allah bai sakar wa mala'ikunsa kome ba? Har su ma ba tsarkaka suke a gare shi ba.

16 Mutum yakan sha mugunta kamar yadda yake shan ruwa, Hakika mutum ya lalace, ya zama mai rainako.

17 “Yanzu ka saurara, ya Ayuba, ga abin da na sani.

18 Mutane masu hikima sun koya mini gaskiya Wadda suka koya daga wurin kakanninsu, Ba su kuwa ɓoye mini asirin kome ba.

19 Ƙasaru 'yantacciya ce daga baƙi Ba wanda zai raba su da Allah.

20 “Mugun mutum mai zaluntar sauran mutane Zai kasance da wahala muddin ransa.

21 Zai ji ƙarar muryoyi masu firgitarwa a kunnuwansa. 'Yan fashi za su fāɗa masa Sa'ad da yake tsammani ba abin da zai same shi.

22 Bai sa zuciya zai kuɓuta daga duhu ba, Gama takobi yana jiransa a wani wuri don ya kashe shi.

23 Yana ta yawon neman abinci, yana ta cewa, ‘Ina yake?’ Ya sani baƙin ciki ne yake jiransa a nan gaba. Kamar sarki mai iko,

24 Haka masifa take shirin fāɗa masa.

25 “Wannan shi ne ƙaddarar mutum, Wanda ya nuna wa Allah yatsa, Ya kuwa raina Mai Iko Dukka.

26 Wannan mutum mai girmankai ne, ɗan tawaye.

27 Ya ɗauki garkuwarsa kamar ɗan yaƙi, Ya ruga don ya yi yaƙi da Allah.

28 Shi ne mutumin da ya ci birane da yaƙi, Ya ƙwace gidajen waɗanda suka tsere, Amma yaƙi ne zai hallaka birane da gidaje.

29 Arzikinsa ba zai daɗe ba, Duk abin da ya mallaka ba zai daɗe ba. Har inuwarsa ma za ta shuɗe,

30 Ba kuwa zai kuɓuta daga duhu ba. Zai zama kamar itacen da wuta ta ƙone rassansa, Kamar itace kuma da iska ta kaɗe furensa.

31 Idan wauta tasa ta kai shi ga dogara ga mugunta, To, mugunta ce kaɗai zai samu.

32 Kafin kwanakinsa su cika zai bushe, Zai bushe kamar reshe, ba zai ƙara yin ganye ba.

33 Zai ama kamar itacen inabi Wanda 'ya'yansa suka kakkaɓe tun kafin su nuna, Kamar itacen zaitun wanda bai taɓa yin 'ya'ya ba.

34 Marasa tsoron Allah ba za su sami zuriya ba, Wuta za ta cinye gidajen da aka gina da dukiyar rashawa.

35 Waɗannan su ne irin mutanen da suke shirya tarzoma, su aikata mugunta. Kullum zuciyarsu cike take da ruɗarwa.”

16

1 Ayuba ya yi magana.

2 “Ai, na taɓa jin magana irin wannan, Ta'aziyyar da kake yi azaba ce kawai.

3 Ka dinga yin magana ke nan har abada? A kullum maganarka ita ce dahir?

4 In da a ce a matsayina kake, ni kuma ina a naka, Ina iya faɗar duk abin da kake faɗa yanzu. Da sai in kaɗa kaina da hikima, In dulmuyar da kai a cikin rigyawar maganganu.

5 Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa, In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa.

6 “Amma ba abin da zan faɗa wanda zai taimaka, Yin shiru kuma ba zai raba ni da azaba ba.

7 Ka gajiyar da ni, ya Allah, Ka shafe iyalina.

8 Ka kama ni, kai maƙiyina ne. Na zama daga fata sai ƙasusuwa, Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne.

9 Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa, Yana dubana da ƙiyayya.

10 Mutane sun buɗe baki don su haɗiye ni Suna kewaye ni suna ta marina.

11 Allah ya bashe ni ga mugaye.

12 Dā ina zamana da salama, Amma Allah ya maƙare ni, Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni. Allah ya maishe ni abin bārata.

13 Ya harbe ni da kibau daga kowane gefe. Kiban sun ratsa jikina sun yi mini rauni, Duk da haka bai nuna tausayi ba!

14 Ya yi ta yi mini rauni a kai a kai, Ya fāɗa mini kamar soja da ƙiyayya ta haukata.

15 “Ina makoki saye da tsummoki, Ina zaune cikin ƙura a kunyace.

16 Na yi ta kuka har fuskata ta zama ja wur, Idanuna kuma suka yi luhuluhu.

17 Amma ban yi wani aikin kama-karya ba, Addu'ata ga Allah kuwa ta gaskiya ce.

18 “Duniya, kada ki ɓoye laifofin da aka yi mini! Kada ki yi shiru da roƙon da nake yi na neman adalci!

19 Akwai wani a Sama Wanda zai tsaya mini ya goyi bayana.

20 Ina so Allah ya ga hawayena, Ya kuma ji addu'ata.

21 “Ina so wanda zai yi roƙo ga Allah domina, Kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.

22 Yanzu shekaruna wucewa suke yi, Ina bin hanyar da ba a komawa.”

17

1 “Ƙarshen raina ya gabato, da ƙyar nake numfashi, Ba abin da ya rage mini sai kabari.

2 Na lura da yadda mutane suke yi mini mummunar ba'a.

3 Ni amintacce ne, ya Allah, ka yarda da maganata. Ba wanda zai goyi bayan abin da nake faɗa.

4 Ka baƙantar da hankalinsu, ya Allah, Kada ka bar su su yi mini duban wulakanci yanzu.

5 A karin maganar mutanen dā an ce, ‘Kowa ya ci amanar abokinsa saboda kuɗi, 'Ya'yansa sā sha wahala!’

6 Yanzu kuwa sun mai da wannan karin magana a kaina. Da mutane suka ji, Suka zo suka yi ta tofa mini yau a fuska.

7 Baƙin cikina ya kusa makantar da ni, Hannuwana da ƙafafuna sun rame, sun zama kamar kyauro.

8 Duk waɗanda suka zaci su adalai ne sun razana. Dukansu sun kāshe ni, cewa ni ba mai tsoron Allah ba ne.

9 Har su ma da suke cewa su mutanen kirki ne Suna ƙara tabbatarwa ba su yi kuskure ba.

10 Amma da a ce dukansu za su zo su tsaya a gabana, Da ba zan sami mai hikima ko ɗaya daga cikinsu ba.

11 “Kwanakina sun ƙare, shirye-shiryena sun kāsa, Ba ni da sauran sa zuciya.

12 Amma abokaina sun ce dare shi ne hasken rana, Sun kuma ce haske yana kusa, Ko da yake ina cikin duhu.

13 Ba ni da sauran sa zuciya, Gidana yana lahira, Inda zan kwanta in yi ta barci cikin duhu.

14 Zan ce kabari shi ne mahaifina, Tsutsotsin da suke cinye ni su ne mahaifiyata, da 'yan'uwana mata.

15 Ina ne zan sa zuciyata? Wane ne ya ga inda zan sa ta?

16 Akwai wanda ya yi shiri a binne shi tare da ni, Mu tafi tare da shi zuwa lahira?”

18

1 Bildad ya amsa.

2 “Ayuba, mutane kamarka sun taɓa yin shiru? Da ka yi ƙoƙari ka kasa kunne da mun yi magana da kai.

3 Me ya sa kake tsammani mu dakikai ne kamar shanu?

4 Cutar kanka kake yi saboda fushin da kake ji. Duniya za ta ƙare ne sabili da kai? Za a kawar da duwatsu sabili da kai?

5 “Za a kashe hasken mugun mutum, Harshen wutarsa ba zai ƙara ci ba.

6 Fitilar da take cikin alfarwarsa ba za ta ba da haske ba.

7 A dā gagau yake tafiya, amma yanzu ɗingishi yake yi, Shawararsa ta kāshe shi.

8 Yana tafiya, sai ya fāɗa cikin tarko. Tarkon ya kama ƙafafunsa.

9 Tarko ya kama diddigensa ya riƙe shi,

10 An binne masa tarko a ƙasa, An kafa masa tarko a hanyarsa.

11 “Kewaye da shi duka razana tana jiransa, Duk inda ya nufa tana biye da shi,

12 Dā attajiri ne, amma yanzu ya talauce, Kusa da shi bala'i na tsaye yana jiransa.

13 Mummunan ciwo ya bazu ko'ina a jikinsa, Yana sa hannuwansa da ƙafafunsa su ruɓe,

14 Dā yana zaune lafiya, Sai razana ta tatike shi, Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa.

15 Yanzu kowa zai iya zama a alfarwarsa, Bayan da an karkashe ƙwayoyin cuta da farar wuta.

16 Saiwoyinsa da rassansa suka yi yaushi suka bushe.

17 Sunansa ya ƙare a gida da a jeji, Ba wanda yake ƙara tunawa da shi.

18 Za a kore shi daga ƙasar masu rai, Za a kore shi daga haske zuwa duhu.

19 Ba shi da zuriya, da sauran waɗanda suka ragu da rai.

20 Daga gabas zuwa yamma, duk wanda ya ji labarin ƙaddarar da ta same shi, Zai yi makyarkyata, ya yi rawar jiki don tsoro.

21 Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wannan ita ce ƙaddarar mutane waɗanda ba su damu da kome na Allah ba.”

19

1 Ayuba ya amsa.

2 “Me ya sa kuke azabta ni da maganganu?

3 A kowane lokaci kuna wulakanta ni, Ba kwa jin kunya yadda kuke zagina.

4 Da a ce ma na aikata abin da yake ba daidai ba ne, Da me ya cuce ku?

5 Tsammani kuke kun fi ni ne, Kuna ɗauka cewa wahalar da nake sha Ta tabbatar ni mai laifi ne.

6 Ba ku iya ganin abin da Allah ya yi mini, Ya kafa tarko don ya kama ni.

7 Na ce ban yarda da kama-karyarsa ba, Amma ba wanda ya kasa kunne. Na nema a aikata gaskiya, amma sam, babu.

8 Allah ya rufe hanya, na kasa wucewa, Ya rufe hanyata da duhu,

9 Gama ya kwashe dukiyata duka, Ya ɓata mini suna.

10 Ya mammangare ni, Ya tumɓuke sa zuciyata, Ya bar ni in yi yaushi, in mutu.

11 Allah ya zaburo mini da fushi, Ya maishe ni kamar mafi mugunta daga cikin maƙiyansa.

12 Ya aiko da rundunar sojansa don ta fāɗa mini, Suka haƙa ramummuka kewaye da alfarwata inda za su yi kwanto.

13 “'Yan'uwana sun yashe ni, Na zama baƙo ga idon sanina.

14 Dangina da abokaina sun tafi.

15 Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni. Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa.

16 Sa'ad da na kira barana, ba ya amsawa, Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni.

17 Har matata ma ba ta iya jurewa da ɗoyin numfashina, 'Yan'uwana maza kuwa ba su ko zuwa kusa da ni.

18 'Yan yara sukan raina ni su yi mini dariya sa'ad da suka gan ni.

19 Aminaina na kusa sukan dube ni, duban ƙyama, Waɗanda na fi ƙaunarsu duka sun zama maƙiyana.

20 Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi, Da ƙyar na kuɓuta.

21 Ku abokaina ne! Ku ji tausayina! Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.

22 Me ya sa kuke ɓata mini rai kamar yadda Allah ya yi? Azabar da kuka yi mini har yanzu ba ta isa ba?

23 “Da ma a ce wani zai rubuta abin da nake faɗa, Ya rubuta shi a littafi!

24 Ko kuwa ya zana kalmomina da kurfi a kan dutse, Ya rubuta su don su tabbata har abada!

25 Amma na sani akwai wani a Samaniya Wanda a ƙarshe zai zo ya tsaya mini.

26 Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata, A wannan jiki zan ga Allah.

27 Zan gan shi ido da ido, Ba kuwa zai zama baƙo a gare ni ba. “Zuciyata ta karai saboda ku mutane kun ce,

28 ‘Ta ƙaƙa za mu yi masa azaba?’ Kuna neman sanadin da za ku fāɗa mini.

29 Amma yanzu, sai ku ji tsoron takobi, Ku ji tsoron takobin da yake kawo hasalar Allah a kan zunubi. Don haka za ku sani akwai wani mai yin shari'a.”

20

1 Zofar ya amsa.

2 “Ayuba, ka ɓata mini rai, Ba zan yi haƙuri ba, sai na ba ka amsa.

3 Abin da ka faɗa raini ne, Amma na san yadda zan ba ka amsa.

4 “Hakika ka sani tun daga zamanin dā, Sa'ad da aka fara sa mutum a duniya,

5 Ba wani mugun mutum wanda ya taɓa daɗewa da farin ciki.

6 Mai yiwuwa ne ya ƙasaita, ya zama kamar hasumiya a sararin sama. Ya ƙasaita har kansa ya taɓa gizagizai.

7 Amma zai shuɗe kamar ƙura. Waɗanda dā suka san shi, Za su yi mamaki saboda rashin sanin inda ya tafi.

8 Zai ɓace kamar mafarki, kamar wahayi da dad dare, Ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.

9 Ba za a ƙara ganinsa a wurin zamansa ba.

10 Tilas 'ya'yansa maza su biya zambar da ya yi wa matalauta, Tilas hannuwansa su biya dukiyar da ya ƙwace.

11 Ko da yake gagau yake, ma'aikaci ne kuma sa'ad da yake yaro, Duk da haka ba da jimawa ba, zai zama ƙura.

12 Ɗanɗana mugunta yana da daɗi a gare shi ƙwarai, Yakan sa wata a bakinsa don ya riƙa jin daɗin tsotsanta.

13

14 Amma a cikinsa wannan abinci yakan zama da ɗaci, Ɗacinsa kamar na kowane irin dafi mai ɗaci ne.

15 Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba, Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa.

16 Abin da mugu ya haɗiye kamar dafi yake, Yakan kashe shi kamar saran maciji mai mugu dafi.

17 Zai mutu bai ga kogunan man zaitun ba, Ba kuwa zai ga rafuffukan da suke da yalwar albarka ba.

18 Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa. Ba dama ya mori dukiyarsa,

19 Saboda zalunci da rashin kula da matalauta, Da ƙwace gidajen da waɗansu suka gina.

20 “Har abada ba zai kai ga samun abin da yake wahala ba.

21 Sa'ad da ya ci ba zai yi saura ba, Gama yanzu dukiyarsa ta ƙare.

22 A lokacin da yake gaɓar samunsa, Baƙin ciki mai nauyin gaske zai ragargaza shi.

23 Bari ya ci duk irin abin da yake so! Allah zai hukunta shi da hasala da fushi.

24 Lokacin da yake ƙoƙari ya kuɓuta daga takobin baƙin ƙarfe, Za a harbe shi da bakan tagulla ya fāɗi warwar.

25 Kibiya za ta kafe a jikinsa Tsininta zai yi ta ɗiɗɗiga da jini, Razana ta kama zuciyarsa.

26 Aka hallaka dukan abin da ya tattara, Wutar da ba hannun mutum ya kunna ba Ta ƙone shi, shi da iyalinsa duka.

27 Samaniya ta bayyana zunubin wannan mutum, Duniya kuma ta ba da shaida gāba da shi.

28 Dukan dukiyarsa za a hallaka ta a rigyawar fushin Allah.

29 “Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wadda Allah ya ƙayyade musu.”

21

1 Ayuba ya amsa.

2 “Ku kasa kunne ga abin da nake faɗa, Wannan ita ce ta'aziyyar da nake nema a gare ku.

3 Ku ba ni zarafi in yi magana, sa'an nan in na gama ku amsa in kun ga dama.

4 “Ba da 'yan adam nake faɗa ba, Ina da isasshen hanzarin da zai sa in yi fushi.

5 Ku dube ni, ashe, wannan bai isa ya sa ku yi zuru, Ku firgita, ku yi shiru ba?

6 Sa'ad da na tuna da abin da ya same ni, Sai jikina ya yi suwu, in yi ta makyarkyata ina rawar jiki.

7 Me ya sa Allah yake barin mugaye Har su tsufa su kuma yi arziki?

8 'Ya'yansu da jikokinsu sukan girma a idonsu.

9 Allah bai taɓa aukar wa gidajensu da bala'i ba, Ba su taɓa zama a razane ba.

10 Hakika shanunsu suna ta hayayyafa, Suna haihuwa ba wahala.

11 'Ya'yansu suna guje-guje, Suna tsalle kamar 'yan raguna,

12 Suna rawa ana kaɗa garaya, Ana busa sarewa.

13 Suka yi zamansu da salama, Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba.

14 Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum, Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.

15 Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah, Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida.

16 Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara, Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.

17 “An taɓa kashe hasken mugun mutum? Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu? Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi,

18 Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa? Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa?

19 “Kukan ce Allah yakan hukunta yaro saboda zunuban mahaifinsa. A'a! Allah dai yakan hukunta wa masu zunubi. Ya kuma nuna ya yi haka saboda zunubansu ne.

20 Bari dai a hukunta masu zunubi Su kuma ga hasalar Allah.

21 Bayan rasuwar mutum, Ruwansa ne ya sani ko 'ya'yansa suna jin daɗi?

22 Mutum zai iya koya wa Allah? Mutum zai iya shara'anta wa Allah Mai Iko Dukka?

23 “Waɗansu mutane sukan yi zamansu ba ciwon kome har ranar mutuwarsu, Suna cikin farin ciki da jin daɗi,

24 Jikunansu kuwa sun yi ɓulɓul.

25 Waɗansu kuwa ba su taɓa sanin farin ciki ba. Sukan yi dukan kwanakinsu su mutu da baƙin ciki.

26 Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne, Tsutsotsi su lulluɓe su duka.

27 “Na san irin tunaninku na hassada,

28 Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu, Wato mutumin da yake aikata mugunta?’

29 “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba? Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?

30 A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci, A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.

31 Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun, Ko ya mayar masa da martani.

32 Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi, A inda ake tsaron kabarinsa,

33 Dubban mutane sukan tafi wurin jana'izarsa, Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali.

34 “Amma ku, ƙoƙari kuke yi ku ta'azantar da ni da maganganun banza. Duk abinda kuka faɗa ƙarya ne!”

22

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Akwai wani mutum, ko mafi hikima, Wanda zai amfani Allah?

3 Gaskiyar da kake yi za ta amfani Allah? Ko kuwa abin kirki da kake yi zai taimake shi?

4 Ai, ba don tsoron Allah da kake yi ba ne, Ya sa wannan tsautawa da jarrabawa suka same ka.

5 Ko kusa ba haka ba ne, Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne. Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata.

6 Don ka sa ɗan'uwanka ya biya ka bashin da kake binsa, Ka ƙwace tufafinsa, ka bar shi huntu.

7 Ka hana wa waɗanda suke ji ƙishi ruwan sha, Ka hana waɗanda suke jin yunwa abinci.

8 Ka mori ikonka da matsayinka, Don ka mallaki dukan ƙasar.

9 Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba, Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su.

10 Don haka ne yanzu akwai ramummuka ko'ina kewaye da kai, Tsoro ya kama ka nan da nan.

11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, Rigyawa ta sha kanka.

12 “Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba? Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne.

13 Duk da haka ka ce, ‘Allah bai san kome ba. Gizagizai sun lulluɓe shi, ƙaƙa zai iya yi mana shari'a?’

14 Kana tsammani gizagizai masu duhu sun hana shi gani, A lokacin da yake tafiya a kan iyakar da take tsakanin duniya da sararin sama.

15 “Ka ɗauka a ranka ka bi gurbin da mugaye suke bi kullum?

16 Kafin ma su kai ga kwanakinsu, Sai rigyawa ta shafe su.

17 Su ne mutanen da suka ƙi Allah, Suka kuwa gaskata ba shi da ikon yi musu kome,

18 Ko da yake Allah ne ya arzuta su. Ba na iya gane tunanin mugaye.

19 Mutanen kirki suna murna, Marasa laifi kuma suna dariya Sa'ad da suka ga ana hukunta mugaye.

20 Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka, Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu.

21 “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah, Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka, In ka yi haka, to, za ka sami albarka.

22 Ka karɓi koyarwar da yake yi, Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.

23 Hakika sai ka yi tawali'u, ka koma wurin Allah, Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka.

24 Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau, Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura.

25 Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka, Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka.

26 Sa'an nan za ka dogara ga Allah kullayaumin, Ka kuma tarar shi ne asalin farin cikinka.

27 Sa'ad da ka yi addu'a zai amsa maka, Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi.

28 Za ka yi nasara a kowane abu da za ka yi, Haske kuma zai haskaka hanyarka.

29 Allah yakan ƙasƙantar da mai girmankai, Yakan ceci mai tawali'u.

30 Zai ceci wanda yake da laifi, Idan abin da kake yi daidai ne.”

23

1 Ayuba ya amsa.

2 “Duk da haka zan yi tawaye in yi wa Allah gunaguni, In dinga yin nishi.

3 Da ma na san inda zan same shi, In kuma san yadda zan kai wurinsa,

4 Da zan kai ƙarata a gare shi, in faɗa masa duk muhawarata, in kāre kaina ne.

5 Ina so in san irin amsar da zai mayar mini, Ina kuma so in san yadda zai amsa mini.

6 Allah kuwa da dukan ƙarfinsa zai yi gāba da ni? A'a, zai saurara in na yi magana.

7 Ina da aminci, zan faɗa wa Allah ra'ayina, Zai tabbatar da amincina duka.

8 “Na nemi Allah a gaba, amma ban same shi a can ba, Ban kuwa same shi a baya ba sa'ad da na neme shi.

9 Allah ya tafi wurin aiki a dama, Ya kuma tafi hagu, amma har yanzu ban gan shi ba.

10 Duk da haka Allah ya san kowane irin hali da nake ciki. Idan ya jarraba ni zai tarar ni tsattsarka ne.

11 Da aminci ina bin hanyar da ya zaɓa, Ban kuwa taɓa kaucewa daga wannan gefe zuwa wancan ba.

12 A kullum ina aikata abin da Allah ya umarta, Ina bin nufinsa, ba nufin kaina ba.

13 “Bai taɓa sākewa ba. Ba wanda zai iya gāba da shi, Ko kuma ya hana shi yin abin da yake so ya aikata.

14 Zai tabbatar da abin da ya shirya domina, Wannan ma ɗaya daga cikin shirye-shiryen da ya yi ne.

15 Don haka in rawar jiki a gabansa saboda tsoro.

16 Allah Mai Iko Dukka ya lalatar da ƙarfin halina. Allah ne ya tsorata ni,

17 Amma ban damu da damu ba, Ko da yake duhu ya dunɗe idanuna.”

24

1 “Me ya sa Allah bai tsai da ranar da zai yi shari'a ba? Me ya sa ba ya tsai da ranar adalci ga Waɗanda suka bauta masa?

2 Mugaye sukan ci iyaka, Don su ƙara yawan gonarsu. Sukan saci tumaki su zuba cikin garkunansu.

3 Sukan saci jakunan marayu, Su kama san gwauruwa, Su ce sai ta biya basusuwanta.

4 Sukan hana matalauta samun halaliyarsu, Sukan tilasta wa masu bukata su gudu su ɓuya.

5 Kamar jakunan jeji waɗanda sukan nemi abinci a busasshen jeji, Haka matalauta suke, Ba inda za su iya samo wa 'ya'yansu abinci.

6 Ya zama tilas a gare su su girbe gonakin da ba nasu ba, Su tattara 'ya'yan inabi daga gonakin mugaye.

7 Da dare sukan kwanta, ba su da abin rufa, Ba su da abin da zai hana su jin sanyi.

8 Sukan jiƙe sharkaf da ruwan sama wanda yake kwararowa daga kan duwatsu. Sun takure a gefen duwatsu neman mafaka.

9 “Mugaye sukan bautar da yara marayu, Sukan kama 'ya'ya matalauta a bakin bashin da suke bi.

10 Amma tilas matalauta su fita huntaye, ba sa da abin sutura. Tilas su girbi alkama suna kuwa jin yunwa.

11 Suna matse mai daga 'ya'yan zaitun. Suna kuma matse ruwan inabi daga 'ya'yan inabi, Amma su kansu suna fama da ƙishi.

12 Kana jin kukan waɗanda suka yi rauni da Waɗanda suke baƙin mutuwa a birni, Amma Allah bai kula da addu'o'insu ba.

13 “Akwai mugaye waɗanda suke ƙin haske, Ba su fahimce shi ba, suka ƙi bin hanyarsa.

14 Da asuba mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci, Da dare kuma ya yi fashi.

15 Mazinaci yakan jira sai da magariba, Sa'an nan ya ɓoye fuskarsa don kada a gane shi.

16 Da dare ɓarayi sukan kutsa kai cikin gidaje, Amma da rana sukan ɓuya, su guje wa haske.

17 Gama tsananin duhu kamar safiya yake gare su, Sun saba da razanar duhu.

18 “Rigyawa takan ci mugun mutum, Ƙasar da ya mallaka kuwa tana ƙarƙashin la'anar Allah. Ba ya kuma iya zuwa aiki a gonar inabinsa.

19 Kamar dusar ƙanƙara take a lokacin zafi da a lokacin fari, Haka mai zunubi yakan shuɗe daga ƙasar masu rai.

20 Ba wanda zai tuna da shi, mahaifiyarsa ma ba za ta lura da shi ba. Tsutotsi sukan ci shi su hallaka shi sarai. Za a sare mugunta kamar itace.

21 Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye. Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba.

22 Allah, da ikonsa, yakan hallaka masu ƙarfi, Allah yakan aikata, sai mugun mutum ya mutu.

23 Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya, Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa.

24 Mugun mutum yakan ci nasara ɗan lokaci, Daga nan sai ya yi yaushi kamar tsiro, Ya yi yaushi kamar karan dawa da aka yanke.

25 Akwai wanda zai iya cewa, ba haka ba ne? Akwai wanda zai tabbatar da cewa kalmomina ba gaskiya ba ne?”

25

1 Bildad ya amsa.

2 “Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa, A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama.

3 Akwai wanda zai iya ƙidaya mala'ikun da suke masa hidima? Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?

4 Akwai wanda ya isa ya zama adali, Ko mai tsarki a gaban Allah?

5 Hasken wata ba haske ba ne a gare shi, Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa.

6 To, mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah?”

26

1 Ayuba ya amsa.

2 “Kai ne mai taimakon marar ƙarfi, Kai ne mai ceton rarrauna!

3 Kai ne kake ba marar hikima shawara, Kai kake sanar da ilimi mai ma'ana a wadace!

4 Kana tsammani wane ne zai ji maganganunka duka? Wane ne ya iza ka ka yi irin wannan magana?

5 “Lahira tana rawa, Mazaunanta suna rawar jiki don tsoro.

6 Lahira tsirara take a gaban Allah, Haka kuma Halaka take a gaban Allah.

7 Allah ne ya shimfiɗa arewa a sarari kurum, Ya rataya duniya ba bisa kan kome ba.

8 Allah ne ya cika gizagizai masu duhu da ruwa, Girgijen kuwa bai kece ba.

9 Ya rufe kursiyinsa, ya shimfiɗa girgije a kansa.

10 Ya shata da'ira a kan fuskar teku, A kan iyakar da take tsakanin haske da duhu.

11 Ginshiƙan samaniya sun girgiza, Sun firgita saboda tsautawarsa.

12 Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku, Da saninsa ya hallaka dodon ruwan nan, wato Rahab.

13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi garau, Ikonsa ne kuma ya sha zarar macijin nan mai gudu.

14 Amma waɗannan kaɗan ne kawai daga cikin al'amuransa. Ɗan ƙis kaɗai muke ji a kansa. Amma wa zai iya fahimtar ikon tsawarsa?”

27

1 Ayuba ya amsa.

2 “Na rantse da Allah Mai Iko Dukka, Wanda ya ƙwace mini halaliyata, Wanda ya ɓata mini rai.

3 Muddin ina numfashi, Ruhun Allah kuma yana cikin hancina

4 Bakina ba zai faɗi ƙarya ba, Harshena kuma ba zai hurta maganganun yaudara ba.

5 Allah ya sawwaƙa in ce kun yi daidai, Har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.

6 Ina riƙe da adalci kam, ba kuwa zan sake shi ba, Zuciyata ba ta zarge ko ɗaya daga cikin kwanakin raina ba.

7 “Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum, Wanda ya tashi gāba da ni ya zama kamar marar adalci.

8 Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah? Sa'ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa?

9 Allah kuwa zai ji kukansa sa'ad da wahala ta same shi?

10 Ko Mai Iko Dukka zai zama abin farin ciki a gare shi? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?

11 “Zan koya muku zancen ikon Allah, Abin da yake na wajen Mai Iko Dukka ba zan ɓoye ba.

12 Ga shi kuwa, dukanku kun gani da kanku, Me ya sa kuka zama wawaye?

13 “Wannan shi ne rabon mugaye daga wurin Allah, Gādo ne kuma wanda azzalumai za su karɓa daga wurin Mai Iko Dukka.

14 Idan 'ya'yansu sun riɓaɓɓanya za su zama rabon takobi, Zuriyarsu kuwa ba za su sami isasshen abinci ba.

15 Waɗanda suka tsira, annoba za ta kashe su, Matansu ba za su yi makokin mutuwarsu ba.

16 Ko da yake sun tsibe azurfa kamar turɓaya, Sun tara tufafi kamar ƙasa,

17 Za su tara, amma adalai za su sa, Marasa laifi ne za su raba azurfar.

18 Sun gina gidajensu kamar saƙar gizo-gizo, Kamar bukkar mai tsaro.

19 Attajirai za su kwanta, amma daga wannan shi ke nan, Za su buɗe ido su ga dukiyan nan ba ta.

20 Razana za ta auka musu kamar rigyawa. Da dare iska za ta tafi da su.

21 Iskar gabas za ta fauce su su tafi, Ta share su ta raba su da wurin zamansu.

22 Za ta murɗe su ba tausayi, Hakika za su yi ƙoƙari su tsere daga ikonsa, Sai su yi ƙundumbala.

23 Kowa zai tafa hannu yă yi musu tsaki har su tashi daga wurin da suke.”

28

1 “Hakika akwai ma'adinai na azurfa, Da wuraren da ake tace zinariya.

2 Mutane sukan haƙo baƙin ƙarfe daga ƙasa, Sukan narkar da tagulla daga dutse.

3 Mutane sukan kawar da duhu, Sukan kuma bincike zuzzurfar iyaka, Sukan haƙo duwatsun da suke cikin duhu, duhu baƙi ƙirin.

4 Sukan haƙa loto a fadama nesa da mutane, Sukan kafa abin lilo su yi ta lilo nesa da mutane.

5 “Daga cikin ƙasa ake samun abinci, Amma a ƙarƙashinta yakan zama kamar wuta.

6 Akwai duwatsu masu daraja cikin duwatsunta, Akwai zinariya a ƙurarta.

7 Tsuntsu mai cin nama bai san wannan hanya ba. Shaho ma bai gan ta ba.

8 Namomin jeji ba su taɓa bin hanyar ba, Ko zaki ma bai taɓa binta ba.

9 “Mutane sun iya sarrafa ƙanƙarar dutse, Suna kuma iya tumɓuke tushen duwatsu.

10 Sukan haƙa magudanar ruwa cikin duwatsu, Idanunsu sukan ga kowane abu mai daraja.

11 Sukan datse rafuffuka su hana su gudu, Su binciko abin da yake ɓoye, ya fito sarari.

12 Amma ina, a ina za a iya samun hikima? A ina za a samo haziƙanci?

13 Mutane ba su san darajar hikima ba, Ba a samunta a ƙasar masu rai.

14 Zurfafa sun ce, ‘Ba ta a cikinmu,’ Tekuna kuma sun ce, ‘Ba ta tare da mu.’

15 Ba za a saye ta da zinariya tsantsa ba. Azurfa ba za ta iya biyan tamaninta ba.

16 Ko zinariyar Ofir, ko onis, Ko saffir, wato duwatsu masu daraja, ba za su iya biyan tamaninta ba.

17 Ba daidai take da zinariya ko madubi ba, Ba za a iya musayarta da kayayyakin da aka yi da zinariya tsantsa ba.

18 Kada ma a ko ambaci murjani, Da duwatsu masu walƙiya. Gama tamanin hikima ya fi na lu'ulu'ai mafiya daraja duka.

19 Ba za a daidaita tamaninta da na duwatsun tofaz na Habasha ba. Tamaninta ya fi na zinariya tsantsa.

20 “To, daga ina hikima ta fito? A wane wuri kuma haziƙanci yake?

21 Ba talikin da ya iya ganinta, Ko tsuntsun da yake tashi sama.

22 Halaka da Mutuwa sun ce, ‘Da kunnuwanmu mun ji ƙishin-ƙishin a kanta.’

23 “Allah ne kaɗai ya san hanya zuwa gare ta, Ya san inda hikima take,

24 Saboda yana ganin duniya ɗungum, Yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sararin sama.

25 Sa'ad da Allah ya sa iska ta hura, Ya yi wa tekuna iyaka.

26 Sa'ad da ya ba da umarni ga ruwan sama, Da kuma hanyar da tsawa za ta bi,

27 Shi ya san hikimar, shi ya sanar, Ya tabbatar da ita, ya bincike ta sarai.

28 “Allah ya ce wa mutane, ‘Duba, tsoron Ubangiji shi ne hikima, Rabuwa da mugunta kuma, ita ce haziƙanci.’ ”

29

1 Ayuba ya ci gaba da magana.

2 Da ma ina cikin lokacin da ya wuce ne, Lokacin da Allah yake lura da ni,

3 Sa'ad da fitilarsa take haskaka mini, Ta wurin haskensa kuma nake tafiya da duhu,

4 Kwanakin da nake gaɓar raina, Lokacin da ni'imar Allah take kan gidana,

5 Sa'ad da Mai Iko Dukka yake tare da ni, 'Ya'yana duka kuma suka kewaye ni,

6 Sa'ad da aka wanke ƙafafuna da madara, Duwatsu kama suna ɓulɓulo mini da rafuffukan mai!

7 A sa'ad da nakan tafi kofar birni, In shirya wurin zamana a dandali,

8 Da samari sun gan ni, sai su kawar da jiki, Tsofaffi kuma su miƙe tsaye,

9 Sarakuna sun yi shiru sun kame bakinsu.

10 Manyan mutane sukan yi shiru, harshensu ya liƙe a dasashi.

11 Waɗanda suka ji labarina sukan sa mini albarka, Waɗanda suka gan ni sukan yi na'am da ni.

12 Domin sa'ad da matalauta suka yi kuka, ni nake cetonsu, Nakan taimaki marayu waɗanda ba su da mai taimako.

13 Waɗanda suke bakin mutuwa sukan sa mini albarka, Na taimaki gwaurayen da mazansu suka mutu, Su raira waƙa don murna.

14 Adalci shi ne suturata, Gaskiya ita ce rigata da rawanina.

15 Ni ne idon makafi, guragu kuma, ni ne ƙafarsu.

16 Ni mahaifi ne ga matalauta, Nakan bincika don in warware al'amarin da ya dami baƙi.

17 Nakan karya muƙamuƙin marar adalci, In sa yă saki ganimar da yă kama.

18 “Da na zaci zan mutu cikin sutura, Kwanakina kuma su riɓaɓɓanya, su yi yawa kamar yashi,

19 Saiwoyina a shimfiɗe suke cikin ruwa, Dukan dare raɓa na sauka a kan rassana .

20 Darajata garau take a gare ni, Bakana kullum sabo yake a hannuna.

21 Mutane sukan kasa kunne su jira, su yi shiru Sa'ad da nake ba da shawara.

22 Bayan na gama magana ba wanda zai ƙara wata magana. Maganata takan shige su.

23 Suna jirana kamar yadda ake jiran ruwan sama, Da baki buɗe, kamar yadda ake jiran ruwan bazara.

24 Nakan yi musu murmushi sa'ad da suka fid da zuciya, Ba su yi watsi da fara'ata ba.

25 Nakan zaɓar musu hanyar da za su bi, Ina zaune kamar sarki a tsakanin mayaƙansu, Kamar mai ta'azantar da masu makoki.”

30

1 “Amma yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a suke mini, Waɗanda iyayensu maza ba su fi karnukan da suke kiwon garken tumakina ba.

2 Wace riba zan samu ta wurin ƙarfin hannuwansu waɗanda ba su da sauran kuzari?

3 Saboda rashi da matsananciyar yunwa sun rame, Sai gaigayar ƙasa suke yi da dare, a cikin kufai.

4 Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci, Sukan ci doyar jeji.

5 Aka kore su daga cikin mutane, Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo,

6 Sai a kwazazzabai suke zama Da a ramummuka da kogwannin duwatsu.

7 Suka yi ta kuka a jeji, Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.

8 Mutane ne marasa hankali marasa suna! Aka kore su daga ƙasar.

9 “Yanzu na zama abin waƙa gare su, Abin ba'a kuma a gare su.

10 Suna ƙyamata, guduna suke yi, Da ganina, sai su tofa mini yau.

11 Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni, Saboda haka sun raba ni da zuriyata,

12 A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini, Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.

13 Sun datse hanyata, Sun jawo mini bala'i, Ba kuwa wanda ya hana su.

14 Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka, Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi.

15 Sun firgita ni, Sun kori darajata kamar da iska, Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.

16 “Yanzu zuciyata ta narke Kwanakin wahala sun same ni.

17 Da dare ƙasusuwana karkaɗuwa suke, Azaba tana ta gaigayata ba hutawa.

18 An yi mini kamun kama-karya, An ci wuyan rigata.

19 Allah ya jefar da ni cikin laka, Na zama kamar ƙura ko toka,

20 “Na yi kira gare ka, ya Allah, amma ba ka amsa mini ba, Na yi addu'a kuma, amma ba ka kula da ni ba.

21 Ka zama mugu a gare ni, Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.

22 Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta, Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri.

23 Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa, Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai.

24 “Ashe, wanda yake gab da gagarumar hallaka, Ba zai miƙa hannu ya roƙi taimako a masifar da yake sha ba?

25 Ashe, ban yi kuka saboda wanda yake shan wahala ba? Ashe, ban yi ɓacin rai saboda matalauta ba?

26 Amma sa'ad da na sa zuciya ga alheri, sai ga mugunta, Sa'ad da nake jiran haske, sai ga duhu ya zo.

27 Zuciyata tana tafasa, ba ta kwanciya, Kwanakin wahala sun auko mini.

28 Na yanƙwane, amma ba yanƙwanewar rana ba, Na tsaya a gaban taron jama'a, ina roƙon taimako.

29 “Na zama ɗan'uwan dila, Na kuma zama aminin jiminai.

30 Fatata ta takura, ta zama baƙa, Ƙasusuwana suna zogi saboda zafi,

31 Saboda haka garayata ta zama ta makoki, Sarewata kuma ta zama muryar masu kuka.”

31

1 “Na yi alkawari da idanuna, Me zai sa in ƙyafaci budurwa?

2 Wane rabo zan samu daga wurin Allah a Sama? Wane gādo kuma zan samu daga wurin Mai Iko Dukka a can samaniya?

3 Yakan aika da masifa da lalacewa Ga waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba.

4 Allah ya san dukan abin da nake yi, Yana ƙididdige dukan takawata.

5 “Idan ina tafiya da rashin gaskiya, Ina hanzari don in aikata yaudara,

6 Bari Allah ya auna ni da ma'aunin da yake daidai, Zai kuwa san mutuncina.

7 Idan dai na kauce daga hanya, Ko kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna, Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna,

8 To, bari in shuka, wani ya ci amfanin, Bari a tumɓuke amfanin gonata.

9 “Idan na yi sha'awar wata mace, Har na je na laɓe a ƙofar maƙwabcina,

10 To, bari matata ta yi wa wani abinci, Bari waɗansu su kwana da ita.

11 Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai, Wanda alƙalai ne za su hukunta.

12 Za ta zama wuta mai ci har ta hallaka, Za ta cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.

13 “Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba, Sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,

14 To, wace amsa zan ba Allah sa'ad da ya tashi don ya hukuntar? Me zan iya faɗa sa'ad da Allah ya zo yi mini shari'a?

15 Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa, Ba shi ne ya halicce su ba? Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?

16 “Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba, Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba,

17 Ko kuwa in bar marayu da yunwa sa'ad da nake cin abincina,

18 Tun suna yara nake goyonsu, Ina lura da su kamar 'ya'yan cikina.

19 “Amma idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura, Ko wani matalauci marar abin rufa,

20 Idan a zuciyarsa bai sa mini albarka ba, Ko bai ji ɗumi da ulun tumakina ba,

21 Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya, Don na ga ina da kafar kuɓuta,

22 To, ka sa kafaɗuna su ɓaɓɓalle daga inda suke. Ka kakkarya gwiwoyin hannuna.

23 Gama bala'i daga wurin Allah ya razanar da ni, Saboda ɗaukakarsa ba zan iya yin kome ba.

24 “Idan na ce ga zinariya na dogara, ko zinariya tsantsa ita ce jigona,

25 Idan kuma saboda yawan dukiyata nake fariya, Ko saboda abin da na mallaka ne,

26 Idan ga hasken rana nake zuba ido, Ko ga hasken farin wata ne,

27 Zuciyata ta jarabtu ke nan a asirce, Ni da kaina ina sumbatar hannuna,

28 Wannan ma zai zama laifi ne wanda alƙalai za su hukunta, Gama na zama munafukin Allah Mai Iko Dukka ke nan.

29 “Idan na yi murna saboda wahala ta sami maƙiyana, Ko na yi fariya saboda mugun abu ya same shi,

30 Ban yi zunubi da bakina ba, Ban nemi ran wani ta wurin la'anta shi ba.

31 Ko mutanen da suke cikin alfarwata ba wanda zai ce, Ga wani can da bai ƙoshi da nama ba.

32 Ban bar baƙi su kwana a titi ba, Ƙofar gidana a buɗe take ga matafiya.

33 Idan na ɓoye laifofina a zuciyata,

34 Ko na tsaya shiru saboda tsoron taron jama'a, Saboda kuma baƙar maganar mutane ta razanar da ni,

35 Da a ce ina da wanda zai kasa kunne gare ni, Da sai in sa hannu a kan abin da na faɗa, Allah kuwa Mai Iko Dukka ya amsa mini. “Da ƙarar da maƙiyana suke kai ni, a rubuce ne,

36 Hakika da sai in ɗauke ta a kafaɗata, In kuwa naɗa ta a kaina kamar rawani.

37 Da na ba Allah dukan lissafin abin da na taɓa yi, In tinƙare shi kamar ni basarauce ne.

38 “Idan ƙasata tana kuka da ni, Ita da kunyoyinta,

39 Ko na ci amfaninta ban biya ba, Ko na yi sanadin mutuwar mai ita,

40 Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha'ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

32

1 Mutanen nan uku sun daina ba Ayuba amsa, saboda yana ganin kansa adali ne.

2 Sai Elihu, ɗan Barakel, mutumin Buz, daga cikin iyalin Arama, ya husata, yana fushi da Ayuba saboda ya baratar da kansa, bai bari Allah ya baratar da shi ba.

3 Yana kuma fushi da abokan nan uku na Ayuba, domin sun rasa amsar da za su ba Ayuba, ko da yake sun hurta Ayuba ne yake da laifi.

4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.

5 Sa'ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da wata amsa da za su ba Ayuba, sai ya yi fushi.

6 Elihu ɗan Barakel, mutumin Buz, ya fara magana, ya ce, “A shekaru dai ni yaro ne ku kuwa manya ne, Don haka ina jin nauyi, Ina kuma jin tsoro in faɗa muku ra'ayina.

7 Na ce wa kaina, ‘Ya kamata kwanaki su yi magana, Yawan shekaru kuma su koyar da hikima.’

8 Amma Ruhun Allah Mai Iko Dukka ne wanda yake cikin mutum, Yakan ba mutane basira.

9 Ba tsofaffi ne masu wayo ba, Ba kuma masu yawan shekaru kaɗai yake gane abin da yake daidai ba.

10 Don haka na ce ku kasa kunne gare ni, Bari in faɗa muku nawa ra'ayi.

11 “Ga shi, na dakata na ji maganarku, Na kasa kunne ga maganarku ta hikima, Tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.

12 Na kasa kunne gare ku sosai, Amma ko ɗaya ba wanda ya kā da Ayuba. Ba kuma wanda ya ba shi amsar tambayarsa.

13 Ku lura kada ku ce kuna da hikima, Allah ne kaɗai yake da iko ya kā da shi, ba mutum ba.

14 Ba da ni Ayuba yake magana ba, Saboda haka ba zan amsa masa da irin amsarku ba.

15 “Abin ya cika musu ciki, ba su ƙara amsawa ba, Wato ba su da ta cewa.

16 Ni kuma sai in tsaya don ba su ce kome ba? Sun tsaya kurum, don ba su da ta cewa?

17 A'a, ni kuma zan ba da tawa amsa, In kuma faɗi ra'ayina.

18 Cike nake da magana, Ruhun da ka cikina ya iza ni.

19 Ga zuciya tana kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska, Kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda take shirin fashewa.

20 Tilas in yi magana don in huce, Dole in ba da amsa.

21 Ba zan yi wa kowa son zuciya ba, Ko kuma in yi wa wani fādanci.

22 Gama ni ban iya fādanci ba, Idan na yi haka kuwa Mahaliccina zai kashe ni nan da nan.”

33

1 “Amma yanzu, kai Ayuba, ka yarda ka ji maganata, Ka kasa kunne ga dukan abin da zan faɗa.

2 Ga shi, na buɗe baki in yi magana.

3 Maganar da zan hurta ainihin gaskiyar da take a zuciyata ce, Abin da zan faɗa kuma dahir ne.

4 Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai.

5 “Ka amsa mini, in ka iya, Ka shirya abubuwan da za ka faɗa mini, ka yi tsaye a kansu.

6 Duba, ni da kai ɗaya muke a wajen Allah, Dukanmu biyu kuma daga yumɓu aka siffata mu.

7 Don haka kada ka razana saboda ni, Abin da zan faɗa maka, ba abin da zai fi ƙarfinka.

8 “Hakika na ji maganar da ka yi, Na kuwa ji amon maganganunka,

9 Ka ce kai tsattsarka ne, ba ka da laifi, Kai tsabtatacce ne, ba ka da wata ƙazanta.

10 Ka ce Allah ya zarge ka ya ɗauke ka tankar maƙiyansa,

11 Ya saka ka a turu, Yana duban dukan al'amuranka.

12 “Amma a kan wannan, Ayuba, ka yi kuskure, zan ba ka amsa, Gama Allah ya fi kowane mutum girma.

13 Me ya sa kake yi wa Allah gunaguni, Cewa ba ya karɓar maganarka ko ɗaya?

14 Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne, I, har sau biyu, duk da haka mutum ba ya lura.

15 Yakan sanar a mafarkai ko a wahayi Sa'ad da barci mai nauyi ya ɗauke su, A sa'ad da suke barci a gadajensu.

16 Yakan buɗe kunnuwan mutane, Ya tsorata su da faɗakarwarsa,

17 Domin ya kawar da su daga aikin da suke yi, Ya kuma kawar musu da girmankai.

18 Yakan hana su zuwa kabari, Ya hana ransu halaka da takobi.

19 “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa, Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,

20 Ransa yana ƙyamar abinci, Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa.

21 Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje.

22 Yana gab da shiga kabari, Ransa yana hannun mala'ikun mutuwa.

23 “Da a ce akwai wani mala'ika mai sulhuntawa a tsakani, Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum,

24 Mala'ikan da zai yi masa alheri ya ce, ‘Ka cece shi daga gangarawa zuwa cikin kabari, Na sami abin da zai fanshe shi!’

25 Naman jikinsa zai koma kamar na saurayi, Zai komo kamar lokacin da yake gaɓar ƙarfinsa.

26 Sa'an nan ne mutum zai yi addu'a ga Allah, ya karɓe shi, Ya zo gabansa da murna, Allah zai komar wa mutum da adalcinsa.

27 Zai raira waƙa a gaban jama'a, ya ce, ‘Na yi zunubi. Ban yi daidai ba, Amma ba a sa ni in biya ba.

28 Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari, Raina kuwa zai ga haske.’

29 “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,

30 Don ya komo da ran mutum daga kabari, Domin a haskaka shi da hasken rai.

31 “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne, Ga abin da nake faɗa, Ka yi shiru, zan yi magana.

32 Amma idan kana da ta cewa, to, amsa, Yi magana, gama ina so in kuɓutar da kai.

33 In kuwa ba haka ba, sai ka yi shiru, Ka kasa kunne gare ni, Zan kuwa koya maka hikima.”

34

1 Elihu ya ci gaba.

2 “Ku mutane masu hikima, ku ji maganata, Ku kasa kunne ga abin da zan faɗa, ku masana.

3 Kunne yake rarrabewa da magana, Kamar yadda harshe yake rarrabewa da ɗanɗanar abinci.

4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, Bari kuma mu daidaita abin da yake mai kyau tsakanin junanmu.

5 Gama Ayuba ya ce, ‘Ni marar laifi ne, Amma Allah ya ƙwace mini halaliyata.

6 Duk da rashin laifina an ɗauke ni a maƙaryaci, Raunina ba ya warkuwa ko da yake ba ni da laifin kome.’

7 “Wane irin mutum ne kai, Ayuba, Da kake shan raini kamar yadda kake shan ruwa,

8 Wanda yake cuɗanya da ƙungiyar masu aikata laifi, Kana yawo tare da mugaye?

9 Gama ka ce, ‘Bai amfana wa mutum kome ba Ya yi murna da Allah.’

10 “Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai, Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne, A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure,

11 Gama bisa ga aikin mutum yake sāka masa, Yana sa aniyarsa ta bi shi.

12 Gaskiya ce, Allah ba zai aikata mugunta ba, Mai Iko Dukka ba zai kauce wa adalci ba.

13 Wa ya shugabantar da shi a kan duniya? Wa ya mallakar masa da duniya duka?

14 Da zai amshe ruhu da numfashin da ya hura wa mutum,

15 Da duk mai rai ya halaka, Mutum kuma ya koma ƙura.

16 “Idan kai haziƙi ne, to, ji wannan, Kasa kunne ga abin da zan faɗa.

17 Da Allah maƙiyin adalci ne, da ya yi mallaka? Ka iya sa wa Adali, Mai Iko Dukka laifi?

18 Ka iya sa wa Allah laifi, Shi da ya ce, ‘Sarki marar amfani ne, Hakimai kuma mugaye’?

19 Ba ya nuna sonkai ga sarakuna, Ko kuma ya fi kulawa da attajira fiye da matalauta, Gama shi ya halicce su duka.

20 Sukan mutu nan da nan, Da tsakar dare manya da ƙanana sukan shuɗe farat ɗaya, An kawar da su ba da hannun mutum ba.

21 “Gama yana ganin al'amuran mutum, Yana kuma ganin dukan manufarsa.

22 Ba wani duhu, ko duhu baƙi ƙirin Inda masu aikata mugunta za su ɓuya.

23 Ba ajiyayyen lokacin da ya ajiye wa kowane mutum Da zai je shari'a a gaban Allah.

24 Yakan ragargaza ƙarfafa ba tare da wani bincike ba, Ya sa waɗansu a madadinsu.

25 Saboda sanin ayyukansu, Yakan kaɓantar da su da dare ya ragargaza su,

26 Yakan buge su a gaban mutane saboda muguntarsu,

27 Don sun daina binsa, ba su kula da ko ɗaya Daga cikin umarnansa ba.

28 Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah, Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa.

29 Idan Allah zai yi shiru, da wa zai sa wa wani laifi? Idan ya ɓoye fuskarsa, wa zai iya ganinsa, Ko aka yi wa al'umma ko ga mutum?

30 Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba, Don kada ya tura jama'a cikin tarko.

31 “Akwai wanda zai ce wa Allah, ‘Ni horarre ne, Ba zan ƙara yin laifi ba?

32 Ka koya mini abin da ban sani ba, Idan na yi laifi, ba zan ƙara yi ba.’

33 Zai kuɓutar domin ya gamshe ka saboda ka ƙi yarda? Tilas kai za ka zaɓa, ba ni ba, Saboda haka sai ka hurta abin da ka sani.

34 “Haziƙan mutane da mutum mai hikima da suka ji ni za su ce,

35 ‘Ayuba yakan yi magana ne ba tare da sanin abin da yake yi ba, Maganarsa ba ta mai hangen nesa ba ce.

36 Da ma a gwada Ayuba har ƙarshe, Saboda amsar da yake bayarwa ta mugaye.

37 Gama ya ƙara zunubinsa da tayarwa, Yana tafa hannunsa a tsakaninmu, Yana yawaita maganganunsa gāba da Allah.’ ”

35

1 Elihu kuwa ya yi magana.

2 “Ayuba, ba daidai ba ne, ka ce, Ba ka yi laifi a gaban Allah ba,

3 Ka kuwa ce, ‘Wace riba na ci? Wane fifiko nake da shi fiye da idan na yi zunubi?’

4 Zan ba ka amsa, kai da abokanka.

5 Ka duba sama, Ka dubi gizagizai waɗanda suke can sama da kai.

6 Idan ka yi zunubi, da me ka cuci Allah? Idan ka aikata laifofi da yawa, wace cuta ka yi masa?

7 Idan kai adali ne da me ka ƙara masa, Ko kuwa me ya samu daga gare ka?

8 Muguntarka ta shafi mutum ne kamarka, Haka kuma adalcinka ya shafi ɗan adam ne kawai.

9 “Saboda yawan zalunci, jama'a sukan yi kuka, Suka nemi taimako, saboda matsin masu ƙarfi.

10 Amma ba su juyo wurin Allah Mahaliccinsu ba, Wanda yakan sa a raira waƙa da dare,

11 Wanda yake koya mana fiye da namomin jeji da suke a duniya, Wanda ya sa muka fi tsuntsayen sama hikima.

12 Suka yi kira don taimako, amma Allah bai amsa ba, Saboda suna da girmankan mugaye.

13 Hakika Allah bai ji holoƙon kukansu ba, Allah Mai Iko Dukka kuwa bai kula da shi ba.

14 “Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba? Da kake cewa ƙararka tana gabansa, Jiransa kake yi?

15 Yanzu fa saboda bai yi hukunci da fushinsa ba, Kamar kuma bai kula da laifi ba,

16 Ayuba, maganarka marar ma'ana ce, Ka yi ta maganganu marasa hikima.”

36

1 Elihu ya ci gaba da magana.

2 “Ka yi mini haƙuri kaɗan, ni kuwa zan nuna maka, Gama har yanzu ina da abin da zan faɗa in kāre Allah.

3 Zan tattaro ilimina daga nesa, In bayyana adalcin Mahaliccina.

4 Gaskiya nake faɗa ba ƙarya ba, Wanda yake da cikakken sani yana tare da kai.

5 “Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa, Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira.

6 Ba ya rayar da masu laifi, Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.

7 Yakan kiyaye waɗanda suke aikata gaskiya, Yakan kafa su har abada tare da sarakuna, A gadon sarauta, ya ɗaukaka su.

8 Amma idan aka ɗaure su da sarƙoƙi, Da kuma igiyar wahala,

9 Sa'an nan yakan sanar da su aikinsu Da laifofin da suke yi na ganganci.

10 Yakan sa su saurari koyarwa, Da umarnai, cewa su juya, su bar mugunta.

11 Idan suka kasa kunne suka bauta masa, Za su cika kwanakinsu da wadata, Shekarunsu kuma da jin daɗi.

12 Amma idan ba su kasa kunne ba, Za a hallaka su da takobi, Su mutu jahilai.

13 “Waɗanda ba su da tsoron Allah a zuciyarsu, Suna tanada wa kansu fushi, Ba su neman taimako sa'ad da ya ɗaure su.

14 Sukan yi mutuwar ƙuruciya, Sukan ƙare kwanakinsu da kunya.

15 Zai kuɓutar da waɗanda suke shan tsanani, Ta wurin tsananin da suke sha, Yakan buɗe kunnuwansu ta wurin shan wahala.

16 Allah ya tsamo ka daga cikin wahala, Ya kawo ka yalwataccen wuri inda ba matsi, Abincin da aka yi na addaras aka jera maka a kan tebur.

17 “Ka damu ƙwarai don ka ga an hukunta mugaye, Amma hukunci da adalci sun kama ka.

18 Ka lura kada ka bar hasalarka ta sa ka raina Allah, Kada kuma ka bar wahalar da kake sha ta sa ka ɓata da mai fansarka.

19 Kukanka ya iya raba ka da wahala, Ko kuwa dukan ƙarfin da kake da shi?

20 Kada ka ƙosa dare ya yi, Domin a lokacin nan ne mutane sukan watse, Kowa ya kama gabansa.

21 Ka lura kada ka rinjayu a kan aikata mugunta, Gama saboda haka kake shan wannan tsanani, Don a tsare ka daga aikata mugunta.

22 “Duba, Allah Maɗaukaki ne cikin ikonsa, Wa ya iya koyarwa kamarsa?

23 Ba wanda zai iya tsara wa Allah abin da zai yi, Wa ya isa ya ce masa ya yi kuskure?

24 “Ka tuna ka girmama aikinsa, Wanda mutane suke yabo.

25 Dukan mutane sun ga ayyukansa, Sun hango shi daga nesa.

26 Ga shi kuwa, Allah Maɗaukaki ne, Ba mu kuwa san iyakar ɗaukakarsa ba, Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.

27 “Allah yakan sa ruwa ya zama tururi, Ya maishe shi ruwan sama,

28 Wanda yakan kwararo daga sama, Ya zubo wa ɗan adam a yalwace.

29 Wa zai iya gane yadda gizagizai suke shimfiɗe a sararin sama, Da tsawar da ake yi a cikinsu?

30 Ga shi, yakan baza waƙiya kewaye da shi, Yakan rufe ƙwanƙolin duwatsu. Zurfin teku yana nan da duhunsa.

31 Gama ta haka yakan shara'anta mutane, Yakan ba da abinci a yalwace.

32 Ya cika hannunsa da walƙiya, Yakan sa ta faɗa a kan abin da ya bārata.

33 Tsawarta tana nuna kasancewar Allah, Ko shanu sun san da zuwan hadiri.”

37

1 “Saboda wannan zuciyata takan kaɗu, Kamar ta yi tsalle daga inda take.

2 Ku kasa kunne ga tsawar muryarsa, Ku saurara ga maganarsa mai ƙarfi.

3 Yakan sako ta a ƙarƙashin samaniya duka, Walƙiyarsa takan zagaya dukan kusurwoyin duniya.

4 Bayan walƙiyar akan ji rugugin muryarsa, Ya yi tsawa da muryarsa ta ɗaukaka, Ko da yake an ji muryarsa bai dakatar da tsawar ba.

5 Muryar tsawar Allah mai banmamaki ce, Yana aikata manyan abubuwa da suka fi ƙarfin ganewarmu.

6 Yakan umarci dusar ƙanƙara ta fāɗo bisa duniya, Yayyafi da ruwan sama kuwa su yi ƙarfi.

7 Yakan tsai da kowane mutum daga aikinsa, Domin dukan mutane su san aikinsa.

8 Namomin jeji sukan shiga wurin kwanciyarsu, Su yi zamansu a ciki.

9 Guguwa takan taso daga inda take, Sanyi kuma daga cikin iska mai hurawa.

10 Numfashin Allah yakan sa ƙanƙara, Yakan sa manyan ruwaye su daskare farat ɗaya.

11 Yakan cika girgije mai duhu da ruwa, Gizagizai sukan baza walƙiyarsa.

12 Sukan yi ta kewayawa ta yadda ya bishe su, Don su cika dukan abin da ya umarce su a duniya da ake zaune a ciki.

13 Allah yakan aiko da ruwan sama ya shayar da duniya, Saboda tsautawa, ko saboda ƙasa, ko saboda ƙauna.

14 “Ka ji wannan, ya Ayuba, Tsaya ka tuna da ayyukan Allah masu banmamaki.

15 Koka san yadda Allah yakan ba su umarni, Ya sa walƙiyar girgijensa ta haskaka?

16 Ko kuma ka san yadda gizagizai suke tsaye daram a sararin sama? Ayyukan banmamaki na Allah, cikakken masani!

17 Ko ka san abin da yake sa ka jin gumi Sa'ad da iskar kudu take hurowa?

18 Ka iya yin yadda ya yi, Kamar yadda ya shimfiɗa sararin sama daram, Kamar narkakken madubi?

19 Ka koya mana abin da za mu faɗa masa, Ba za mu iya gabatar da ƙararrakinmu ba, gama mu dolaye ne.

20 A iya faɗa masa, cewa zan yi magana? Mutum ya taɓa so a haɗiye shi da rai?

21 “A yanzu dai mutane ba su iya duban haske, Sa'ad da yake haskakawa a sararin sama, Bayan da iska ta hura ta share gizagizai sarai.

22 Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki, Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro.

23 Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu, Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya, Da yalwataccen adalci, Ba ya garari.

24 Saboda haka mutane suke tsoronsa, Bai kula da waɗanda suke ɗaukar kansu su masu hikima ba ne.”

38

1 Ubangiji ya yi magana da Ayuba ta cikin guguwa.

2 “Wane ne wannan da yake ɓāta shawara Da maganganu marasa ma'ana?

3 Ka tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji, Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

4 A ina kake sa'ad da na aza harsashin gina duniya? Faɗa mini idan ka sani.

5 Wane ne ya zayyana kusurwoyinta? Hakika ka sani. Wane ne kuma ya auna ta?

6 A kan me aka kafa tushenta? Wa ya aza dutsen kan kusurwarta?

7 Sa'ad da taurarin asuba suka raira waƙa tare, Sai mala'iku duka suka yi sowa saboda murna.

8 “Wa ya yi wa teku iyaka Sa'ad da ta tumbatso daga zurfafa?

9 Sa'ad da na suturta ta da gizagizai, Na yi mata maɗauri da duhu ƙirin.

10 Na sa mata iyakoki, Na sa mata ƙyamare da ƙofofi,

11 Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan, Ba za ki wuce ba. Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’

12 “Ayuba, a dukan kwanakinka Ka taɓa umartar wayewar gari, Ko ka sa alfijir ya keto?

13 Da gari ya waye, Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?

14 Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi, Yakan rine kamar riga.

15 Akan hana wa mugaye haske, Sa'ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su.

16 “Ko ka taɓa shiga cikin maɓuɓɓugan teku? Ka taɓa yin tafiya a cikin zurfin lallokin teku?

17 An taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa? Ko kuwa ka taɓa ganin ƙofofin duhu ƙirin?

18 Ko ka san iyakar fāɗin duniya? Ka amsa mini in ka san dukan waɗannan.

19 “Ina hanya zuwa wurin da haske yake? A ina kuma duhu yake?

20 Ka san iyakarsa ko mafarinsa?

21 Ka sani, gama a lokacin nan an haife ka, Shekarunka kuwa suna da yawa.

22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara? Ko kuwa ka taɓa shiga rumbunan ajiyar ƙanƙara?

23 Na adana su ne don lokacin wahala, Domin ranar faɗa da ta yaƙi.

24 Ina hanya zuwa inda rana take fitowa, Ko kuma ta inda iskar gabas take hurowa ta māmaye ko'ina?

25 “Wa ya haƙa hanyar da ruwan sama mai kwararowa zai bi? Da kuma hanyar da gatarin aradu zai bi?

26 Wa ya kuma kawo ruwan sama a ƙasar da ba mutane, Da a cikin hamada inda ba kowa,

27 Don a shayar da zozayar ƙasa inda ba kowa, Har ta tsiro da ciyayi?

28 “Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya haifi ɗiɗɗigar raɓa?

29 Wace ce mahaifiyar ƙanƙara? Wace ce kuma ta haifi jaura?

30 Ruwa ya daskare ya yi ƙarfi kamar dutse, Teku ta daskare.

31 “Za ka iya ɗaure sarƙoƙin kaza-da-'ya'yanta? Ko ka iya kwance igiyoyin mafarauci-da-kare-da-zomo?

32 Za ka iya bi da yaneyanen sararin sama bisa ga fasalinsu?

33 Ka san ka'idodin sammai? Ko ka iya faɗar yadda suka danganta da duniya?

34 “Kana iya yi wa gizagizai tsawa, Don su kwararo ruwan sama, ya rufe ka?

35 Ka iya aikar walƙiyoyi su tafi, Sa'an nan su ce maka, ‘Ga mu mun zo?’

36 Wa ya sa hikima a gizagizai, Ko kuma wa ya ba da ganewa ga kāsashi?

37 Akwai mai hikimar da zai iya ƙidaya gizagizai? Ko kuwa wa zai iya karkato da salkunan ruwan sammai,

38 Sa'ad da ƙura ta murtuke ta taru jingim, ta game kam?

39 “Ka iya farauto wa zakoki abinci? Ko ka ƙosar da yunwar sagarun zakoki,

40 Sa'ad da suke fako a kogwanninsu, Ko suna kwance suna jira a maɓoyarsu?

41 Wa yake tanada wa hankaka abincinsa, Sa'ad da 'ya'yansa suke kuka ga Allah, Suna kai da kawowa saboda rashin abinci?”

39

1 “Ka san lokacin da awakan dutse suke haihuwa? Ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?

2 Ka san ko watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin haihuwarsu?

3 Ka san lokacin naƙudarsu, sa'ad da suke haihuwar 'ya'yansu, Lokacin da 'ya'yansu suke fita cikinsu?

4 'Ya'yansu sukan yi ƙarfi su girma a fili cikin saura, Sukan yi tafiyarsu ba su komawa wurin iyayensu.

5 “Wa ya bar jakin jeji ya yi yadda yake so? Wa ya ɓalle dabaibayin jaki mai sauri,

6 Wanda na ba fili fetal ya zama gidansa, Da ƙasa mai gishiri a wurin zamansa?

7 Yakan yi wa hayaniyar birane ba'a, Ba ruwansa da tsawar masu kora.

8 Tsaunukan duwatsu ne wurin kiwonsa, A can yake neman kowane ɗanyen abu.

9 “Kutunkun ɓauna zai yarda ya yi maka aiki? Zai yarda ya kwana ɗaya a dangwalinka?

10 Ka iya ɗaure shi da igiya a kwarin kunya? Ko kuwa zai yi maka kaftu a fadamarka?

11 Za ka dogara gare shi saboda tsananin ƙarfinsa? Za ka kuma bar masa aikinka?

12 Ka gaskata zai komo, Ya kawo maka hatsi a masussukarka?

13 “Jimina takan karkaɗa fikafikanta da alfarma! Amma ba su ne gashin fikafikan ƙauna ba.

14 Jimina takan bar wa ƙasa ƙwayayenta, Ta bar ƙasa ta ɗumama su.

15 Takan manta wani ya iya taka su su fashe, Ya yiwu kuma wani naman jeji ya tattake su.

16 Takan yi wa 'ya'yanta mugunta, Sai ka ce ba nata ba ne, Ko da yake ta sha wahala a banza, Duk da haka ba ta damu ba.

17 Gama Allah bai ba ta hikima ba, Bai kuwa ba ta fahimi ba.

18 Amma sa'ad da ta sheƙa a guje, Takan yi wa doki maguji da mahayinsa dariya.

19 “Kai ka yi wa doki ƙarfinsa? Kai ne kuma ka daje wuyansa da geza?

20 Kai ne ka sa shi tsalle kamar ɗango? Kwarjinin firjinsa yana da bantsoro.

21 Yakan yi nishi a fadama, Yana murna saboda ƙarfinsa, A wurin yaƙi ba ya ja da baya, ba ya jin tsoron kibau.

22 Tsoro abin dariya ne a gare shi, bai damu ba. Ba ya ba da baya ga takobi,

23 Kibau na ta shillo a kansa, Māsu suna ta gilmawa a gabansa.

24 Da tsananin fushi da hasala yana kartar ƙasa, Da jin ƙarar ƙaho, sai ya yi ta zabura.

25 Sa'ad da aka busa ƙaho yana ce, ‘Madalla.’ Yakan ji warin yaƙi daga nesa, da hargowar sarakunan yaƙi da ihunsu.

26 “Ta wurin hikimarka ne shirwa take tashi, Ta buɗe fikafikanta ta nufi kudu?

27 Ta wurin umarninka ne gaggafa take tashi sama Ta yi sheƙarta can ƙwanƙoli?

28 A kan dutse take zaune, a can take gidanta, Cikin ruƙuƙin duwatsu.

29 Daga can takan tsinkayi abincinta Idanunta sukan hango shi tun daga nesa.

30 'Yayanta sukan tsotsi jini, A inda kisassu suke, can take.”

40

1 Ubangiji ya yi wa Ayuba magana.

2 “Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka? Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.”

3 Ayuba ya amsa wa Ubangiji ya ce,

4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba, Wace amsa zan ba ka? Na rufe bakina na yi gam.

5 Ai, na riga na yi magana sau ɗaya, har ma sau biyu, Ba zan amsa ba, ba zan ƙara cewa kome ba.”

6 Sa'an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba daga cikin guguwa, ya ce,

7 “Tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji, Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

8 Kai kanka za ka sa mini laifi? Za ka kā da ni don kai ka barata?

9 Kana da ƙarfi kamar na Allah? Kana iya tsawa da murya kamar tasa?

10 “Ka caɓa ado da kwarjini da ɗaukaka, Ka yafa daraja da maƙami.

11 Ka kwararar da rigyawar fushinka, Ka dubi dukan wanda yake alfarma, a wulakance.

12 Ka dubi dukan wanda yake alfarma ka ƙasƙantar da shi, Ka tattake mugaye a inda suke.

13 Dukansu ka binne su a ƙasa, Ka ɗaure fuskokinsu, ka jefa su a lahira.

14 Sa'an nan ni kaina kuma zan sanar da kai, Cewa da hannun damanka za ka yi nasara.

15 “Ga dorina wanda ni na halicce ta, Kamar yadda na halicce ka, Tana cin ciyawa kamar sa.

16 Ga shi, ƙarfinta yana cikin ƙugunta, Ikonta yana cikin tsakar cikinta.

17 Na yi mata wutsiya miƙaƙƙiya, mai ƙarfi kamar itacen al'ul, Jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe wuri ɗaya

18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, Gaɓoɓinta kamar sandunan ƙarfe ne.

19 “Ita ce ta farko cikin ayyukan Allah, Sai Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkararta da takobi!

20 Gama duwatsu suke ba ta abinci, A inda dukan namomin jeji suke wasa.

21 Takan kwanta a inuwar ƙaddaji, Ta ɓuya a cikin iwa, da a fadama.

22 Gama inuwar da take rufe ta ta ƙaddaji ce, Itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.

23 Ga shi, ba ta jin tsoron tumbatsar kogi, A natse take, ko da ta bakinta rigyawar Urdun take wucewa.

24 Akwai wanda zai iya kama ta da ƙugiya, Ko ya sa mata asirka?”

41

1 “Ka iya kama dodon ruwa da ƙugiyar kama kifi? Ko kuma ka iya zarge harshensa da igiya?

2 Ka iya sa wa hancinsa asirka? Ko ka iya huda muƙamuƙinsa da ƙugiya?

3 Zai ta yi maka godo? Zai yi maka magana da tattausar murya?

4 Zai ƙulla alkawari da kai, Cewa zai zama baranka har abada?

5 Za ka yi wasa da shi kamar yadda za ka yi da tsuntsu? Ko za ka ɗaure shi da tsarkiya domin barorinka mata?

6 'Yan kasuwa za su saye shi? Za su karkasa shi ga fatake?

7 Za ka iya huhhuda fatarsa da zaguna? Ko kuwa kansa da māsu?

8 In ka kama shi, ka daɗe kana tunawa da yaƙin da ba za ka ƙara marmarin yi ba!

9 Ba ma amfani a yi ƙoƙarin kama shi, Tunanin yin haka ma abin tsoro ne.

10 Ba wani mai zafin hali da zai kuskura ya tsokane shi. Wane ne wannan da zai iya tsayawa a gabana?

11 Wa ya ba ni har da zan biya shi? Dukan abin da yake cikin duniyan nan nawa ne.

12 “Ba zan yi shiru a kan zancen gaɓoɓinsa ba, Ko babban ƙarfinsa, ko kyan ƙirarsa.

13 Wa zai iya yaga babbar rigarsa? Ko kuwa ya kware sulkensa da aka ninka biyu?

14 Wa zai iya buɗe leɓunansa? Gama haƙoransa masu bantsoro ne.

15 An yi gadon bayansa da jerin garkuwoyi ne, An haɗa su daɓa-daɓa kamar an liƙe.

16 Suna haɗe da juna gam, Ko iska ba ta iya ratsa tsakaninsu.

17 Sun manne da juna har ba su rabuwa.

18 Atishawarsa takan walƙata walƙiya, Idanunsa kuma kamar ketowar alfijir.

19 Harsunan wuta kamar jiniya suna fitowa daga bakinsa, Tartsatsin wuta suna ta fitowa.

20 Hayaƙi na fita daga hancinsa Kamar tururi daga tukunya mai tafasa, Ko bāgar da ta kama wuta.

21 Numfashinsa yakan kunna gawayi, Harshen wuta yana fita daga bakinsa.

22 A wuyansa ƙarfi yake zaune, Razana tana rausaya a gabansa.

23 Namansa yana ninke, manne da juna, Gama ba ya motsi.

24 Zuciyarsa tana da ƙarfi kamar dutse, Ƙaƙƙarfa kamar dutsen niƙa.

25 Sa'ad da ya miƙe tsaye, ƙarfafa sukan tsorata, Su yi ta tutturmushe juna.

26 Ko an sare shi da takobi, Ko an nashe shi da māshi ko hargi, ko an jefe shi, Ba sa yi masa kome.

27 Kamar ciyawa baƙin ƙarfe yake a gare shi, Tagulla ma kamar ruɓaɓɓen itace take.

28 Kibiya ba za ta sa ya gudu ba, Jifar majajjawa a gare shi kamar jifa da tushiyoyi ce.

29 A gare shi kulake kamar tushiyoyi ne, Kwaranniyar karugga takan ba shi dariya.

30 Kaifin ƙamborin cikinsa kamar tsingaro ne. Yana jan ciki a cikin laka kamar lular ƙarfe.

31 Yakansa zurfafa su tafasa kamar tukunya, Teku kuwa kamar kwalabar man shafawarsa.

32 Idan yana wucewa sai a ga hasken dārewar ruwa, Yakansa zurfafa su yi kumfa.

33 A duniya ba kamarsa, Taliki ne wanda ba shi da tsoro.

34 Yakan dubi kowane abu da yake mai alfarma, Shi sarki ne a bisa dukan masu girmankai.”

42

1 Ayuba ya amsa wa Ubangiji.

2 “Na sani kai kake da ikon yin dukan abu, Ba wanda ya isa ya hana ka yin abin da ka nufa.

3 Wane ne wannan marar ilimi da zai ɓoye shawara? Saboda haka na hurta abin da ban gane ba, Abubuwa waɗanda ban gane ba suna banmamaki ƙwarai.

4 Ka ce, ‘Kasa kunne, zan yi magana da kai, Zan yi maka tambaya, ka ba ni amsa.’

5 Dā jin labarinka nake, Amma yanzu na gan ka ido da ido.

6 Saboda haka na ga ni ba kome ba ne, Na tuba, ina hurwa da ƙura da toka.”

7 Bayan da Ubangiji ya gama faɗa wa Ayuba waɗannan magana, sai ya ce wa Elifaz, mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokan nan naka biyu, gama ba ku faɗi gaskiya game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.

8 Yanzu fa, sai ku kama bijimai bakwai da raguna bakwai, ku kai wa Ayuba, ku miƙa su hadaya ta ƙonawa domin kanku. Ayuba zai yi addu'a dominku, ni kuwa zan amsa addu'arsa don kada in sāka muku bisa ga wautarku. Gama ba ku faɗi gaskiya game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.”

9 Sai Elifaz mutumin Teman, da Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na'ama suka tafi suka yi kamar yadda Ubangiji ya faɗa musu, Ubangiji kuwa ya karɓi addu'ar Ayuba.

10 Ubangiji kuwa ya mayar wa Ayuba da dukiyarsa, sa'ad da ya yi addu'a domin abokansa, sai Ubangiji ya mayar masa da riɓin abin da yake da shi dā.

11 Sa'an nan dukan 'yan'uwan Ayuba mata da maza da dukan waɗanda suka san shi a dā, suka zo gidansa suka ci abinci tare da shi, suka yi juyayin abin da ya same shi, suka ta'azantar da shi,saboda dukan wahalar da Ubangiji ya aukar masa. Kowannensu ya ba shi 'yan kuɗi da zoben zinariya.

12 Ubangiji ya sa wa wannan zamani na Ayuba albarka, har fiye da na farko. An ba shi tumaki dubu goma sha huɗu (14,000), da raƙuma dubu shida (6,000), da takarkari dubu biyu (2,000), da jakai mata dubu ɗaya (1,000).

13 Ya kuma haifi 'ya'ya maza bakwai, mata uku.

14 Ya raɗa wa ta farin suna Yemima, da ta biyun Keziya,da ta ukun Keren-Haffuk.

15 Duk ƙasar ba 'yan mata kyawawa kamar 'ya'yan Ayuba. Mahaifinsu kuwa ya ba su gādo tare da 'yan'uwansu maza.

16 Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba'in bayan wannan, ya ga 'ya'yansa, ya ga jikokin jikokinsa har tsara ta huɗu.

17 Sa'an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.