1

1 Waɗannan su ne sunayen 'ya'ya maza na Isra'ila, waɗanda suka tafi Masar tare da Yakubu, kowanne da iyalinsa.

2 Su ne Ra'ubainu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza,

3 da Issaka, da Zabaluna, da Biliyaminu,

4 da Dan, da Naftali, da Gad, da Ashiru.

5 Zuriyar Yakubu duka mutum saba'in ne, Yusufu kuwa, an riga an kai shi Masar.

6 Ana nan sai Yusufu ya rasu, shi da dukan 'yan'uwansa na wannan tsara.

7 Amma 'ya'yan Isra'ila suka hayayyafa, suka ƙaru ƙwarai, suka riɓaɓɓanya, suka ƙasaita ƙwarai da gaske, har suka cika ƙasar.

8 A wannan lokaci kuwa aka yi wani sabon sarki a Masar wanda bai san Yusufu ba.

9 Sai ya ce wa mutanensa, “Duba, jama'ar Isra'ila sun cika yawa sun fi ƙarfinmu.

10 Zo, mu san irin dabarar da za mu yi musu, don kada su riɓaɓɓanya, domin in aka faɗa mana da yaƙi, kada su haɗa kai da maƙiyanmu, su yaƙe mu, su tsere daga ƙasar.”

11 Suka kuwa naɗa musu shugabannin aikin gandu domin su wahalshe su da mawuyacin aiki. Aka sa su su gina wa Fir'auna biranen ajiya, wato Fitom da Ramases.

12 Amma ko da yake Masarawa sun ƙara tsananta musu, duk da haka sai suka ƙara ƙaruwa, suna ta yaɗuwa. Masarawa kuwa suka tsorata saboda Isra'ilawa.

13 Suka kuma tilasta wa Isra'ilawa su yi ta aiki mai tsanani.

14 Suka baƙanta musu rai da aiki mai tsanani na kwaɓa, da yin tubali, da kowane irin aiki a saura. A cikin ayyukansu duka suka tsananta musu.

15 Sarkin Masar ya ce wa ungozomar Ibraniyawa, Shifra da Fu'a,

16 “Sa'ad da kuke yi wa matan Ibraniyawa hidimarku ta ungozomai, in kuka gan su durƙushe, in jariri ne suka haifa, sai ku yi masa sanadin mutuwa, in kuma jaririya ce, ku bar ta da rai.”

17 Amma da yake ungozomar masu tsoron Allah ne, ba su yi yadda Sarkin Masar ya umarce su ba, amma suka bar 'ya'ya maza da rai.

18 Don haka Sarkin Masar ya kirawo ungozomar, ya ce musu, “Me ya sa kuka bar 'ya'ya maza da rai?”

19 Ungozomar suka ce wa Fir'auna, “Domin matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gama su masu ƙwazo ne, sukan haihu tun ungozomar ba su kai wurinsu ba.”

20 Allah kuwa ya yi wa ungozoman nan alheri. Mutanen suka riɓanya, suka ƙasaita ƙwarai.

21 Allah kuma ya ba ungozoman nan zuriya domin sun ji tsoronsa.

22 Fir'auna kuwa ya umarci dukan mutanensa ya ce, “Duk jaririn da aka haifa wa Ibraniyawa, sai ku jefa shi cikin Kogin Nilu, amma idan jaririya ce, ku bar ta da rai.”

2

1 Sai wani mutum, Balawe, ya auro 'yar Lawi.

2 Matar kuwa ta yi ciki, ta haifi ɗa. Sa'ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har wata uku.

3 Da ta ga ba za ta iya ƙara ɓoye shi ba, sai ta saƙa kwando da iwa, ta yaɓe shi da katsi, ta sa jaririn a ciki, ta ajiye shi cikin kyauro a bakin Kogin Nilu.

4 Ga 'yar'uwarsa kuma a tsaye daga nesa don ta san abin da zai same shi.

5 Gimbiya, wato 'yar Fir'auna, ta gangaro domin ta yi wanka a Kogin Nilu, barorinta 'yan mata suna biye da ita a gaɓar Kogin Nilu. Da ta ga kwando a cikin kyauro, ta aiki baranyarta ta ɗauko mata shi.

6 Sa'ad da ta tuɗe kwandon ta ga jariri yana kuka. Sai ta ji tausayinsa, ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin 'ya'yan Ibraniyawa ne.”

7 'Yar'uwar jaririn kuwa ta ce wa Gimbiya, “In tafi in kirawo miki wata daga cikin matan Ibraniyawa da za ta yi miki renon ɗan?”

8 Sai Gimbiya ta ce mata, “Je ki.” Yarinyar kuwa ta tafi ta kirawo mahaifiyar jaririn.

9 Da ta zo, sai Gimbiya ta ce mata, “Dauki wannan jariri, ki yi mini renonsa, zan biya ki ladanki.” Matar kuwa ta ɗauki jaririn ta yi renonsa.

10 Da jaririn ya yi girma sai ta kai shi wurin Gimbiyar. Yaro kuwa ya zama tallafinta. Ta raɗa masa suna Musa, gama ta ce, “Domin na tsamo shi daga cikin ruwa.”

11 Ana nan wata rana, sa'ad da Musa ya yi girma, ya tafi wurin mutanensa, sai ya ga yadda suke shan wahala. Ya kuma ga wani Bamasare yana dūkan Ba'ibrane, ɗaya daga cikin 'yan'uwansa.

12 Da ya waiwaya, bai ga kowa ba, sai ya kashe Bamasaren, ya turbuɗe shi cikin yashi.

13 Kashegari da ya sāke fita, sai ya ga waɗansu Ibraniyawa biyu suna faɗa da juna. Ya ce wa wanda yake ƙwaran ɗan'uwansa, “Me ya sa kake bugun ɗan'uwanka?”

14 Ya amsa, ya ce, “Wa ya naɗa ka sarki ko alƙali a bisanmu? So kake ka kashe ni kamar yadda ka kashe Bamasaren?” Sai Musa ya tsorata, ya ce, “Assha, ashe, an san al'amarin!”

15 Da Fir'auna ya ji, sai ya nema ya kashe Musa. Amma Musa ya gudu daga gaban Fir'auna, ya tafi, ya zauna a ƙasar Madayana. Da ya kai, sai ya zauna a bakin wata rijiya.

16 Ana nan waɗansu 'yan mata bakwai, 'ya'yan firist na Madayana suka zo su cika komaye da ruwa domin su shayar da garken mahaifinsu.

17 Sai makiyaya suka zo, suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su, ya kuma shayar da garkensu.

18 Lokacin da suka koma wurin mahaifinsu, Reyuwel, wato Yetro, ya ce musu, “Yaya aka yi yau, kuka komo da sauri haka?”

19 Sai suka ce, “Wani Bamasare ne ya cece mu daga hannun makiyaya, har ya ɗebo ruwa, ya shayar da garkenmu.”

20 Reyuwel kuwa ya ce wa 'ya'yansa mata, “A ina yake? Me ya sa ba ku zo da shi ba? Ku kirawo shi, ya zo, ya ci abinci.”

21 Musa kuwa ya yarda ya zauna tare da Reyuwel. Sai ya aurar wa Musa da 'yarsa Ziffora.

22 Ita kuwa ta haifa masa ɗa, ya raɗa masa suna Gershom, gama ya ce, “Baƙo ne ni, a baƙuwar ƙasa.”

23 Ana nan, a kwana a tashi, sai Sarkin Masar ya rasu. Jama'ar Isra'ila suka yi nishi, suka yi kuka kuma saboda bautarsu, kukansu na neman gudunmawa ya kai gun Allah.

24 Allah kuwa ya ji nishinsu, sai ya tuna da alkawarinsa da ya yi wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.

25 Allah ya dubi jama'ar Isra'ila, ya kuwa kula da su.

3

1 Wata rana, sa'ad da Musa yake kiwon garken surukinsa, Yetro, firist na Madayana, sai ya kai garken yammacin jeji, har ya zo Horeb, wato dutsen Allah.

2 A can mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi cikin harshen wuta daga cikin kurmi. Da Musa ya duba, sai ga kurmin yana cin wuta, amma duk da haka bai ƙone ba.

3 Musa kuwa ya ce, “Bari in ratse, in ga wannan abin banmamaki da ya sa kurmin bai ƙone ba.”

4 Sa'ad da Ubangiji ya ga ya ratse don ya duba, sai Allah ya kira shi daga cikin kurmin, ya ce, “Musa, Musa.” Musa ya ce, “Ga ni.”

5 Allah kuwa ya ce, “Kada ka matso kusa, ka cire takalminka, gama wurin da kake tsaye, tsattsarka ne.”

6 Ya kuma ce, “Ni ne Allah na kakanninka, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.” Sai Musa ya ɓoye fuskarsa, gama yana jin tsoro ya dubi Allah.

7 Ubangiji kuwa ya ce, “Na ga wahalar jama'ata waɗanda suke a Masar, na kuma ji kukansu da suke yi a kan shugabanninsu. Na san wahalarsu,

8 don haka na sauko in cece su daga hannun Masarawa, in fito da su daga cikin wannan ƙasa zuwa kyakkyawar ƙasa mai ba da yalwar abinci, wato ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa.

9 Yanzu fa, ga shi, kukan jama'ar Isra'ila ya zo gare ni. Na kuma ga wahalar da Masarawa suke ba su.

10 Zo, in aike ka wurin Fir'auna domin ka fito da jama'ata, wato Isra'ilawa, daga cikin Masar.”

11 Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi gaban Fir'auna in fito da Isra'ilawa daga cikin Masar?”

12 Sai Allah ya ce, “Zan kasance tare da kai, wannan kuwa zai zama alama a gare ka, cewa ni ne na aike ka. Sa'ad da ka fito da jama'ar daga Masar, za ku bauta wa Allah a bisa dutsen nan.”

13 Sai Musa ya ce wa Allah, “Idan na je wurin Isra'ilawa na ce musu, ‘Allah na ubanninku ya aiko ni gare ku,’ idan sun ce mini, ‘Yaya sunansa?’ Me zan faɗa musu?”

14 Allah kuwa ya ce wa Musa, “NI INA NAN YADDA NAKE,” ya kuma ce, “Haka za ka faɗa wa Isra'ilawa, ‘NI NE ya aiko ni gare ku.”’

15 Allah kuma ya sāke ce wa Musa, “Faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Ubangiji Allah na kakanninku, wato na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu ya aiko ni gare ku.’ Wannan shi ne sunana har abada. Da wannan suna za a tuna da ni a dukkan zamanai.

16 Tafi, ka tattara dattawan Isra'ila, ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah na kakanninku ya bayyana gare ni, wato na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, ya ce, sosai ya ziyarce ku, ya kuma ga abin da ake yi muku a Masar.

17 Ya yi alkawari cewa zai fisshe ku daga wahalar Masar zuwa ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. Ƙasa wadda take mai ba da yalwar abinci.’

18 Za su kasa kunne ga muryarka. Sa'an nan kai da dattawan Isra'ila za ku tafi gaban Sarkin Masar ku ce masa, ‘Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya gamu da mu. Yanzu fa, muna roƙonka, ka yarda mana mu yi tafiyar kwana uku a cikin jeji mu miƙa masa hadaya.’

19 Amma na sani Sarkin Masar ba zai bar ku ku fita ba, sai an yi masa tilas.

20 Domin haka zan miƙa hannuna in bugi Masar da dukan mu'ujizaina waɗanda zan aikata cikinta, sa'an nan zai bar ku ku fita.

21 “Zan sa wannan jama'a su yi farin jini a idanun Masarawa, sa'ad da kuka fita kuma, ba za ku fita hannu wofi ba.

22 Amma kowace mace za ta roƙi maƙwabciyarta da wadda take cikin gidanta kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, za ku sa wa 'ya'yanku mata da maza. Da haka za ku washe Masarawa.”

4

1 Musa kuwa ya amsa ya ce, “Ai, ba za su gaskata ni ba, ba kuma za su kasa kunne ga maganata ba, gama za su ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba.”’

2 Amma Ubangiji ya ce masa, “Mene ne wannan a hannunka?” Ya ce, “Sanda ne.”

3 Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Sai ya jefa shi ƙasa, sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya yi gudunsa.

4 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka ka kama wutsiyarsa.” Ya miƙa hannunsa ya kama shi, ya zama sanda kuma a hannunsa.

5 Sai Ubangiji ya ce, “Ta haka za su gaskata Ubangiji Allah na kakanninsu ne, wato na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, ya bayyana gare ka.”

6 Sai Ubangiji ya sāke ce masa, “Sa hannunka cikin ƙirjinka.” Sa'ad da ya fitar da shi, ga hannunsa a kuturce fari fat.

7 Allah kuma ya ce masa, “Mai da hannunka cikin ƙirjinka.” Sai ya mai da hannunsa cikin ƙirjinsa. Sa'ad da ya fitar da shi, ga hannun ya koma kamar sauran jikinsa.

8 Ubangiji kuma ya ce, “Idan kuma ba su gaskata ka ba, ba su kuma kula da mu'ujiza ta fari ba, ya yiwu su gaskata ta biyun.

9 Idan ba su gaskata mu'ujizan nan biyu ba, ba su kuma kula da maganarka ba, sai ka ɗibi ruwa daga Kogin Nilu, ka zuba bisa busasshiyar ƙasa. Ruwan zai zama jini a bisa busasshiyar ƙasa.”

10 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangijina, ni ba mai lafazi ba ne, ban taɓa zama ba, ko a yanzu ma, bayan da ka yi magana da bawanka, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”

11 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Wa ya yi bakin ɗan adam? Wa ya yi bebe ko kurma, ko mai gani ko makaho? Ko ba ni Ubangiji ba ne?

12 Yanzu fa, tafi, zan kasance tare da bakinka, in koya maka abin da za ka faɗa.”

13 Amma Musa ya ce, “Ya Ubangijina, in ka yarda, ka aiki wani.”

14 Ubangiji kuwa ya hasala da Musa, ya ce, “Haruna ɗan'uwanka Balawe ba ya nan ne? Lalle na san shi ya iya magana, ga shi nan ma, yana fitowa ya tarye ka. Sa'ad da ya gan ka kuwa zai yi murna cikin zuciyarsa.

15 Sai ka yi magana da shi. Ka kuma sa masa maganata a baka, zan kuwa kasance tare da bakinka da bakinsa. Zan kuma sanar da ku abin da za ku yi.

16 Shi zai yi maka magana da jama'a, zai zama bakinka, kai kuwa za ka zama kamar Allah a gare shi.

17 Za ka riƙe wannan sanda a hannunka, da shi za ka aikata mu'ujizan.”

18 Musa ya koma wurin Yetro, surukinsa, ya ce masa, “Ina roƙonka, ka bar ni in koma wurin 'yan'uwana a Masar, in ga ko a raye suke har yanzu.” Sai Yetro ya ce wa Musa, “Ka tafi lafiya.”

19 Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa a Madayana, ya koma Masar, gama dukan waɗanda suke neman ransa sun rasu.

20 Saboda haka Musa ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa maza, ya haushe su bisa kan jaki, ya koma ƙasar Masar, yana riƙe da sandan Allah a hannunsa.

21 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Sa'ad da ka koma Masar, sai ka kula, ka aikata a gaban Fir'auna dukan mu'ujizan da na sa cikin ikonka. Amma zan taurara zuciyarsa, don kada ya bar jama'a su fita.

22 Za ka ce wa Fir'auna, Ubangiji ya ce, ‘Isra'ila ɗan fārina ne.

23 Na ce maka ka bar ɗana ya tafi domin ya bauta mini, amma in ka ƙi ka bar shi ya tafi, yanzu zan kashe ɗan fārinka.”’

24 Ya zama kuwa sa'ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.

25 Sai Ziffora ta ɗauki ƙanƙara ta yanke loɓar ɗanta, ta taɓa gaban Musa da shi, ta ce, “Kai angon jini kake a gare ni.”

26 Sa'an nan Ubangiji ya ƙyale shi. Ta kuma ce, “Kai angon jini ne,” saboda kaciyar.

27 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi, ka taryi Musa cikin jeji.” Ya kuwa tafi ya tarar da shi a dutsen Allah, ya sumbace shi.

28 Sa'an nan Musa ya faɗa wa Haruna abubuwan da Ubangiji ya aike shi ya yi, da dukan mu'ujizan da ya umarce shi ya aikata.

29 Sai Musa da Haruna suka tafi suka tattara dukan dattawan Isra'ila.

30 Haruna dai ya hurta wa dattawan al'amuran da Ubangiji ya faɗa wa Musa. Ya kuma aikata mu'ujizan a idanunsu.

31 Dattawan kuwa suka gaskata. Sa'ad da suka ji Ubangiji ya ziyarci Isra'ilawa, ya kuma ga wahalarsu, sai suka sunkuya, suka yi masa sujada.

5

1 Bayan wannan Musa da Haruna suka tafi gaban Fir'auna, suka ce, “Ga abin da Ubangjiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Bar jama'ata su tafi domin su yi mini idi cikin jeji.”’

2 Amma Fir'auna ya ce, “Wane ne Ubangiji, har da zan ji maganarsa, in bar Isra'ilawa su tafi? Ai, ban san Ubangiji ɗin nan ba, balle in bar Isra'ilawa su tafi.”

3 Sai suka ce, “Allahn Ibraniyawa ya gamu da mu, muna roƙonka, ka bar mu mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji domin mu yi wa Ubangiji Allahnmu hadaya, don kada ya aukar mana da annoba ko takobi.”

4 Amma Sarkin Masar ya ce wa Musa da Haruna, “Me ya sa kuke hana jama'ar yin aikinsu? Ku tafi wurin aikin gandunku.”

5 Ya kuwa ci gaba ya ce, “Ga jama'ar ƙasar sun yi yawa, yanzu kuna so ku hana su yin aikinsu.”

6 A ran nan fa Fir'auna ya umarci shugbannin aikin gandu da manyan jama'a, ya ce,

7 “Nan gaba kada ku ƙara ba mutanen nan budu na yin tubali kamar dā. Ku sa su, su tafi, su tara budu da kansu.

8 Duk da haka, kada su kāsa cika yawan tubalin da aka ƙayyade musu da fari. Ai, su ragwaye ne, shi ya sa suke kuka, suna cewa, ‘A bar mu, mu tafi mu miƙa wa Allahnmu hadaya.’

9 Ku sa mutanen su yi aiki mai tsanani har da ba za su sami damar kasa kunne ga maganganun ƙarya ba.”

10 Sai shugabannin aikin gandu da manyan jama'a suka tafi suka faɗa wa jama'a cewa, “Ga abin da Fir'auna ya ce, ‘Ba zan ba ku budu ba.

11 Ku je, ku da kanku, ku nemi budu inda duk za ku iya samowa, amma daɗai, ba za a sawwaƙe muku aikinku ba.”’

12 Sai jama'a suka watsu ko'ina cikin ƙasar Masar, suna tattara budu.

13 Shugabannin aikin gandun suka matsa musu, suna cewa, “Sai ku cika aikinku na kowace rana daidai yadda kuke yi a dā lokacin da ake ba ku budu.”

14 Aka kuwa bulali manya waɗanda suke Isra'ilawa waɗanda shugabannin aikin gandu na Fir'auna suka sa a bisa Isra'ilawa, ana cewa, “Me ya sa jiya da yau ba ku cika yawan tubalin da aka ƙayyade, kamar dā ba?”

15 Manyan Isra'ilawa kuwa suka tafi suka yi kuka a gaban Fir'auna, suka ce, “Me ya sa ka yi wa bayinka haka?

16 Ba a ba mu budu, amma ana ce mana mu yi tubali. Ga shi ma, dūkan bayinka suke yi. Ai, jama'arka ne suke da laifin.”

17 Fir'auna kuwa ya ce musu, “Ku ragwaye ne ƙwarai, shi ya sa kuke cewa a bar ku ku tafi, ku miƙa wa Ubangiji hadaya.

18 Ku tafi, ku kama aiki, ba za a ba ku budu ba, duk da haka za ku cika yawan tubali da aka sa muku.”

19 Manyan Isra'ilawa suka ga lalle sun shiga uku, da yake aka ce dole su cika yawan tubali da aka yanka musu kowace rana.

20 Da suka fita daga gaban Fir'auna, sai suka sadu da Musa da Haruna, suna jiransu.

21 Suka ce wa Musa da Haruna, “Allah ya duba, ya hukunta ku, gama kun sa mun yi baƙin jini a wurin Fir'auna da barorinsa, har suka ɗauki takobi don su kashe mu.”

22 Sai Musa ya koma wurin Ubangiji, ya ce, “Ya Ubangijina, me ya sa ka jawo wa wannan jama'a masifa? Me ya sa ka aike ni?

23 Gama tun da na tafi wurin Fir'auna, na yi masa magana da sunanka, ya mugunta wa wannan jama'a, kai kuwa ba ka ceci jama'arka ba ko kaɗan!”

6

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Yanzun nan, za ka ga abin da zan yi da Fir'auna. Gama zan tilasta shi ya bar su su fita, har ma ya iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”

2 Allah kuma ya yi magana da Musa, ya ce, “Ni ne Ubangiji.

3 Na bayyana ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu a kan ni Allah Maɗaukaki ne, amma sunan nan nawa, Yahweh, ban sanasshe su ba.

4 Na kuma yi musu alkawari zan ba su ƙasar Kan'ana, inda suka yi zaman baƙunci.

5 Yanzu na ji nishin Isra'ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuwa tuna da alkawarina.

6 Sai ka faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Ni Ubangiji zan 'yantar da ku daga wulakancin nan da Masarawa suke yi muku. Zan kuɓutar da ku daga bautar Masarawa. Da ƙarfi zan aikata hukuntaina masu iko don in cece ku.

7 Zan tallafe ku, ku zama jama'ata, ni kuwa in zama Allahnku. A sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya 'yanto ku daga wulakancin Masarawa.

8 Sa'an nan zan kawo ku cikin ƙasar da na rantse zan bai wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. Zan ba ku ita ta zama mallakarku. Ni ne Ubangiji.”’

9 Sai Musa ya faɗa wa Isra'ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne gare shi ba, saboda ɓacin rai da tsananin bauta.

10 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

11 “Tafi gaban Fir'auna, Sarkin Masar, ka faɗa masa ya bar Isra'ilawa su fita ƙasa tasa.”

12 Amma Musa ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Duba, tun da yake Isra'ilawa ba su kasa kunne gare ni ba, yaya Fir'auna zai kasa kunne gare ni, ni mutum mai nauyin baki?”

13 Ubangiji kuma ya yi magana da Musa da Haruna, su tafi wurin Isra'ilawa da wurin Fir'auna, Sarkin Masar, su ba su umarni, su kuma fito da Isra'ilawa daga cikin ƙasar Masar.

14 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu. 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, ɗan farin Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi. Waɗannan su ne iyalan kabilar Ra'ubainu.

15 'Ya'yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Ohad, da Yakin, da Zohar, da Shawul ɗan Bakan'aniya, waɗannan su ne iyalan kabilar Saminu.

16 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Lawi bisa ga iyalansu, Gershon, da Kohat, da Merari. Lawi ya rayu shekara ɗari da talatin da bakwai.

17 'Ya'yan Gershon, maza kuwa, su ne Libni, da Shimai bisa ga iyalansu.

18 'Ya'ya maza na Kohat kuwa, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel. Kohat ya rayu shekara ɗari da talatin da uku.

19 'Ya'ya maza na Merari, su ne Mali, da Mushi. Waɗannan su ne kabilar Lawi bisa ga zuriyarsu.

20 Amram ya auri Yokabed 'yar'uwar mahaifinsa, ta kuwa haifa masa Haruna da Musa. Amram ya rayu shekara ɗari da talatin da bakwai.

21 'Ya'yan Izhara, su ne Kora, da Nefeg, da Zikri.

22 'Ya'ya maza na Uzziyel, su ne Mishayel, da Elzafan, da Zitri.

23 Haruna ya auri Elisheba, 'yar Amminadab 'yar'uwar Nashon. Sai ta haifa masa Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.

24 'Ya'ya maza na Kora, su ne Assir, da Elkana, da Abiyasaf. Waɗannan su ne iyalin Kora.

25 Ele'azara, ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Futiyel. Ita kuwa ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan kabilar Lawi bisa ga kabilansu.

26 Wannan Haruna ne da Musa, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana su fito da Isra'ilawa daga cikin ƙasar Masar, ƙungiya ƙungiya.

27 Su ne waɗanda suka yi magana da Sarkin Masar ya bar Isra'ilawa su fita daga Masar. Musa da Haruna ne suka yi wannan.

28 Wata rana Ubangiji ya yi magana da Musa a ƙasar Masar ya ce,

29 “Ni ne Ubangiji, sai ka faɗa wa Fir'auna, Sarkin Masar, dukan abin da na faɗa maka.”

30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, yaya Fir'auna zai kasa kunne gare ni?”

7

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, zan maishe ka kamar Allah ga Fir'auna. Ɗan'uwanka, Haruna kuwa, zai zama manzonka.

2 Kai za ka faɗa wa Haruna, ɗan'uwanka, dukan abin da na umarce ka, shi kuwa zai faɗa wa Fir'auna ya bar Isra'ilawa su fita ƙasa tasa.

3 Amma zan taurare zuciyar Fir'auna don in aikata alamu da mu'ujizai cikin ƙasar Masar.

4 Amma Fir'auna ba zai kasa kunne gare ku ba, don haka zan miƙa hannuna a bisa Masar, zan fitar da rundunar jama'ata, wato Isra'ilawa, daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu iko.

5 Masarawa kuma za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na miƙa hannuna gāba da Masar, don in fito da Isra'ilawa daga tsakiyarsu.”

6 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarce su.

7 Musa yana da shekara tamanin, Haruna kuwa yana da shekara tamanin da uku sa'ad da suka yi magana da Fir'auna.

8 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,

9 “Idan Fir'auna ya ce muku, ‘Aikata waɗansu al'ajabai don ku nuna isarku,’ sai ka faɗa wa Haruna ya ɗauki sandansa, ya jefa shi ƙasa a gaban Fir'auna. Sandan kuwa zai zama maciji.”

10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa a gaban Fir'auna. Da sandan ya fāɗi, sai ya zama maciji.

11 Fir'auna kuwa ya kirawo shahararrun malamai, da masu sihiri, su kuma su yi haka ta wurin sihirinsu na Masarawa.

12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, sai sandunan suka zama macizai. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.

13 Duk da haka zuciyar Fir'auna ta taurare kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir'auna yana da taurin zuciya, ga shi, ya ƙi sakin jama'ar.

15 Ka tafi wurinsa da safe daidai lokacin da ya fita zai tafi Kogin Nilu. Ka jira don ka sadu da shi a bakin Nilu. Ka kuma ɗauki sandan nan wanda ya juye ya zama maciji.

16 Za ka faɗa wa Fir'auna cewa, ‘Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya aike ni gare ka da cewa ka saki jama'ar Ubangiji domin su yi masa hidima a jeji. Amma ga shi, har yanzu ba ka yi biyayya ba.

17 Ubangiji ya ce, za ka sani shi ne Ubangiji ta wurin abin da zan aikata. Zan bugi ruwan Nilu da sandan da yake hannuna, ruwan kuwa zai rikiɗe ya zama jini.

18 Kifayen da suke cikin Nilu za su mutu. Nilu kuwa zai yi ɗoyi, har da Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.”’

19 Ubangiji kuma ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya ɗauki sandansa ya miƙa shi a bisa ruwayen Masar, da kogunansu, da rafuffukansu, da fadamunsu, da dukan tafkunansu don ruwansu ya zama jini. Jini zai kasance ko'ina a ƙasar Masar, i, har ma cikin randuna.

20 Musa da Haruna kuwa suka yi daidai kamar yadda Ubangiji ya umarta. Sai Haruna ya ta da sandansa sama ya bugi ruwan Nilu a gaban Fir'auna da fādawansa. Dukan ruwan Nilu kuwa ya rikiɗe jini.

21 Kifayen da suke cikin Nilu suka mutu. Nilu kuwa ya yi ɗoyi, har Masarawa ba su iya shan ruwansa ba. Ko'ina kuma a ƙasar Masar akwai jini.

22 Masu sihiri kuma na Masar suka yi haka, su ma, ta wurin sihirinsu, don haka zuciyar Fir'auna ta daɗa taurarewa, ya kuwa ƙi jin Musa da Haruna kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

23 Sai ya juya, ya koma fādarsa, bai ko kula da abin da aka yi ba.

24 Dukan Masarawa suka tattone ramummuka a bakin Nilu, suna neman ruwan sha, gama ba su iya shan ruwan Nilu ba.

25 Kwana bakwai suka cika bayan da Ubangiji ya bugi Kogin Nilu.

8

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin Fir'auna, ka ce masa, ‘Ubangiji ya ce ka saki jama'arsa domin su yi masa sujada.

2 Idan ka ƙi sakinsu, zai hore ka da kwaɗi.

3 Nilu zai cika da kwaɗi, za su tashi, su shiga cikin fādarka, da ɗakin kwanciyarka, da gadonka, har da gidajen fadawanka da jama'arka. Za su kuma shiga matuyanka da kwanon tuwonka,

4 har ma za su hau bisa kanka, da jama'arka, da dukan fādawanka.’ ”

5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya miƙa sandansa a bisa koguna, da rufuffuka, da tafkuna don ya sa kwaɗi su fito, su rufe ƙasar Masar.

6 Haruna ya miƙa sandansa a bisa ruwayen Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka rufe ƙasar Masar.

7 Masu sihiri kuma suka sa kwaɗi su fito a bisa ƙasar Masar ta wurin sihirinsu.

8 Sai Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna, ya ce su roƙi Ubangiji ya kawar masa da kwaɗin, shi da mutanensa, sa'an nan zai saki jama'ar, su tafi su miƙa wa Ubangiji hadaya.

9 Musa ya ce wa Fir'auna, “In ka yarda, a wane lokaci ne kake so in roƙa maka, kai da barorinka da jama'arka domin a kawar da kwaɗin daga gidajenku, a hallakar muku da su, sai dai na cikin Kogin Nilu za a bari?”

10 Fir'auna ya ce, “Gobe ne.” Musa kuwa ya ce, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani allah kamar Ubangiji Allahnmu.

11 Kwaɗin za su rabu da ku, da kai, da gidanka, da fādawanka, da jama'arka, sai na cikin Nilu kaɗai za a bari.”

12 Da Musa da Haruna suka fita daga gaban Fir'auna, sai Musa ya roƙi Ubangiji ya kawar da kwaɗin nan da suka azabta wa Fir'auna.

13 Ubangiji kuwa ya karɓi addu'ar Musa, sai kwaɗin da suke cikin gida da waɗanda suke kewaye da gida, da waɗanda suke cikin saura suka mutu.

14 Aka tsiba su tsibi tsibi. Suka sa ƙasar ta yi ɗoyi.

15 Da Fir'auna ya ga an kawar masa da kwaɗin, sai ya taurare zuciyarsa, ya ƙi jinsu kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

16 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya miƙa hannunsa ya bugi ƙurar ƙasar, ta zama kwarkwata a ƙasar Masar.

17 Haka kuwa suka yi. Haruna ya miƙa sandansa ya bugi ƙurar ƙasa, sai ta zama kwarkwata a bisa 'yan adam, da bisa dabbobi. Dukan ƙurar ta zama kwarkwata ko'ina cikin ƙasar Masar.

18 Masu sihiri suka ƙokarta su sa kwarkwata ta bayyana ta wurin sihirinsu, amma ba su iya ba. Kwarkwata kuma ta yayyaɓe 'yan adam da dabbobi.

19 Sai masu sihiri suka ce wa Fir'auna, “Ai, wannan aikin Allah ne.” Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, har da bai kasa kunne ga Musa da Haruna ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

20 Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe ka sami Fir'auna a daidai lokacin da ya fita za shi rafi, ka ce masa, ‘Ni Ubangiji na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada.

21 In kuwa ka ƙi sakin jama'ata, sai in koro maka ƙudaje, da kai da fādawanka, da jama'arka, da gidajen Masarawa, har ma duk da ƙasa inda suke takawa.

22 A wannan rana fa zan keɓe ƙasar Goshen inda jama'ata suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, ta haka ne za ka sani ni Ubangiji ina nan a duniya.

23 Zan sa iyaka tsakanin jama'ata da jama'arka. Gobe ne wannan mu'ujiza za ta auku.”’

24 Haka kuwa Ubangiji ya aikata. Ƙudaje masu yawa suka shiga gidan Fir'auna, da gidan fādawansa, da ko'ina a ƙasar Masar. Ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.

25 Sa'an nan Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna, ya ce, “Tafi, ku yi wa Allahnku hadaya a ƙasan nan.”

26 Amma Musa ya ce, “Ba zai kyautu a yi haka ba, gama irin dabbobin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu hadaya da su, haramu ne ga Masarawa. Idan fa muka miƙa hadaya da waɗannan dabbobi da suke haramu a idon Masarawa za su jajjefe mu da duwatsu.

27 Za mu yi tafiya kwana uku a jeji kafin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu kamar yadda ya umarce mu.”

28 Sai Firauna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, ku miƙa wa Ubangiji Allahnku hadaya a jeji, sai dai kada ku tafi da nisa. Ku kuma yi mini addu'a.”

29 Musa kuwa ya ce, “Nan da nan da tashina daga gabanka, zan yi addu'a ga Ubangiji, ƙudajen kuwa za su rabu da kai, da fādawanka, da jama'arka gobe, kada ka sāke yin ruɗi, ka ƙi barin jama'ar su tafi, su miƙa wa Ubangiji hadaya.”

30 Musa ya fita daga wurin Fir'auna, ya roƙi Ubangiji.

31 Ubangiji kuwa ya aikata bisa ga roƙon Musa. Ƙudajen suka rabu da Fir'auna, da fādawansa, da jama'arsa. Ko ƙuda ɗaya bai ragu ba.

32 Duk da haka Fir'auna ya taurare zuciyarsa a wannan lokaci kuma, ya ƙi sakin jama'ar.

9

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je ka wurin Fir'auna, ka faɗa masa cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Ibraniyawa, na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada.

2 Amma idan ka ƙi sakinsu, wato kana ta riƙonsu,

3 to, hannuna zai auka wa dabbobinka cikin sauruka, da dawakai, da jakai, da raƙuma, da shanu, da tumaki, da awaki, da annoba mai tsanani.

4 Zan raba tsakanin dabbobin Isra'ilawa, da na Masarawa. Ko ɗaya daga cikin dabbobin Isra'ilawa ba zai mutu ba. Na riga na sa lokacin.

5 Gobe ne zan aikata al'amarin nan a ƙasar.”’

6 Kashegari kuwa Ubangiji ya aikata al'amarin. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, na Isra'ilawa kuwa, ko ɗaya bai mutu ba.

7 Sai Fir'auna ya aika, ya tambaya, ashe, ko dabba guda daga cikin na Isra'ilawa ba ta mutu ba? Duk da haka zuciyar Fir'auna ta taurare, bai kuwa saki jama'ar ba.

8 Ubangiji kuma ya ce wa Musa da Haruna, “Dibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa ta sama a gaban Fir'auna.

9 Tokar za ta zama kamar ƙura a dukan ƙasar Masar, ta zama marurai, suna kuwa fitowa a jikin mutum da dabba a dukan ƙasar Masar.”

10 Sa'an nan suka ɗauko toka daga matoya, suka tsaya a gaban Fir'auna. Da Musa ya watsa ta sama, sai ta zama marurai suna ta fitowa a jikin mutum da dabba.

11 Amma masu sihirin suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran, gama suka kamu da maruran kamar sauran Masarawa.

12 Ubangiji kuma ya taurare zuciyar Fir'auna har ya ƙi jin Musa da Haruna kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa wa Musa.

13 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka je ka sami Fir'auna, ka ce masa, ‘Ni Ubangiji Allah na Ibraniyawa, na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada.

14 A wannan karo, ni da kaina zan kawo maka, da fādawanka, da jama'arka annoba, domin ka sani babu mai kama da ni a dukan duniya.

15 Gama da ni kaina na miƙa dantsena na buge ka da jama'arka da annoba, ai, da an hallakar da ku a duniya ƙaƙaf.

16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana ya zama abin darajantawa a dukan duniya.

17 Har yanzu kana fariya a kan jama'ata, ba ka sake su ba.

18 Gobe war haka zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske irin wadda Masar ba ta taɓa gani ba tun kafawarta, har zuwa yanzu.

19 Yanzu fa, sai ka ba da umarni a lura da awaki, da dukan abin da yake naku wanda yake a saura, gama duk mutum ko dabba wanda ya ragu a saura, wato wanda ba a kawo shi gida ba, zai mutu sa'ad da ƙanƙarar ta zo.”’

20 Akwai waɗansu daga cikin fādawan Fir'auna waɗanda suka tsorata saboda abin da Ubangiji ya faɗa, sai suka kawo bayinsu da dabbobinsu cikin gida.

21 Amma waɗanda ba su kula da abin da Ubangiji ya faɗa ba, suka bar bayinsu da dabbobinsu a waje cikin saura.

22 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa mutum da dabba da bisa dukan itatuwan saura a dukan ƙasar Masar.”

23 Sai Musa ya miƙa sandansa sama, Ubangiji kuwa ya aiko da tsawa da ƙanƙara, wuta kuwa ta bi ƙasar. Ubangiji ya sa aka yi ƙanƙara a bisa ƙasar Masar.

24 Ƙanƙarar tana faɗowa, wuta kuma tana tartsatsi a cikin ƙanƙara. Aka yi ƙanƙara mai tsananin gaske irin wadda ba a taɓa yi ba cikin dukan ƙasar Masar tun lokacin da ta zama al'umma.

25 Ƙanƙarar ta bugi ko'ina a Masar. Dukan abin da yake cikin saura, mutum duk da dabba, da tsire-tsire duka, ƙanƙara ta buge su. Duk itatuwan da yake a saura aka ragargaza su.

26 Sai dai a ƙasar Goshen inda Isra'ilawa suke, ba a yi ƙanƙara ba.

27 Fir'auna ya aika, aka kirawo Musa da Haruna, ya ce musu, “Lalle a wannan karo na yi laifi, Ubangiji shi ne da gaskiya. Ni da jama'ata muke da kuskure.

28 Ku roƙi Ubangiji ya tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”

29 Musa ya ce masa, “Da fitata daga cikin birnin, zan yi addu'a ga Ubangiji, walƙiya kuwa za ta tsaya, ƙanƙara kuma ta daina, don ku sani duniya ta Ubangiji ce.

30 Amma dai na sani, da kai da fādawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”

31 Rama da sha'ir suka lalace, gama sha'ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana huda.

32 Amma alkama da maiwa ba su lalace ba, gama kakarsu ba ta yi ba tukuna.

33 Sai Musa ya fita daga wurin Fir'auna ya rabu da birnin. Ya yi addu'a ga Ubangiji sai walƙiya da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.

34 Da Fir'auna ya ga an ɗauke ruwa, da ƙanƙara, da kuma walƙiya, sai ya sāke yin zunubi, ya taurare zuciyarsa, da shi da fādawansa.

35 Zuciyar Fir'auna ta taurare, har ya ƙi sakin Isra'ilawa kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta bakin Musa.

10

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Je ka wurin Fir'auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da ta fādawansa domin in aikata waɗannan mu'ujizai nawa a tsakiyarsu,

2 domin kuma ka sanar da 'ya'yanka da jikokinka yadda na shashantar da Masarawa, na kuma aikata waɗannan mu'ujizai a tsakiyarsu. Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.”

3 Saboda haka Musa da Haruna suka tafi gaban Fir'auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi yarda ka ba da kanka a gare ni? Saki jama'ata don su tafi su yi mini sujada.

4 In kuwa ka ƙi yarda ka bar jama'ata su tafi, to, gobe zan aiko da fara cikin ƙasarka,

5 za ta rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za ta cinye sauran abin da ya kuɓuta daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a ƙasar.

6 Za su cika fādarka, da dukan gidajen fādawanka, da na dukan Masarawa. Iyayenka da kakanninka ba su taɓa ganin irin faran nan ba, tun daga ran da suke ƙasar, har wa yau.”’ Sai ya juya ya fita daga gaban Fir'auna.

7 Fādawan Fir'auna kuwa suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai riƙa jawo mana masifa? Ka saki mutanen, su fita su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Ashe, har yanzu ba ka sani Masar ta lalace ba?”

8 Aka komar da Musa da Haruna gaban Fir'auna. Sai Fir'auna ya ce musu, “Ku tafi ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”

9 Musa ya amsa, “Da samarinmu, da tsofaffinmu za mu tafi, da 'ya'yanmu mata da maza za su fita tare da mu, da kuma garkunanmu da shanunmu, gama wajibi ne mu yi idi a gaban Ubangiji.

10 Fir'auna ya ce musu, “To, Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba, gama kuna da niyyar mugunta a zuciyarku.

11 Sai dai ku mazaje, ku tafi ku bauta wa Ubangiji, gama abin da kuke so ke nan.” To, aka kore su daga gaban Fir'auna.

12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa ƙasar Masar domin fara ta zo. Farar kuwa za ta rufe ƙasar Masar, ta cinye duk tsire-tsire da ganyayen da suke cikin ƙasar, da iyakar abin da ƙanƙara ta rage.”

13 Sai Musa ya miƙa sandansa bisa ƙasar Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a ƙasar dukan yini da dukan dare, har safiya. Iskar gabas ɗin kuwa ta kawo farar.

14 Farar ta mamaye ƙasar Masar, ta rufe dukan ƙasar. Ba a taɓa ganin fara ta taru da yawa kamar haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin kamar haka ba.

15 Ta rufe dukan fuskar ƙasa har ƙasar ta yi duhu. Ta cinye kowane tsiro na ƙasar da dukan 'ya'yan itatuwa waɗanda ƙanƙara ta rage. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.

16 Fir'auna ya aika da gaggawa a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.

17 Amma ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma roƙar mini Ubangiji Allahnku ya ɗauke mini wannan mutuwa.”

18 Sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna, ya tafi ya roƙi Ubangiji.

19 Ubangiji kuwa ya sa iska mai ƙarfi ta huro daga wajen yamma, ta kwashi farar, ta zuba ta a Bahar Maliya. Ko fara guda ba ta ragu a cikin iyakar Masar ba.

20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, Fir'auna kuwa ya ƙi sakin Isra'ilawa.

21 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama, domin a yi duhu cikin ƙasar Masar, irin duhun da za a iya taɓawa.”

22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuwa yi duhu baƙi ƙirin har kwana uku a dukan ƙasar Masar.

23 Mutum bai iya ganin ɗan'uwansa ba, ba kuma mutumin da ya iya fita gidansa har kwana uku. Amma akwai haske inda Isra'ilawa suke zaune.

24 Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya ce musu, “Ku tafi ku bauta wa Ubangiji, sai dai ku bar tumakinku, da awakinku, da shanunku a nan, amma ku ku tafi da 'ya'yanku.”

25 Musa kuwa ya ce, “In haka ne, kai ka ba mu abin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu hadayu da su.

26 Don haka sai mu tafi da dabbobinmu, ko kofato ba za a bari a baya ba, gama daga cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”

27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna har bai yarda ya sake su ba.

28 Fir'auna ma ya ce wa Musa, “Tafi, ka ba ni wuri, ka mai da hankali fa, kada in ƙara ganinka, gama ran da na sāke ganinka ran nan kā mutu.”

29 Sai Musa ya amsa ya ce, “Haka nan ne kuwa, ba zan ƙara ganin fuskarka ba.”

11

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yanzu dai zan ƙara bugun Fir'auna da Masarawa sau ɗayan nan kawai da annoba. Bayan wannan zai sake ku. Sa'ad da ya bar ku ku tafi, zai iza ƙyeyarku.

2 Sai ka faɗa wa jama'a, kowane mutum da kowace mace su roƙi kayan ado na azurfa da na zinariya daga wurin maƙwabtansu.”

3 Ubangiji kuwa ya sa jama'a su yi farin jini a idanun Masarawa. Musa kuwa ya zama babban mutum a ƙasar Masar a gaban fādawan Fir'auna da kuma gaban jama'ar.

4 Musa ya ce wa Fir'auna, “Ga abin da Ubangiji ya faɗa, ‘A wajen tsakar dare zan ratsa cikin Masar.

5 Kowane ɗan farin da yake ƙasar Masar zai rasu, daga ɗan farin Fir'auna wanda zai hau gadon sarautarsa, har zuwa ɗan farin kuyanga wadda take niƙa, da dukan ɗan farin shanu.

6 Za a kuwa yi kuka mai zafi ko'ina a ƙasar Masar irin wanda ba a taɓa yi ba, ba kuma za a ƙara yi ba.

7 Amma ko kare ba zai yi wa wani mutum ko dabba na Isra'ila haushi ba, domin ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masarawa da Isra'ilawa.’

8 Sa'an nan dukan fādawanka za su zo wurina su fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama'arka!’ Sa'an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna a husace.

9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir'auna ba zai kasa kunne gare ka ba, sai na ƙara aikata waɗansu mu'ujizai cikin ƙasar Masar.”

10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu'ujizai a gaban Fir'auna. Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, bai kuwa saki Isra'ilawa daga ƙasarsa ba.

12

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna cikin ƙasar Masar,

2 wannan wata zai zama wata na farko a shekara a gare su.

3 A faɗa wa dukan taron Isra'ilawa cewa, “A rana ta goma ga watan nan, kowane namiji ya ɗauki ɗan rago ko ɗan akuya daga cikin garke domin iyalinsa, dabba ɗaya domin kowane gida.

4 Idan da wanda iyalinsa ba za su iya cinye dabba guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki dabba guda gwargwadon yawansu.

5 Tilas ne dabbar ta kasance lafiyayyiya ƙalau, bana ɗaya. Za ku kamo daga cikin tumakinku ko awaki.

6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato sa'ad da dukan taron jama'ar Isra'ila za su yanka ragunansu da maraice.

7 Sa'an nan ku ɗibi jinin, ku sa a dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar gidajen da za a ci naman dabbobin.

8 A daren nan za ku gasa naman, ku ci da abinci marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.

9 Kada ku ci shi ɗanye ko daffaffe da ruwa, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kayan cikin.

10 Kada ku bar kome ya kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.

11 Ga yadda za ku ci shi, da ɗamara a gindinku, da takalma a ƙafafunku, da sanda a hannunku, da gaggawa kuma za ku ci shi. Idin Ƙetarewa ne ga Ubangiji.

12 A daren nan zan ratsa ƙasar Masar, in bugi kowane ɗan fari na ƙasar, na mutum da na dabba. Zan hukunta gumakan Masar duka, gama ni ne Ubangiji.

13 Jinin da yake bisa gidajenku zai nuna inda kuke. Sa'ad da na ga jinin zan tsallake ku, ba kuma wani bala'in da zai same ku, ya hallaka ku, a lokacin da zan bugi ƙasar Masar.

14 Ranan nan za ta zama ranar tunawa a gare ku, za ku kiyaye ta, ranar idi ga Ubangiji. Dukan zamananku za ku kiyaye ta, idi ga Ubangiji har abada.

15 “Za ku yi kwana bakwai kuna cin abinci marar yisti. A rana ta fari za ku fitar da yisti daga cikin gidajenku, gama duk wanda ya ci abin da aka sa wa yisti tun daga rana ta fari har zuwa ta bakwai za a fitar da shi daga cikin Isra'ila.

16 A kan rana ta fari za ku yi tsattsarkan taro, haka kuma za ku yi a rana ta bakwai. A cikin waɗannan ranaku ba za a yi kowane aiki ba, sai na abin da kowa zai ci.

17 Za ku kiyaye idin abinci marar yisti, gama a wannan rana na fitar da rundunarku daga ƙasar Masar. Ku kiyaye wannan rana dukan zamananku. Wannan farilla ce ta har abada.

18 Za ku ci abinci marar yisti da maraice a kan rana ta goma sha huɗu ga wata na fari, har zuwa rana ta ashirin da ɗaya ga watan da maraice.

19 Amma kada a iske yisti a gidajenku har kwana bakwai, gama idan wani ya ci abin da aka sa wa yisti za a fitar da shi daga cikin taron jama'ar Isra'ila, ko shi baƙo ne ko kuwa haifaffen ƙasar.

20 Dukan abin da yake da yisti ba za ku ci shi ba, wato sai abinci marar yisti ne kaɗai za ku ci a dukan gidajenku.”

21 Musa ya kirayi dattawan Isra'ila duka, ya ce musu, “Gaggauta, ku zaɓa wa kanku ɗan tunkiya ko akuya bisa ga iyalanku, ku yanka domin Idin Ƙetarewa.

22 Ku ɗauki tuntun ezob, ku tsoma cikin jinin da yake a kasko, ku yarfa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada kowa ya fita daga gidansa sai da safe.

23 Gama Ubangiji zai ratsa don ya kashe Masarawa, sa'ad da ya ga jinin a bisa kan ƙofar, da dogaran ƙofa duka biyu sai ya wuce ƙofar, ba zai bar mai hallakarwa ya shiga gidanku, ya kashe ku ba.

24 Za ku kiyaye waɗannan ƙa'idodi, ku riƙe su farilla, ku da 'ya'yanku har abada.

25 Sa'ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku kamar yadda ya alkawarta, wajibi ne ku kiyaye wannan farilla.

26 Sa'ad da 'ya'yanku suka tambaye ku, ‘Ina ma'anar wannan farilla?’

27 Za ku ce, ‘Hadaya ce ta Idin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra'ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.”’ Sai jama'ar suka durƙusa suka yi sujada.

28 Isra'ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.

29 Da tsakar dare sai Ubangiji ya karkashe dukan 'ya'yan fari maza a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir'auna, wato magajinsa, har zuwa ɗan farin ɗan sarka da yake a kurkuku, har da dukan 'ya'yan fari maza na dabbobi.

30 Da dare Fir'auna ya tashi, shi da dukan fādawansa, da dukan Masarawa, suka yi kuka mai tsanani a Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.

31 Sai Fir'auna ya sa aka kirawo masa Musa da Haruna da daren, ya ce musu, “Tashi, ku da jama'arku, ku fita daga cikin jama'ata. Tafi, ku bauta wa Ubangiji kamar yadda kuka ce.

32 Kwashi garkunanku na tumaki da awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”

33 Masarawa suka iza mutanen su gaggauta, su fita ƙasar, gama suka ce, “Ƙarewa za mu yi idan ba ku tafi ba.”

34 Sai jama'ar suka ɗauki ƙullun da ba a sa masa yisti ba, da ƙorensu na aikin ƙullun, suka ƙunshe a mayafansu, suka saɓa a kafaɗunsu.

35 Isra'ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya faɗa musu, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.

36 Ubangiji ya sa jama'a su yi farin jini a wurin Masarawa, saboda haka Masarawa suka ba su abin da suka roƙa. Ta haka suka washe Masarawa.

37 Isra'ilawa mutum wajen zambar ɗari shida maza (600,000), banda iyalansu, suka kama tafiya daga Ramases zuwa Sukkot.

38 Babban taron tattarmuka kuma suka tafi tare da su, da garkunan tumaki da awaki, da na shanu tinjim.

39 Suka toya abinci marar yisti da ƙullun da suka fita da shi daga Masar, gama ba su sa yisti cikin ƙullun ba domin an iza ƙyeyarsu, ba su sami damar dakatawa ba, ba su kuwa shirya wa kansu guzuri ba.

40 Zaman da Isra'ilawa suka yi a Masar shekara ce arbaminya da talatin.

41 A ranar da shekara arbaminya da talatin ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan rundunar Ubangiji suka fita daga ƙasar Masar.

42 Daren nan da Ubangiji ya sa domin ya fito da Isra'ilawa daga ƙasar Masar, daren ne wanda wajibi ne Isra'ilwa su kiyaye domin su girmama Ubangiji dukan zamanansu.

43 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Wannan ita ce ƙa'idar Idin Ƙetarewa, baƙo ba zai ci ba.

44 Amma kowane bawa da aka saya da kuɗi ya iya ci, in dai an yi masa kaciya.

45 Amma da baƙo da wanda aka yi ijararsa ba zai ci shi ba.

46 A gidan da aka shirya, nan za a ci, kada a fitar da naman waje, kada kuma a karye ƙashinsa.

47 Dukan taron jama'ar Isra'ila za su kiyaye Idin Ƙetarewa.

48 Idan baƙon da yake zaune tare da ku yana so ya yi Idin Ƙetarewa ga Ubangiji tare da ku, to, sai a yi wa kowane namiji da yake a gidansa kaciya sa'an nan ya iya shiga idin, shi kuma ya zama ɗan ƙasa. Daɗai, marar kaciya ba zai ci ba.

49 Wannan ka'ida ta shafi ɗan ƙasa daidai da baƙon da yake baƙunci tsakaninku.”

50 Isra'ilawa suka yi na'am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.

51 A wannan rana ce Ubangiji ya fitar da Isra'ilawa runduna runduna daga ƙasar Masar.

13

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

2 “Keɓe mini 'ya'yan fari maza duka. Kowane ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa cikin Isra'ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”

3 Musa ya ce wa jama'a, “Ku kiyaye wannan rana da kuka fito daga Masar, daga gidan bauta, gama da hannu mai ƙarfi Ubangiji ya fitar da ku daga wurin. Daɗai, ba za ku ci abinci mai yisti ba.

4 A wannan rana kuka fita, wato a watan Abib.

5 Sai ku kiyaye wannan farilla a wannan wata sa'ad da Ubangiji ya kai ku ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, wadda ya rantse wa kakanninku zai ba ku, wato ƙasar da take ba da yalwar abinci.

6 Sai ku riƙa cin abinci marar yisti har kwana bakwai, amma a rana ta bakwai za ku yi idi ga Ubangiji.

7 Abinci marar yisti za a ci har kwana bakwai. Kada a ga wani da abinci mai yisti, ko kuma yisti ɗin kansa, a ko'ina a wurarenku.

8 A wannan rana kowa zai sanar wa ɗansa cewa abubuwan nan da muke yi, muna yi ne don tunawa da abin da Ubangiji ya yi mana sa'ad da ya fitar da mu daga Masar.

9 Zai zama matuni kamar alama a hannunku, da abin tunawa a goshinku, domin shari'ar Ubangiji ta zama a bakinku, gama da hannu mai ƙarfi Ubangiji ya fisshe ku daga Masar.

10 Sai ku kiyaye farillan nan kowace shekara a lokacinta.”

11 “Sa'ad da Ubangiji ya kai ku ƙasar Kan'aniyawa wadda zai ba ku kamar yadda ya rantse muku, ku da kakanninku,

12 sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Kowane ɗan farin dabbarku na Ubangiji ne.

13 Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. Idan kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Kowane ɗan farin 'ya'yanku, sai ku fanshe shi.

14 In wata rana 'ya'yanku suka tambaye ku cewa, ‘Ina ma'anar wannan?’ Sai ku ce musu, ‘Da iko Ubangiji ya fisshe mu daga Masar, daga gidan bauta.

15 Gama sa'ad da Fir'auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, Ubangiji kuwa ya kashe dukan 'ya'yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba gaba ɗaya. Domin haka muke yin hadaya ga Ubangiji da 'ya'yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma mukan fanshi dukan 'ya'yan farinmu, maza.’

16 Al'amarin nan kuwa zai zama matuni kamar alama a hannunku ko a goshinku, gama da iko Ubangiji ya fisshe mu daga Masar.”

17 Da Fir'auna ya bar jama'a su tafi, Allah bai bi da su ta hanyar ƙasar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ta fi kusa, gama Allah ya ce, “Don kada jama'a su sāke tunaninsu sa'ad da suka ga yaƙi, su koma Masar.”

18 Amma Allah ya kewaya da jama'a ta hanyar jeji, wajen Bahar Maliya. Isra'ilawa kuwa suka fita daga ƙasar Masar da shirin yaƙi.

19 Musa ya kuma ɗauki ƙasusuwan Yusufu, gama Yusufu ya riga ya rantsar da Isra'ilawa su kwashe ƙasusuwansa daga Masar sa'ad da Allah ya ziyarce su.

20 Sai suka ci gaba da tafiya daga Sukkot suka yi zango a Etam a gefen jejin.

21 Da rana Ubangiji yakan yi musu jagora da al'amudin girgije, da dare kuwa da al'amudin wuta, domin ya ba su haske domin su iya tafiya dare da rana.

22 Al'amudan nan biyu kuwa, na girgijen da na wutar, ba su daina yi wa jama'a jagora ba.

14

1 Ubangiji ya ce wa Musa,

2 “Faɗa wa Isra'ilawa su juya su yi zango a gaban Fi-hahirot tsakanin Migdol da bahar, a gaban Ba'alzefon. Sai ku yi zango gab da bahar.

3 Gama Fir'auna zai ce, ‘Aha, Isra'ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta cinye su.’

4 Zan taurare zuciyar Fir'auna, zai kuwa bi ku, ni Ubangiji zan nuna ɗaukakata a bisa Fir'auna da dukan rundunansa. Masarawa kuwa za su sani ni ne Ubangiji.” Haka kuwa Isra'ilawa suka yi.

5 Da aka faɗa wa Sarkin Masar jama'a sun gudu, sai shi da fādawansa suka sāke tunaninsu game da jama'ar, suka ce, “Me muka yi ke nan, da muka bar Isra'ilawa su fita daga cikin bautarmu?”

6 Ya kuwa shirya karusarsa, ya ɗauki rundunarsa tare da shi.

7 Ya kuma ɗauki zaɓaɓɓun karusai ɗari shida da sauran karusan Masar duka waɗanda shugabanni suke bi da su.

8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, Sarkin Masar, sai ya bi Isra'ilawa sa'ad da suka fita gabagaɗi.

9 Masarawa kuwa, da dukan dawakan Fir'auna, da karusai, da mahayan dawakansa, da askarawansa, suka bi su, suka ci musu a inda suka yi zango a bakin bahar, kusa da Fi-hahirot wanda ya fuskanci Ba'alzefon.

10 Da Fir'auna ya matso, Isra'ilawa kuwa suka ɗaga idanunsu suka ga Masarawa tafe, sun tasar musu, sai suka firgita ƙwarai, suka yi kuka ga Ubangiji.

11 Suka ce wa Musa, “Donin ba makabarta a Masar, shi ya sa ka fito da mu, mu mutu a jeji? Me ke nan ka yi mana da ka fito da mu daga Masar?

12 Ashe, ba abin da muka faɗa maka tun a Masar ke nan ba cewa, ‘Ka rabu da mu, mu bauta wa Masarawa’? Gama gwamma mu bauta wa Masarawa da mu mutu a jeji.”

13 Sai Musa ya ce wa jama'a, “Kada ku tsorata, ku tsaya cik, ku ga ceton Ubangiji, wanda zai yi muku yau, gama Masarawan nan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba faufau.

14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, sai dai ku tsaya kurum!”

15 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Me ya sa kake yi mini kuka? Faɗa wa Isra'ilawa su ci gaba.

16 Ɗaga sandanka, ka miƙa hannunka a bisa bahar, ka raba shi, domin Isra'ilawa su taka busasshiyar ƙasa cikin bahar, su haye.

17 Ni kuwa zan taurare zukatan Masarawa domin su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir'auna da rundunansa, da karusansa, da mahayan dawakansa.

18 Masarawa kuwa za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na sami nasara bisa kan Fir'auna, da karusansa, da mahayan dawakansa.”

19 Mala'ikan Allah kuwa wanda yake tafiya a gaban rundunar Isra'ila ya tashi ya koma bayansu, haka kuma al'amudin girgijen ya tashi daga gabansu ya tsaya a bayansu.

20 Ya shiga tsakanin sansanin Masarawa da zangon Isra'ilawa. Girgije mai duhu na tsakaninsu, amma ya haskaka wajen Isra'ilawa har gari ya waye, ba wanda ya kusaci wani.

21 Da Musa ya miƙa hannunsa bisa bahar, sai Ubangiji ya sa iskar gabas mai ƙarfi ta tsaga bahar, ta tura ta baya, ta yi ta hurawa dukan dare har bahar ta bushe, ruwan kuwa ya dāre.

22 Isra'ilawa kuwa suka bi ta tsakiyar bahar, a busasshiyar ƙasa. Ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.

23 Masarawa kuwa suka bi su har tsakiyar bahar, da dawakan Fir'auna duka, da karusansa, da mahayan dawakansa.

24 Da asubahin fāri, Ubangiji, daga cikin al'amudin wuta da na girgije, ya duba rundunar Masarawa, ya gigitar da su.

25 Kafafun karusansu suka fara kwaɓewa, da ƙyar ake jansu. Daga nan Masarawa suka ce, “Mu guje wa Isra'ilawa, gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masarawa.”

26 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa bahar domin ruwa ya koma bisa kan Masarawa, da bisa karusansu, da mahayan dawakansu.”

27 Gari na wayewa sai Musa ya miƙa hannunsa bisa bahar, ruwan kuwa ya koma kamar yadda yake a dā. Da Masarawa suka yi ƙoƙarin tserewa, sai ruwan ya rufe su. Ubangiji kuwa ya hallaka su a tsakiyar bahar.

28 Ruwan ya komo ya rufe dukan karusai, da mahayan dawakai, da dukan rundunar Fir'auna waɗanda suka bi ta cikin bahar, ba ko ɗaya da ya ragu.

29 Amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busasshiyar ƙasa a tsakiyar bahar, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.

30 A wannan rana, Ubangiji ya ceci Isra'ilawa daga hannun Masarawa. Isra'ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin bahar.

31 Isra'ilawa suka ga gawurtaccen aikin da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa. Isra'ilawa kuwa suka ji tsoron Ubangiji, suka gaskata Ubangiji da bawansa Musa.

15

1 Musa da jama'ar Isra'ila suka raira wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara, Dawakai da mahayansu ya jefar cikin bahar.

2 Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, Shi ne wanda ya cece ni. Wannan ne Allahna, zan yabe shi, Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.

3 Ubangiji mayaƙi ne, Yahweh ne sunansa.

4 “Karusan Fir'auna da rundunarsa, ya jefar cikin bahar, Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.

5 Rigyawa ta rufe su, Suka nutse cikin zurfi kamar dutse.

6 Ya Ubangiji dantsen damanka, mai iko ne, Ya Ubangiji, dantsen damanka ya ragargaza magabta.

7 Cikin girman ɗaukakarka, ka kā da maƙiyanka, ka aika da hasalarka, Ka cinye su kamar ciyawa.

8 Da hucin numfashin hancinka ruwa ya tattaru, Rigyawa ta tsaya kamar tudu, Zurfafan ruwa suka daskare a tsakiyar bahar.

9 Magabcin ya ce, ‘Zan bi, in kama su, in raba ganima, Muradina a kansu zai biya, zan zare takobina, hannuna zai hallaka su.’

10 Ka hura iskarka, bahar ta rufe su, suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.

11 “Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.

12 Ka miƙa dantsen damanka, ƙasa ta haɗiye su.

13 Da tabbatacciyar ƙaunarka, ka bi da jama'arka da ka fansa, Ka bi da su da ƙarfinka zuwa tsattsarkan mazauninka.

14 Al'ummai suka ji suka yi rawar jiki, Tsoro ya kama mazaunan Filistiya.

15 Sarakunan Edom suka tsorata, Shugabannin Mowab suna rawar jiki, Dukan mazaunan Kan'ana sun narke.

16 Tsoro da razana sun aukar musu, Ta wurin ikonka suka tsaya cik kamar dutse, Har jama'arka, ya Ubangiji, suka haye, I, jama'arka, ya Ubangiji, suka haye,

17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka, Wurin, ya Ubangiji, da ka maishe shi tsattsarkan mazauninka, Tsattsarkan wurinka, ya Ubangiji, wanda ka kafa da ikonka.

18 Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”

19 Gama sa'ad da dawakan Fir'auna, da karusansa, da mahayan dawakansa suka shiga bahar, Ubangiji ya komar da ruwan bahar a bisansu, amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busassiyar ƙasa ta tsakiyar bahar.

20 Sai Maryamu, annabiya, 'yar'uwar Haruna, ta ɗauki kuru cikin hannunta. Mata duka suka fita, suka bi ta da kuwaru suna ta rawa.

21 Maryamu tana raira musu waƙa tana cewa, “Raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara, Doki da mahayinsa, ya jefar cikin bahar.”

22 Musa kuwa ya bi da Isra'ilawa daga Bahar Maliya, suka shiga jejin Sur. Suka yi tafiya kwana uku cikin jejin, ba su sami ruwa ba.

23 Sa'ad da suka zo Mara, sun kasa shan ruwan Mara saboda ɗacinsa, don haka aka sa masa suna Mara.

24 Sai mutanen suka yi wa Musa gunaguni suna cewa, “Me za mu sha?”

25 Musa ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sa'an nan Musa ya karyi itacen, ya jefa cikin ruwa, ruwan kuwa ya zama mai daɗi. A nan ne Ubangiji ya kafa musu dokoki da ka'idodi, a nan ne kuma ya gwada su.

26 Ya ce, “In za ku himmantu ku yi biyayya da ni, ni da nake Ubangiji Allahnku, sai ku aikata abin da yake daidai a gare ni, ku kuma kiyaye umarnaina da dokokina duka, to, ba zan sa muku cuce-cuce irin waɗanda na sa wa Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”

27 Daga nan suka je Elim inda akwai maɓuɓɓugan ruwa goma sha biyu, da itatuwan giginya saba'in. A nan suka yi zango a bakin ruwa.

16

1 Taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga Elim suka shiga jejin Sin wanda yake tsakanin Elim da Sina'i, a rana ta goma sha biyar ga watan biyu bayan fitowarsu daga ƙasar Masar.

2 Sai dukan taron jama'ar Isra'ilawa suka yi wa Musa da Haruna gunaguni cikin jejin, suka ce musu,

3 “Da ma mun mutu ta ikon Ubangiji a ƙasar Masar lokacin da muka zauna kusa da tukwanen nama, muka ci abinci muka ƙoshi. Ga shi, kun fito da mu zuwa cikin jeji don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”

4 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ga shi, zan sauko muku da abinci daga sama. A kowace rana jama'a za su fita su tattara abin da zai ishe su a yini, da haka zan gwada su, ko za su kiyaye maganata, ko babu.

5 A kan rana ta shida, sai su ninka abin da suka saba tattarawa na kowace rana, su shirya shi.”

6 Musa da Haruna kuwa suka ce wa Isra'ilawa, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fisshe ku daga ƙasar Masar.

7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, gama ya ji gunagunin da kuka yi a kansa, gama wane, mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”

8 Musa ya kuma ce, “Da yamma Ubangiji zai ba ku nama ku ci, da safe kuwa zai ƙosar da ku da abinci, gama Ubangiji ya riga ya ji irin gunagunin da kuka yi a kansa. Ai, gunagunin ba a kanmu yake ba, wane mu? A kan Ubangiji ne kuka yi.”

9 Musa ya ce wa Haruna, “Faɗa wa taron jama'ar Isra'ila, su matso nan a gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninsu.”

10 Sa'ad da Haruna yake magana da taron jama'ar, suka duba wajen jeji, sai ga ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a cikin girgije.

11 Ubangiji kuwa ya yi magana da Musa ya ce,

12 “Na ji gunagunin Isra'ilawa, amma ka faɗa musu cewa, ‘A tsakanin faɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe za ku kuma ƙoshi da abinci. Sa'an nan za ku sani, ni Ubangiji Allahnku ne.”’

13 Da maraice makware suka zo suka rufe zangon, da safe kuma raɓa ta kewaye zangon.

14 Sa'ad da raɓar ta kaɗe, sai ga wani abu tsaki-tsaki mai laushi, fari, kamar hazo a ƙasa.

15 Sa'ad da Isra'ilawa suka gan shi, suka ce wa junansu, “Manna,” wato “Mece ce wannan?” Gama ba su san irinta ba. Musa kuwa ya ce musu, “Wannan ita ce abincin da Ubangiji ya ba ku, ku ci.

16 Abin da Ubangiji ya umarta ke nan, kowannenku ya tattara wadda ta ishe shi ci, kowa ya sami mudu daidai bisa ga yawan mutanen da yake cikin kowace alfarwa.”

17 Isra'ilawa suka yi haka nan, suka tattara, waɗansu suka zarce, waɗansu kuma ba su kai ba.

18 Amma da aka auna da mudu, ta waɗanda suka zarce ba ta yi saura ba, ta waɗanda ba su kai ba, ba ta gaza ba. Kowane mutum ya tattara daidai cinsa.

19 Musa ya ce musu, “Kada wani ya ci, ya bar saura har safiya.”

20 Amma waɗansu ba su kasa kunne ga Musa ba, suka bar saura, har ta kwana, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.

21 Kowace safiya sukan tattara ta, kowa gwargwadon cinsa, amma da rana ta yi zafi sai manna ɗin ta narke.

22 A kan rana ta shida suka tattara biyu ɗin abin da suka saba, kowane mutum mudu biyu biyu. Sai shugabannin taron suka zo suka faɗa wa Musa.

23 Shi kuwa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarta, ‘Gobe ranar hutawa ce ta saduda, Asabar ce, tsattsarka ga Ubangiji. Ku toya abin da za ku toya, ku kuma dafa abin da za ku dafa. Abin da kuka ci kuka rage, ku ajiye don gobe.”’

24 Suka ajiye har gobe kamar yadda Musa ya umarta, amma ba ta yi ɗoyi ba, ba ta kuwa yi tsutsotsi ba.

25 Sai Musa ya ce, “Ita za ku ci yau, gama yau Asabar ce ga Ubangiji. Yau ba za ku same ta a saura ba.

26 Kwana shida za ku tattara ta, amma a rana ta bakwai wadda take asabar, ba za a iske kome ba.”

27 Amma a rana ta bakwai ɗin waɗansu mutane suka tafi don su tattara, ba su kuwa sami kome ba.

28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi kiyaye dokokina da umarnaina?

29 Lura fa, Ubangiji ne ya ba ku ranar Asabar, domin haka a rana ta shida yakan ba ku abinci na kwana biyu. Kowanne ya yi zamansa a inda yake. Kada kowa ya bar inda yake a rana ta bakwai ɗin.”

30 Sai jama'a suka huta a rana ta bakwai.

31 Isra'ilawa kuwa suka sa wa wannan abinci suna, Manna. Manna wata irin tsaba ce kamar farin riɗi. Ɗanɗanarta kuwa kamar waina ce da aka yi da zuma.

32 Sai Musa ya ce, “Ubangiji ya umarta a cika mudu da ita, a adana ta dukan zamananku domin kowane zamani a ga irin abincin da ya ciyar da ku cikin jeji lokacin da ya fito da ku daga ƙasar Masar.”

33 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ɗauki tukunya, ka zuba mudu guda na manna a ciki, ka ajiye a gaban Ubangiji, a adana har dukan zamananku.”

34 Kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa, haka Haruna ya ajiye ta a gaban akwatin alkawari domin kiyayewa.

35 Shekara arba'in Isra'ilawa suka yi suna cin manna, har suka kai ƙasar da take da mutane, suka ci manna, har zuwa kan iyakar ƙasar Kan'ana.

36 Mudu ɗaya humushin garwa ɗaya ta gari.

17

1 Dukan taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga jejin Sin, suna tafiya daga zango zuwa zango bisa ga umarnin Ubangiji. Suka yi zango a Refidim, amma ba ruwan da jama'a za su sha.

2 Domin haka jama'a suka zargi Musa suka ce, “Ba mu ruwa, mu sha.” Musa ya amsa musu ya ce, “Don me kuke zargina? Don me kuke gwada Ubangiji?”

3 Amma jama'a suna fama da ƙishirwa, suka yi wa Musa gunaguni. Suka ce, “Don me ka fito da mu daga Masar? Ashe, domin ka kashe mu ne, da mu, da 'ya'yanmu, da dabbobinmu da ƙishi?”

4 Sai Musa ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Me zan yi wa jama'an nan? Ga shi, saura kaɗan su jajjefe ni da duwatsu.”

5 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ɗauki waɗansu dattawa daga cikin jama'ar Isra'ila, ka wuce a gaban jama'ar. Ka kuma ɗauki sandanka wanda ka bugi Nilu da shi, ka tafi.

6 Zan tsaya a dutsen Horeb can a gabanka. Za ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito domin jama'a su sha.” Musa kuma ya yi haka nan a gaban dattawan Isra'ila.

7 Sai aka sa wa wurin suna, “Masaha” da “Meriba”, saboda Isra'ilawa suka yi husuma, suka kuma jarraba Ubangiji suna cewa, “Ubangiji yana tare da mu, ko babu?”

8 Amalekawa suka zo su yi yaƙi da Isra'ilawa a Refidim.

9 Sai Musa ya ce wa Joshuwa, “Zaɓo mana mutane, ka fita ka yi yaƙi da Amalekawa gobe. Zan tsaya a bisa dutsen da sandan mu'ujiza a hannuna.”

10 Joshuwa kuwa ya yi yadda Musa ya faɗa masa, ya fita ya yi yaƙi da Amalekawa. Musa, da Haruna, da Hur kuma suka hau kan dutsen.

11 Muddin hannun Musa na miƙe, sai Isra'ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.

12 Sa'ad da hannuwan Musa suka gaji, Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka ajiye wa Musa, ya zauna a kai, su kuwa suka tsaya a gefen damansa da hagunsa suna tallabe da hannunsa sama, suka tallabe su har faɗuwar rana.

13 Joshuwa kuwa ya ragargaza rundunar Amalekawa da takobi.

14 Ubangiji ya ce wa Musa, “Rubuta wannan a littafi domin a tuna da shi, ka kuma faɗa wa Joshuwa zan shafe Amalekawa ɗungum.”

15 Sai Musa ya gina bagade ya sa masa suna, Yahweh Nissi, wato Ubangiji ne tutarmu.

16 Ya ce, “Ubangiji ya tabbata zai yaƙi Amalekawa har abada.”

18

1 Yetro, firist na Madayana, surukin Musa, ya ji dukan abin da Allah ya yi wa jama'arsa, wato Musa da Isra'ilawa, yadda Ubangiji ya fito da su daga Masar.

2 Ya kawo Ziffora matar Musa, wadda Musa ya aika da ita gida.

3 Yetro kuma ya kawo 'ya'yanta biyu maza, Gershom da Eliyezer tare da ita. Gama Musa ya ce, “Ni baƙo ne a baƙuwar ƙasa.” Saboda haka ne ya raɗa wa ɗaya daga cikin 'ya'yansa, suna, Gershom.

4 Ya kuma ce, “Allah na ubanan shi ne ya taimake ni, ya cece ni daga takobin Fir'auna,” saboda haka ya raɗa wa ɗayan, suna, Eliyezer.

5 Sai Yetro ya kawo wa Musa 'ya'yansa maza da matarsa a cikin jeji inda suka yi zango kusa da dutsen Allah.

6 Aka faɗa wa Musa, “Ga surukinka, Yetro, yana zuwa wurinka da matarka da 'ya'yanta biyu tare da ita.”

7 Musa kuwa ya fita ya marabce shi, ya sunkuya, ya sumbace shi. Suka gaisa, suka tambayi lafiyar juna, sa'an nan suka shiga alfarwa.

8 Sai Musa ya faɗa wa surukinsa dukan abin da Ubangiji ya yi da Fir'auna da Masarawa saboda Isra'ilawa, ya kuma faɗa masa dukan wahalar da suka sha a kan hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.

9 Yetro kuwa ya yi murna saboda alherin da Ubangiji ya yi wa Isra'ilawa da yadda ya cece su daga hannun Masarawa.

10 Yetro kuma ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da Fir'auna, wanda kuma ya ceci jama'arsa daga bautar Masarawa.

11 Yanzu na sani Ubangiji yake gāba da sauran alloli duka, gama ya ceci Isra'ilawa daga tsanantawar da Masarawa suka yi musu.”

12 Yetro, surukin Musa kuwa, ya miƙa hadaya ta ƙonawa da sadaka ga Allah. Sai Haruna ya zo tare da dattawan Isra'ila duka don su ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.

13 Kashegari da Musa ya zauna garin yi wa jama'ar shari'a, mutane suka kekkewaye shi tun dage safiya har zuwa yamma.

14 Da surukin Musa ya ga yadda Musa yake fama da jama'a, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa jama'a? Don me kake zaune kai kaɗai, mutane kuwa na tsattsaye kewaye da kai, tun daga safe har zuwa maraice?”

15 Sai Musa ya ce wa surukinsa, “Mutane suna zuwa wurina ne domin su san faɗar Allah.

16 A sa'ad da suke da wata matsala sukan zo wurina, ni kuwa nakan daidaita tsakanin mutum da maƙwabcinsa, nakan kuma koya musu dokokin Allah da umarnansa.”

17 Amma surukin Musa ya ce, “Abin nan da kake yi ba daidai ba ne.

18 Kai da jama'an nan da suke tare da kai za ku rafke, saboda abin da kake yi ya fi ƙarfinka, kai kaɗai ba za ka iya ba.

19 Yanzu sai ka saurari maganata, zan ba ka shawara, Allah kuwa ya kasance tare da kai. Za ka wakilci jama'a a gaban Allah, ka kai matsalolinsu gare shi.

20 Ka koya musu dokokin da umarnan, ka nuna musu hanyar da ya kamata su yi.

21 Ka kuma zaɓa daga cikin jama'a isassun mutane, masu tsoron Allah, amintattu, waɗanda suke ƙyamar cin hanci. Ka naɗa su shugabannin jama'a na dubu dubu da na ɗari ɗari, da na hamsin hamsin, da na goma goma.

22 Za su yi wa mutane shari'a koyaushe, amma kowace babbar matsala sai su kawo maka, ƙaramar matsala kuwa su yanke da kansu. Da haka za su ɗauki nauyin jama'a tare da kai don ya yi maka sauƙi.

23 In ka bi wannan shawara, in kuma Allah ya umarce ka da yin haka, za ka iya ɗaukar nawayar jama'ar. Mutane duka kuwa za su yi zamansu lafiya.”

24 Musa kuwa ya saurari maganar surukinsa, ya yi abin da ya ce duka.

25 Sai Musa ya zaɓi isassun mutane daga cikin Isra'ilawa ya naɗa su shugabannin jama'a na dubu dubu, da na ɗari ɗari, da na hamsin hamsin, da na goma goma.

26 Suka yi ta yi wa jama'a duka shari'a kullayaumin, amma matsaloli masu wuya sukan kawo wa Musa, ƙananan kuwa sukan yanke da kansu.

27 Sa'an nan Musa ya sallami surukinsa, ya koma garinsu.

19

1 Isra'ilawa sun kai jejin Sina'i a farkon watan uku bayan fitowarsu daga ƙasar Masar.

2 Da suka tashi daga Refidim, suka shiga jejin Sina'i, sai suka yi zango gaban dutsen.

3 Musa kuwa ya hau bisa dutsen don ya sadu da Allah. Ubangiji ya kira shi daga kan dutsen, ya ce, “Abin da za ka faɗa wa gidan Yakubu, wato Isra'ilawa ke nan,

4 ‘Kun dai ga abin da na yi da Masarawa, da yadda na ɗauke ku kamar yadda gaggafa take ɗaukar 'yan tsakinta, na kawo ku gare ni.

5 Yanzu fa, in za ku yi biyayya da ni, ku kuma kiyaye maganata, za ku zama mutanena. Dukan duniya tawa ce, amma ku za ku zama zaɓaɓɓiyar jama'ata,

6 za ku zama daular firistoci da al'umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne zantuttukan da za ka faɗa wa Isra'ilawa.”

7 Sa'an nan Musa ya je ya kira taron dattawan jama'a, ya bayyana musu dukan zantuttukan da Ubangiji ya umarce shi.

8 Dukan jama'a kuwa suka amsa masa baki ɗaya, suka ce, “Dukan abin da Ubangiji ya faɗa za mu aikata.” Musa kuwa ya mayar wa Ubangiji da amsar da jama'ar suka bayar.

9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ga shi, ni da kaina, ina zuwa a gare ka cikin duhun girgije, domin jama'a su ji sa'ad da nake magana da kai, domin su amince da kai tutur.” Musa kuwa ya mayar wa Ubangiji da amsar da jama'ar suka bayar.

10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je ka wurin jama'a ka tsarkake su yau da kuma gobe, su kuma wanke tufafinsu.

11 Su shirya saboda rana ta uku, gama a kan rana ta uku zan sauko a bisa dutsen Sina'i a gabansu duka.

12 Sai ka yi wa jama'a iyaka kewaye da dutsen, ka faɗa musu cewa, ‘Ku yi hankali kada ku hau dutsen ko ku taɓa shi. Duk wanda ya taɓa dutsen za a kashe shi,

13 za a jajjefe shi da duwatsu ko a harbe shi da kibiya, kada kowa ya taɓa dutsen da hannu. Wannan kuwa ya shafi mutane duk da dabbobi, tilas ne a kashe su.’ Sa'ad da aka busa ƙahon rago, sai mutane su taru a gindin dutsen.”

14 Da Musa ya gangaro daga dutsen zuwa wurin mutane, ya tsarkake su. Su kuwa suka wanke tufafinsu.

15 Sai Musa ya ce musu, “Ku shirya saboda rana ta uku, kada ku kusaci mace.”

16 A safiyar rana ta uku aka yi tsawa, da walƙiyoyi, da girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama'ar da suke cikin zango suka yi rawar jiki.

17 Musa kuwa ya fito da jama'a daga zango ya shugabance su, su sadu da Allah, suka tsattsaya a gindin dutsen.

18 Ga shi, hayaƙi ya tunnuƙe dutsen Sina'i duka, saboda Ubangiji ya sauko a bisa dutsen da wuta. Hayaƙi kuwa ya tunnuƙe, ya yi sama kamar na wurin narka ma'adinai, dutsen duka ya girgiza ƙwarai.

19 Da busar ƙaho ta ƙara tsananta, sai Musa ya yi magana, Ubangiji kuwa ya amsa masa da tsawa.

20 Ubangiji ya sauko bisa dutsen Sina'i bisa ƙwanƙolin dutsen. Ya kirawo Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen, Musa kuwa ya hau.

21 Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, ka faɗakar da jama'ar, don kada su ƙetare kan iyakar, su zo garin a kalli Ubangiji, da yawa daga cikinsu kuwa su mutu.

22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji, sai su tsarkake kansu, don kada in hukunta su.”

23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su iya hawan dutsen Sina'i ba, gama kai da kanka ka umarce mu cewa, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen, ku tsarkake shi.’ ”

24 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Sauka, ka hau tare da Haruna. Amma kada ka bar firistoci da jama'a su ƙetare kan iyakar su hau zuwa wurina, don kada in hukunta su.”

25 Sai Musa ya sauka wurin jama'a ya faɗa musu.

20

1 Allah ya faɗi dukan waɗannan zantuttuka, ya ce,

2 “Ni ne Ubangiji Allahnka wanda ya fisshe ka daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.

3 “Kada ka kasance da waɗansu alloli sai ni.

4 “Kada ka yi wa kanka wani gunki ko kuwa wata siffa ta wani abu a sama a bisa, ko a duniya a ƙasa, ko kuma a ruwa a ƙarƙarshin ƙasa.

5 Kada ka rusuna musu, kada kuwa ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, mai kishi ne. Nakan hukunta 'ya'ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina.

6 Amma nakan gwada madawwamiyar ƙaunata ga dubban tsararrakin da suke ƙaunata, masu kiyaye dokokina.

7 “Kada ka kama sunan Ubangiji Allahnka a banza, gama zan hukunta duk wanda ya kama sunana a banza.

8 “Tuna da rana Asabar, ka kiyaye ta da tsarki.

9 Za ku yi dukan ayyukanku cikin kwana shida,

10 amma rana ta bakwai keɓaɓɓiya ce ga Ubangiji Allahnka. A ranar ba za ka yi kowane irin aiki ba, ko kai, ko 'ya'yanka, ko barorinka, ko dabbobinka, ko kuwa baƙon da yake zaune tare da ku.

11 Gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama, da duniya, da teku, da dukan abin da yake cikinsu, amma a rana ta bakwai ya huta. Soboda haka Ubangiji ya keɓe ranar Asabar, ya tsarkake ta.

12 “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.

13 “Kada ka yi kisankai.

14 “Kada ka yi zina.

15 “Kada ka yi sata.

16 “Kada ka ɓāta sunan maƙwabcinka.

17 “Kada ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka. Kada kuma ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka, ko barorinsa mata da maza, ko sansa, ko jakinsa, ko kowane abin da yake nasa.”

18 Da jama'a suka ji tsawar hadiri, da ƙarar ƙaho mai tsanani suka kuma ga walƙiya, da dutsen yana hayaƙi, sai suka ji tsoro suka yi rawar jiki, suka tsaya nesa.

19 Suka ce wa Musa, “Kai, ka yi magana da mu, za mu ji, amma kada Allah ya yi magana da mu don kada mu mutu.”

20 Musa kuwa ya ce wa jama'a, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo ne don ya jarraba ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”

21 Sai jama'a suka tsattsaya nesa, Musa kuwa ya matsa kusa da girgije mai duhu inda Allah yake.

22 Ubangiji ya ce wa Musa, “Haka za ka faɗa wa Isra'ilawa, ‘Ku da kanku kun ji na yi magana da ku daga sama.

23 Banda ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa da na zinariya.

24 Za ku gina mini bagade na ƙasa. A kansa za ku miƙa mini hadayu na ƙonawa da na salama, da tumakinku da shanunku. A duk inda na sa a tuna da sunana zan zo wurinku in sa muku albarka.

25 Idan kuwa za ku gina mini bagade na dutse, kada ku gina mini da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama idan guduma ta taɓa duwatsun sun haramtu.

26 Kada ku yi wa bagadena matakai domin kada tsiraicinku ya bayyana a bisansu sa'ad da kuke hawansu.”’

21

1 “Waɗannan su ne ka'idodin da za a ba Isra'ilawa.

2 Idan ka sayi bawa Ba'ibrane, zai yi bauta shekara shida, a shekara ta bakwai kuwa, a 'yantar da shi kyauta.

3 Idan yana shi kaɗai aka saye shi, sai ya fita shi kaɗai, idan kuwa yana da aure sa'ad da aka saye shi, sai matarsa ta fita tare da shi.

4 Idan kuwa ubangijinsa ne ya auro masa matar, ta kuwa haifa masa 'ya'ya mata ko maza, to, matar da 'ya'yanta za su zama na ubangijinsa, amma shi kaɗai zai fita.

5 Amma idan hakika bawa ya hurta ya ce, yana ƙaunar ubangijinsa, da matarsa, da 'ya'yansa, ba ya son 'yancin,

6 to, sai ubangijinsa ya kawo shi a gaban Allah a ƙofa ko a madogarar ƙofa, sa'an nan ubangijinsa ya huda kunnensa da abin hudawa. Zai bauta wa ubangijinsa muddin ransa.

7 “Idan mutum ya sayar da 'yarsa kamar baiwa, ba za a 'yanta ta kamar bawa ba.

8 Idan ba ta gamshi maigidanta wanda ya maishe ta kamar ɗaya daga cikin matansa ba, sai ya yarda a fanshe ta. Amma ba shi da iko ya sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba.

9 Idan ya ba da ita ga ɗansa ne sai ya maishe ta kamar 'yarsa.

10 In mutumin ya auri wata kuma, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba.

11 Idan kuwa bai cika mata wajiban nan uku ba, sai ta fita abinta, ba zai karɓi kome ba.”

12 “Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle, shi ma sai a kashe shi.

13 In ba da nufi ya kashe shi ba, amma tsautsayi ne, to, sai mutumin ya tsere zuwa inda zan nuna muku.

14 Amma idan mutum ya fāɗa wa ɗan'uwansa da niyyar kisankai, lalle, sai a kashe shi ko da ya gudu zuwa bagadena.

15 “Wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lalle, kashe shi za a yi.

16 “Wanda ya saci mutum, ya sayar, ko kuwa a iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.

17 “Wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lalle kashe shi za a yi.

18 “Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,

19 idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓāta masa, ya kuma lura da shi har ya warke sarai.

20 “In mutum ya dūki bawansa ko baiwarsa da sanda har ya mutu a hannunsa, lalle ne a hukunta shi.

21 Amma idan bawan ya rayu kwana ɗaya ko biyu, to, kada a hukunta shi, gama bawan dukiyarsa ne.

22 “Idan mutum biyu na faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka zai biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.

23 Amma in wani lahani ya auku, to, sai a hukunta rai a maimakon rai,

24 ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa,

25 ƙuna a maimakon ƙuna, rauni a maimakon rauni, ƙujewa a maimakon ƙujewa.

26 “Idan mutum ya bugi bawansa ko baiwarsa a ido har idon ya lalace, sai ya 'yanta bawan ko baiwar a maimakon idon.

27 Idan ya fangare haƙorin bawansa ko na baiwarsa, sai ya 'yanta bawan ko baiwar a maimakon haƙorin.”

28 “Idan sa ya kashe ko mace ko namiji, to, lalle ne a jajjefi san da duwatsu, kada kuma a ci namansa, mai san kuwa zai kuɓuta.

29 Amma idan san ya saba fafarar mutane, aka kuma yi wa mai shi kashedi, amma bai kula ba, har san ya kashe ko mace ko namiji, sai a jajjefi san duk da mai shi.

30 Idan an yanka masa diyya, sai ya biya iyakar abin da aka yanka masa don ya fanshi ransa.

31 Haka kuma za a yi idan san ya kashe ɗan wani ko 'yar wani.

32 Idan san ya kashe bawa ko baiwa, sai mai san ya biya wa ubangijin bawan, ko baiwar, shekel talatin a kuma jajjefi san.

33 “Idan mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai rufe ba, in sa ko jaki ya fāɗa ciki,

34 mai ramin zai biya mai san ko mai jakin, mushen ya zama nasa.

35 Idan san wani ya yi wa na wani rauni har ya mutu, sai ya sayar da san da yake da rai a raba kuɗin. Haka kuma za su raba mushen.

36 Amma idan dā ma an sani san mafaɗaci ne, mai san kuwa bai kula da shi ba, sai ya biya, wato ya ba da sa a maimakon mushen. Mushen kuwa zai zama nasa.”

22

1 “Idan mutum ya saci sa ko tunkiya, ya yanka ko ya sayar, zai biya shanu biyar a maimakon sa, tumaki huɗu maimakon tunkiya.

2 In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga ya yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa ga kowa ba,

3 sai dai ko in gari ya riga ya waye. Dole ɓarawon ya yi cikakkiyar ramuwa, in kuwa ba shi da abin biya, a sayar da shi a biya abin da ya satar.

4 In kuwa aka iske dabbar da ya satar a hannunsa da rai, ko sa, ko jaki, ko tunkiya, lalle ne ya biya riɓi biyu.

5 “In mutum ya kai dabbarsa kiwo a saura ko a garka, ya bar ta, ta yi ɓarna a gonar wani, ko a gonar inabin wani, sai a sa mai dabbar ya biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.

6 “Idan wuta ta tashi a jeji ta ƙone tarin hatsi, ko hatsin da yake tsaye, ko gona, wanda ya sa wutar lalle ya biya cikakkiyar ramuwa.

7 “Idan mutum ya ba amininsa amanar kuɗi, ko amanar kadara, amma aka sace, in aka sami ɓarawon, a sa shi ya biya ninki biyu.

8 In kuwa ba a sami ɓarawon ba, sai a kawo maigidan a gaban Allah don a tabbatar babu hannunsa a cikin dukiyar amininsa.

9 “A kowane laifi na cin amana, ko sa ne, ko jaki, ko tunkiya, ko tufa, ko kowane ɓataccen abu, da abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin nan a gaban Allah. Wanda Allah ya ce shi ne da laifi, sai ya biya wa ɗayan ninki biyu.

10 “In mutum ya bai wa amininsa amanar jaki, ko sa, ko tunkiya ko kowace irin dabba, amma dabbar ta mutu, ko ta yi rauni, ko ta ɓace, in ba shaida,

11 rantsuwa ce za ta raba tsakaninsu don a tabbatar babu hannunsa a dukiyar amininsa, mai dukiyar kuwa ya yarda da rantsuwar. Wanda aka bai wa amanar ba zai biya ba.

12 In dai sacewa aka yi, sai ya biya mai shi.

13 Idan kuwa naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shida. Ba zai yi ramuwar abin da naman jeji ya kashe ba.

14 “Idan mutum ya yi aron wani abu a wurin maƙwabcinsa, in abin ya yi rauni ko ya mutu, sa'ad da mai abin ba ya nan, lalle ne ya yi ramuwa.

15 Amma in mai abin yana wurin, wanda ya yi aro ba zai yi ramuwa ba. Idan kuwa jingina ce aka yi, kuɗin jinginar ne ramuwar.”

16 “Idan mutum ya rarrashi budurwa wadda ba a tashinta, har ya ɓata ta, sai ya biya sadaki, ya aure ta.

17 Amma idan mahaifinta bai yarda ya ba da ita gare shi ba, sai mutumin ya ba da sadaki daidai da abin da akan biya domin budurwa.

18 “Kada a bar mace mai sihiri ta rayu.

19 “Duk wanda ya kwana da dabba, lalle kashe shi za a yi.

20 “Wanda ya miƙa hadaya ga wani allah, ba ga Ubangiji ba, sai a hallaka shi ɗungum.

21 “Kada ku wulakanta baƙo ko ku zalunce shi, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.

22 Kada ku ci zalun marayu da gwauraye.

23 In kun tsananta musu, ba shakka za su yi kuka gare ni, ni kuma, hakika zan ji kukansu.

24 Zan husata, in sa a kashe ku cikin yaƙi, matanku, su ma, su zama gwauraye, 'ya'yanku kuwa su zama marayu.

25 “Idan kun ranta wa jama'ata matalauta da suke tsakaninku kuɗi, ba za ku zama musu kamar masu ba da rance da ruwa ba. Kada ku nemi ruwan kuɗin daga gare su.

26 In har wani ya karɓi rigar amininsa jingina, lalle ne ya mayar masa da ita kafin faɗuwar rana.

27 Gama wannan ne kaɗai mayafinsa, da shi zai rufe huntancinsa. Da me zai rufa ya yi barci? Zan amsa masa kuwa in ya yi kuka gare ni, gama cike nake da juyayi.

28 “Kada ku saɓi Allah, kada kuma ku zagi mai mulkin jama'arku.

29 “Kada ku yi jinkirin fitar da zakar amfanin gonarku ta hatsi da ta abin matsewa. 'Ya'yan farinku, maza, kuma za ku ba ni su.

30 Haka kuma za ku yi da 'ya'yan farin shanunku, da na awakinku, da na tumakinku. Ɗan farin zai yi kwana bakwai tare da uwar, amma a rana ta takwas za ku ba ni shi.

31 “Za ku zama keɓaɓɓun mutane a gare ni. Kada ku ci dabbar da naman jeji ya yayyage shi, sai ku jefa wa karnuka.”

23

1 Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada wani ya haɗa baki da mugu ya zama munafukin mashaidi.

2 Kada ku yi mugunta domin galibin mutane na yi, kada kuwa ku yi shaidar zur a gaban shari'a don ku faranta zuciyar yawancin mutane, domin kada ku sa a kauce wa adalci.

3 Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari'a.

4 “Idan wani ya iske san maƙiyinsa ko jakinsa ya ɓace, sai ya komar masa da shi.

5 Idan wani ya ga kaya ya danne jakin maƙiyinsa kada ya tafi ya bar shi da shi, sai ya taimaka a ɗaga masa.

6 “Kada ku rasa yin adalci ga matalauci a wurin shari'a.

7 Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi da kuma adali, gama ba zan baratar da mugu ba.

8 Kada ku ci hanci, gama cin hanci yakan makantar da masu mulki, yakan kuma karkatar da manufar masu gaskiya.

9 “Kada ku wulakanta baƙo, kun dai san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.”

10 “Za ku nomi gonakinku shekara shida, kuna tattara amfaninsu.

11 Amma a shekara ta bakwai, ku bar su su huta kurum, ba za ku girbi kome daga ciki ba, domin mutanenku matalauta su ci abin da ya ragu, namomin jeji kuma su ci. Haka kuma za ku yi da gonakinku na inabi da na zaitun.

12 “Cikin kwana shida za ku yi aikinku, amma a kan rana ta bakwai sai ku huta, don shanunku da jakunanku su kuma su huta, don bayinku da baƙinku su wartsake.

13 Ku kula da dukan abin da na faɗa muku. Kada a ji bakinku na roƙon kome ga waɗansu alloli.”

14 “Sau uku a shekara za ku yi mini idi.

15 Wajibi ne ku yi idin abinci marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Za ku ci abinci marar yisti kwana bakwai lokacin da aka ayyana a watan Abib, gama a wannan wata ne kuka fito daga Masar. Kada wani ya zo wurina hannu wofi.

16 Ku kuma yi idin nunan fari na amfanin gonakinku da kaka. Sa'an nan kuma za ku yi idin gama tattara amfanin gonakinku a ƙarshen shekara.

17 Sau uku a shekara mazaje za su gabatar da kansu a gaban Ubangiji.

18 “Kada ku miƙa jinin hadayata tare da abinci mai yisti. Kada kuma ku ajiye kitsen abin da aka yanka a lokacin idina, ya kwana.

19 “Wajibi ne ku kawo mafi kyau daga cikin nunan fari na amfanin gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya cikin madarar uwarsa.”

20 “Ni da kaina zan aiki mala'ika a gabanku don ya kiyaye ku a sa'ad da kuke tafiya, ya kuma kai ku inda na shirya muku.

21 Ku nuna masa bangirma, ku kasa kunne ga maganarsa. Kada ku tayar masa, gama ba zai gafarta muku laifofinku ba, gama shi wakilina ne.

22 Idan kun kasa kunne a hankali ga maganarsa, kuka aikata dukan abin da na faɗa, sai in zama maƙiyin maƙiyanku da magabcin magabtanku.

23 Mala'ikana zai wuce gabanku, ya bi da ku inda Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan'aniyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa suke, zan kuma hallakar da su ƙaƙaf.

24 Ba za ku rusuna wa allolinsu ba, balle fa ku bauta musu, kada ku yi yadda suke yi. Sai ku hallaka allolinsu ɗungum, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu.

25 Za ku bauta wa Ubangiji Allahnku, ni kuwa zan yalwata abincinku da ruwan shanku, in kuma kawar muku da ciwo.

26 A ƙasarku, mace ba za ta yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.

27 “Zan aiki razanata a gabanku, in sa mutanen da za ku gamu da su su ruɗe. Zan sa maƙiyanku duka su ba ku baya, su sheƙa a guje.

28 Zan aiki zirnako a gabanku, su kore muku Hiwiyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa.

29 Ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar ta zama kufai har namomin jeji su fi ƙarfinku.

30 Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku ya kai yadda za ku mallaki ƙasar.

31 Zan yanka muku kan iyaka daga Bahar Maliya zuwa tekun Filistiyawa, daga jeji kuma zuwa Kogin Yufiretis. Gama zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kore su daga gabanku.

32 Kada ku ƙulla alkawari da su, ko da allolinsu.

33 Kada su zauna cikin ƙasarku domin kada su sa ku ku yi mini zunubi, ku bauta wa allolinsu, har abin kuwa ya zamar muku tarko.”

24

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku zo wurina, kai, da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila. Ku yi sujada daga nesa kaɗan.

2 Musa ne kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama'a su hau tare da shi.”

3 Musa ya tafi, ya faɗa wa jama'a dukan dokokin Ubangiji da ka'idodinsa, sai dukan jama'a suka amsa gaba ɗaya, suka ce, “Za mu kiyaye dukan dokokin da Ubangiji ya ba mu.”

4 Musa kuwa ya rubuta dukan dokokin Ubangiji. Kashegari da sassafe ya gina bagade a gindin dutsen, da kuma ginshiƙai goma sha biyu bisa ga yawan kabilai goma sha biyu na Isra'ila.

5 Ya kuma sa samarin Isra'ila su miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama, da bijimai ga Ubangiji.

6 Sai Musa ya zuba rabin jinin a tasa, sauran rabin jinin kuwa ya yayyafa a kan bagade.

7 Ya kuma ɗauki Littafin Alkawari, ya karanta wa jama'a, sai suka ce, “Za mu yi dukan abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi biyayya.”

8 Musa kuwa ya ɗauki jinin ya watsa wa jama'ar. Sa'an nan ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, wanda yake cikin dokokin nan duka.”

9 Musa ya haura tare da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawan nan saba'in na Isra'ila.

10 Suka ga Allah na Isra'ila. Wurin da yake ƙarƙashin tafin ƙafafunsa yana kama da daɓen da aka yi da dutsen yakutu, garau kamar sararin sama.

11 Amma Ubangiji bai yi wa dattawan Isra'ila wani abu ba, ko da yake suka ga zatin Allah. Su kuma suka ci suka sha a gaban Allah.

12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka hawo zuwa wurina a bisa dutsen, ka zauna har in ba ka allunan dutse da yake da dokoki da farillan da na rubuta don a koya musu.”

13 Sai Musa ya tashi, shi da baransa Joshuwa, suka tafi, suka hau dutsen Allah.

14 Ya ce wa dattawan, “Ku dakata a nan har mu komo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai ya je wurinsu.” Sa'an nan Musa ya hau bisa dutsen.

15 Da hawan Musa bisa dutsen, girgije ya rufe kan dutsen.

16 Ɗaukakar Ubangiji kuma ta zauna bisa Dutsen Sina'i. Girgijen ya lulluɓe dutsen har kwana shida, a rana ta bakwai kuwa Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.

17 Isra'ilawa suka ga ɗaukakar Ubangiji kamar wuta mai cinyewa a bisa ƙwanƙolin dutsen.

18 Sai Musa ya shiga girgijen, ya hau bisa dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba'in da dare arba'in.

25

1 Ubangiji ya ce wa Musa,

2 “Faɗa wa Isra'ilawa su karɓo mini kaya daga dukan wanda ya yi niyyar bayarwa.

3 Ga irin sadakokin da za ku karɓa, zinariya, da azurfa, da tagulla,

4 da ulu mai launin shuɗi, da mai launin shunayya, da mai launin ja, da lilin mai laushi, da gashin akuya,

5 da jemammun fatun raguna, da fatun awaki, da itacen ƙirya,

6 da mai domin fitila, da kayan yaji domin man keɓewa, da turaren ƙonawa,

7 da onis, da duwatsun da za a mammanne a falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

8 Za su yi tsattsarkan wuri domina, don in zauna tare da su.

9 Za ku yi mazaunina da kayayyakinsa duka, bisa ga irin fasalin da zan nuna maka.”

10 “Sai ku yi akwatin alkawari da itacen maje, tsawonsa ya zama kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa ya zama kamu ɗaya da rabi.

11 Ku dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje. Ku yi wa gyaffansa ado da gurun zinariya.

12 Za ku yi wa akwatin ƙawanya huɗu na zinariya ku liƙa a kowace kusurwar akwatin, wato ƙawanya biyu a kowane gefe na tsawon.

13 Za ku kuma yi sanduna da itacen ƙirya, ku dalaye su da zinariya.

14 Ku sa sandunan a kafar kowace ƙawanya da take gyaffan akwatin saboda ɗaukarsa.

15 Za a bar sandunan cikin ƙawanen akwatin, kada a zare su.

16 A kuma sa allunan da suke da dokokin da zan ba ka a cikin akwatin.

17 “Za ku yi wa akwatin murfi da zinariya tsantsa, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.

18 Za ku yi siffofin kerubobi biyu da ƙerarriyar zinariya, ku sa a gefen nan biyu na murfin.

19 Siffar kerub ɗaya a kowane gefe. Ku yi su ta yadda za su zama ɗaya da murfin.

20 Fikafikan kerubobin za su miƙe bisa domin su inuwantar da murfin, za su fuskanci juna, suna duba murfin.

21 Za ku sa murfin bisa akwatin. A cikin akwatin kuwa za ku sa allunan da suke da dokokin da zan ba ka.

22 A nan zan zo in sadu da kai, in yi magana da kai, wato tsakanin kerubobi biyu da suke bisa akwatin alkawari. Zan ba ka umarnaina duka don Isra'ilawa.”

23 “Ku yi tebur da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu, fāɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa kuma kamu ɗaya da rabi.

24 Ku dalaye shi da zinariya tsantsa, ku kuma yi masa ado kewaye da gurun zinariya.

25 Za ku yi wa tebur ɗin dajiya mai fāɗin tafin hannu, ku kuma yi wa dajiyar ado da gurun zinariya.

26 Za ku yi ƙawanya huɗu da zinariya, ku sa a kusurwa huɗu na ƙafafun teburin.

27 Ƙawanen za su kasance kusa da dajiyar don su riƙe sandunan ɗaukar teburin.

28 Ku yi sanduna da itacen ƙirya, sa'an nan ku dalaye su da zinariya. Da su za a riƙa ɗaukar teburin.

29 Da zinariya tsantsa kuma za ku yi farantansa, da kwanonin tuya, da butocinsa, da kwanoninsa domin yin hadayu na sha.

30 Kullum za ku riƙa ajiye gurasar da kuke kawo mini a bisa teburin.”

31 “Ku kuma yi alkuki da zinariya tsantsa. Ku yi gindinsa da gorar jikinsa da ƙerarriyar zinariya. Ƙoƙuna, da mahaɗai, da furanninsa a haɗe da shi za ku yi su.

32 Alkukin ya kasance da rassa shida, rassa uku a kowane gefe.

33 A kowane reshe na alkuki za a yi ƙoƙuna uku masu kamar tohon almond. Ya kasance kuma da mahaɗai da furanni.

34 Za a yi wa gorar alkukin ƙoƙuna huɗu masu kamar tohon almond, da mahaɗai da furanni.

35 A gindin kowane reshe biyu za a yi mahaɗi ɗaya.

36 Da mahaɗai da rassan za su kasance a haɗe da alkukin. Da ƙerarriyar zinariya za a yi su.

37 Ku kuma yi fitilu bakwai, ku sa su a bisa alkukin ta yadda za su haskaka wajen da suka fuskanta.

38 Ku kuma yi hantsuka da farantai da zinariya tsantsa.

39 Da zinariya tsantsa na talanti ɗaya za ku yi alkukin da waɗannan abubuwa duka.

40 Sai ku lura, ku yi waɗannan abubuwa duka bisa ga fasalin da aka nuna maka a bisa dutsen.”

26

1 “Alfarwar kanta, za ku yi ta da labule goma na lilin mai laushi ninki biyu, da ulu mai launi shuɗi, da launi shunayya da launi ja. Waɗannan labule za a yi musu zānen siffofin kerubobi, aikin gwani.

2 Tsawon kowane labule zai zama kamu ashirin da takwas, fāɗinsa kuwa kamu huɗu. Labulen su zama daidai wa daida.

3 Labule biyar biyar, za a harhaɗa, a ɗinka.

4 Ku kuma yi wa labulen nan biyu hantuna na shuɗi a karbunsu na bisa.

5 Za ku yi wa kowane labule hantuna hamsin. Hantunan labulen nan biyu su yi daura da juna.

6 Za ku yi maɗauri guda hamsin da zinariya don a haɗa hantuna na labulen nan domin alfarwa ta zama ɗaya.

7 “Ku yi labule goma sha ɗaya da gashin awaki, da za ku rufe alfarwar da shi.

8 Tsawon kowanne zai zama kamu talatin, fāɗinsa kamu huɗu. Labulen za su zama daidai wa daida.

9 Za ku harhaɗa biyar ku ɗinka. Haka kuma za ku yi da sauran shidan. Ku ninka na shida riɓi biyu, ku yi labulen ƙofar alfarwa da shi.

10 Za ku kuma sa hantuna hamsin a karbun labulen daga bisa. Haka nan kuma za a sa hantuna hamsin a karbun ɗayan.

11 Sa'an nan ku yi maɗauri hamsin da tagulla, ku ɗaura hantunan da su don ku haɗa alfarwar ta zama ɗaya.

12 Ragowar rabin labulen da yake a bisa alfarwar, sai a bar shi yana reto a bayan alfarwar.

13 Kamu ɗayan da ya ragu a kowane gefe na tsawon, sai a bar shi yana reto a kowane gefe domin ya rufe alfarwar.

14 Za ku yi abin rufe alfarwa da fatun raguna da aka rina ja, za ku kuma yi wani abin rufewa da fatun da aka jeme.

15 “Za ku yi alfarwar da katakon itacen ƙirya. Za ku kakkafa su a tsaye.

16 Tsawon kowane katako zai zama kamu goma, fāɗinsa kamu ɗaya da rabi.

17 Za a fiƙe kan kowane katako. Haka za ku yi da dukan katakan.

18 Za ku shirya katakan alfarwa kamar haka, katakai ashirin wajen gefen kudu.

19 Ku kuma yi kwasfa arba'in da azurfa da za a sa wa katakan nan ashirin. Za a sa kawunan katakan da aka fiƙe a cikin kwasfa.

20 Za ku kuma kafa katakai ashirin wajen gefen arewa na alfarwar.

21 Haka kuma za ku yi kwasfa arba'in da azurfa dominsu. Kwasfa biyu domin kowane katako.

22 A wajen yamma ga alfarwa kuma ku kafa katakai shida.

23 Ku kuma sa katakai biyu a kowace kusurwa ta yamma a alfarwa.

24 Katakan nan kuwa, sai a haɗa su daga ƙasa zuwa sama, a ɗaure. Haka za a yi da katakan kusurwan nan biyu. Za su zama na kusurwa biyu.

25 Za a sami katakai takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida, kowane katako yana da kwasfa biyu.

26 “Sai ku yi sanduna da itacen ƙirya. Sanduna biyar domin katakai na gefe ɗaya.

27 Biyar kuma domin katakai na wancan gefe. Har yanzu kuma biyar domin katakai na gefen yamma.

28 Sandan da yake tsakiyar katakan zai bi daga wannan gefe zuwa ƙarshen wancan gefe.

29 Za ku dalaye katakan da zinariya, ku kuma yi musu ƙawanen zinariya inda za a sa sandunan. Za ku dalaye sanduna kuma da zinariya.

30 Ta haka za ku yi alfarwar bisa ga fasalin da aka nuna maka a bisa dutsen.

31 “Za ku yi labule da lallausan zaren lilin, mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. A yi shi da gwaninta, a zana siffofin kerubobi a kansa.

32 Ku rataye shi a bisa dirkoki huɗu nan itacen ƙirya waɗanda aka dalaye da zinariya, da maratayansu na zinariya waɗanda aka sa cikin kwasfa huɗu na azurfa.

33 Za ku sa labulen a ƙarƙashin maɗauran, sa'an nan ku shigar da akwatin alkawari a bayan labulen. Labulen zai raba tsakanin Wuri Mai Tsarki da Wuri Mafi Tsarki.

34 Ku sa murfin a bisa akwatin alkawari a Wuri Mafi Tsarki.

35 Sai ku sa teburin a gaban labulen wajen arewa, ku kuma sa alkukin a kudancin alfarwar daura da teburin.

36 Haka nan kuma za ku yi wa ƙofar alfarwa makari da lallausan zaren lilin mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi, aikin mai gwaninta.

37 Ku yi dirkoki biyar da itacen ƙirya saboda makarin, ku dalaye su da zinariya. Ku kuma yi maratayansu da zinariya. Ku yi wa waɗannan dirkoki kwasfa biyar da tagulla.”

27

1 “Za ku yi bagaden da itacen ƙirya, mai tsawo kamu biyar, da fāɗi kamu biyar, tsayinsa kamu uku. Bagaden zai zama murabba'i.

2 A yi masa zankaye a kusurwoyinsa. Za ku haɗa zankayen da jikin bagaden. Za ku dalaye bagaden duka da tagulla.

3 Za ku ƙera kwanoni domin tokar bagade, da manyan cokula da daruna, da cokula masu yatsotsi, da kuma farantai domin wuta. Za ku ƙera dukan kayayyakin bagaden da tagulla.

4 Za ku kuma yi wa bagaden raga da tagulla, sa'an nan ku sa wa ragar ƙawane a kusurwoyinta huɗu.

5 Za ku sa ragar a cikin bagaden a tsakiya.

6 Ku yi wa bagaden sanduna da itacen ƙirya, sa'an nan ku dalaye su da tagulla.

7 Za a zura sandunan a ƙawanen da suke gyaffan bagade don ɗaukarsa.

8 Za ku yi bagaden da katakai, sa'an nan ku roɓe cikinsa. Ku yi shi bisa ga fasalin da na nuna maka bisa dutsen.

9 “Za ku yi wa alfarwa farfajiya. A kudancin farfajiyar, sai ku rataye labule mai tsawo kamu ɗari wanda aka saƙa da lallausan zaren lilin.

10 Za ku yi masa dirkoki guda ashirin, da kwasfansu guda ashirin da tagulla, amma ku yi wa dirkokin maratayai da maɗaurai da azurfa.

11 A wajen arewa kuma, sai ku rataya labule mai tsawon kamu ɗari. Ku yi masa dirkoki da kwasfansu guda ashirin da tagulla, amma ku yi wa dirkokin maratayai da maɗaurai da azurfa.

12 Fāɗin labulen a wajen yamma na farfajiyar, zai zama kamu hamsin. A yi wa labulen dirkoki goma, a kuma yi wa dirkokin kwasfa goma.

13 Fāɗin labulen wajen gabas na farfajiyar zai zama kamu hamsin.

14 Labulen ƙofa na gefe ɗaya zai zama kamu goma sha biyar, da dirkoki uku tare da kwasfansu uku.

15 Haka kuma labulen ƙofa na wancan gefe zai zama kamu goma sha biyar, da dirkoki uku tare da kwasfansu uku.

16 Za a saƙa labule mai kamu ashirin da lallausan zaren lilin mai launi shuɗi, da shunayya, da mulufi domin ƙofar farfajiyar. Za a sa wa ƙofar dirkoki huɗu tare da kwasfansu huɗu.

17 Za a yi wa dukan dirkokin da suke kewaye da farfajiyar maɗaurai da maratayai na azurfa, da kwasfa ta tagulla.

18 Tsawon farfajiyar zai zama kamu ɗari, fāɗinta kamu hamsin, tsayinta kamu biyar. Za a saƙa labulenta da lallausan zaren lilin, a kuma yi kwasfanta da tagulla.

19 Da tagulla kuma za a yi turakun alfarwar, da turakun farfajiyar, da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a cikin alfarwar.”

20 “Sai a umarci Isra'ilawa su kawo tsabtataccen man zaitun tatacce domin fitilar. Za a kunna fitilar ta yi ta ci koyaushe.

21 Za a ajiye ta a cikin alfarwar a gaban labule na wurin shaida. Haruna da 'ya'yansa za su lura da ita daga safiya har maraice. Wannan zai zama ka'ida har abada ga Isra'ilawa.”

28

1 “Daga cikin 'ya'ya maza na Isra'ila sai ka kirawo ɗan'uwanka Haruna tare da 'ya'yansa, Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar, su zama firistoci masu yi mini aiki.

2 A ɗinka wa Haruna ɗan'uwanka, tufafi masu tsarki domin daraja da kwarjini.

3 Ka kuma yi magana da gwanayen sana'a duka waɗanda na ba su fasaha, don su ɗinka wa Haruna tufafi, gama za a keɓe shi ya zama firist ɗina.

4 Waɗannan su ne irin tufafin da za su ɗinka, ƙyallen maƙalawa a ƙirji, da falmaran, da taguwa, da zilaika, da rawani, da abin ɗamara. Za su yi wa ɗan'uwanka, Haruna, da 'ya'yansa tufafi tsarkaka, don su zama firistoci masu yi mini aiki.

5 Sai su yi amfani da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin.

6 “Za su yi falmaran da zinariya, da shuɗi, da shunayya da mulufi, da lallausan zaren lilin, aikin gwani.

7 Za a yi mata kafaɗa biyu, sa'an nan a haɗa su a karbunsu.

8 Za a yi mata abin ɗamara da irin kayan da aka yi falmaran, wato da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. Za a yi mata saƙar gwaninta.

9 A kuma ɗauki duwatsu biyu masu daraja, a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a kai.

10 Sunaye shida a kowane dutse bi da bi bisa ga haihuwarsu.

11 Za a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a bisa duwatsun nan kamar yadda mai yin aiki da lu'ulu'u yakan zana hatimai. Za a sa kowane dutse a cikin tsaiko na zinariya.

12 A sa duwatsun a kafaɗun falmaran domin a riƙa tunawa da 'ya'yan Isra'ila. Haruna zai rataya sunayensu a kafaɗunsa a gaban Ubangiji domin a tuna da su.

13 Za ku yi tsaiko biyu na zinariya,

14 ku kuma yi tukakkun sarƙoki biyu na zinariya tsantsa. Za ku ɗaura wa tsaikunan nan tukakkun sarƙoƙi.

15 “Ku kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji domin neman nufin Allah. Sai a saƙa shi da gwaninta kamar yadda aka saƙa falmaran ɗin. A saƙa shi da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin.

16 Ƙyallen maƙalawa a ƙirji zai zama murabba'i, a ninke shi biyu tsawonsa da fāɗinsa su zama kamu ɗaya ɗaya.

17 Sai a yi jeri huɗu na duwatsun a kanta. A jeri na fari, a sa yakutu, da tofaz, da zumurrudu.

18 A jeri na biyu, a sa turkos, da saffir, da daimon.

19 A jeri na uku, a sa yakinta, da idon mage, da ametis.

20 A jeri na huɗu, a sa beril, da onis, da yasfa. Za a sa su cikin tsaiko na zinariya.

21 A bisa duwatsun nan goma sha biyu, sai a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila bisa ga kabilansu goma sha biyu. Za a zana sunayen kamar hatimi.

22 Ku kuma yi wa ƙyallen maƙalawa a ƙirji tukakkun sarƙoƙi na zinariya tsantsa.

23 Za ku yi ƙawanya biyu na zinariya, ku sa su a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

24 Ku sa tukakkun sarkoƙin nan biyu na zinariya a cikin ƙawanya biyu na zinariya da suke a gyaffan ƙyallen maƙalawa a ƙirji, a haɗa su daga gaba a kafaɗun falmaran.

25 Za ku kuma sa sauran bakunan sarƙoƙin nan biyu a cikin tsaikuna, sa'an nan a sa shi a gaban kafaɗun falmaran.

26 Ku kuma yi waɗansu ƙawane na zinariya, a sa su a sauran kusurwoyi na ƙyallen maƙalawa a ƙirji, a gefe na cikin da yake manne da falmaran.

27 Ku kuma yi waɗansu ƙawanya biyu na zinariya, a sa su a ƙashiyar kafaɗu biyu na falmaran daga gaba, a sama da abin ɗamaran nan.

28 Za su ɗaure ƙyallen maƙalawa a ƙirji a ƙawanensa haɗe da ƙawanen falmaran da shuɗiyar igiya domin ƙyallen maƙalawa a ƙirji ya zauna bisa abin ɗamarar falmaran, don kuma kada ya yi sako-sako a bisa falmaran.

29 Duk sa'ad da Haruna zai shiga Wuri Mai Tsarki, zai ɗauki sunayen 'ya'yan Isra'ila a gaban Ubangiji kullum, a kan ƙyallen maƙalawa domin nemar musu nufin Allah.

30 Za ku kuma sa Urim da Tummin a kan ƙyallen maƙalawar domin su kasance a zuciyar Haruna sa'ad da ya shiga gaban Ubangiji. Haka kuwa kullum Haruna zai riƙa kai kokekoken Isra'ilawa a gaban Ubangiji.

31 “Sai ku yi taguwar falmaran da shuɗi duka.

32 Za a yanke wuya a tsakiyarta don sawa. A yi wa wuyan shafi, sa'an nan a yi wa wuyan basitsa, wato cin wuya, domin kada ya kece.

33 Za a yi wa karbun taguwar ado da fasalin 'ya'yan rumman masu launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. A sa ƙararrawa ta zinariya a tsakankaninsu.

34 Za a jera su bi da bi, wato 'ya'yan rumman na biye da ƙararrawar zinariya.

35 Sai Haruna ya sa taguwar sa'ad da yake aiki. Za a ji ƙarar ƙararrawar a lokacin da yake shiga da lokacin da yake fita Wuri Mai Tsarki a gaban Ubangiji don kada ya mutu.

36 “Sai kuma a yi allo na zinariya tsantsa, a zana rubutu irin na hatimi a kansa haka, ‘MAI TSARKI GA UBANGIJI.’

37 Sai a ɗaura shi da shuɗiyar igiya a rawanin daga gaba.

38 Haruna kuwa zai sa shi bisa goshinsa, ta haka zai ɗauki kurakuran da ya yiwu Isra'ilawa sun yi cikin miƙa sadakokinsu masu tsarki. Kullum Haruna zai riƙa sa shi bisa goshinsa don su zama karɓaɓɓu ga Ubangiji.

39 “Ku saƙa zilaika da lallausan zaren lilin. Ku yi rawani da lallausan zaren lilin, ku kuma saƙa abin ɗamara mai ado.

40 “Za a yi wa 'ya'yan Haruna, maza, zilaiku, da abubuwan ɗamara, da huluna don daraja da kwarjini.

41 Ka sa wa Haruna, ɗan'uwanka, da 'ya'yansa maza, sa'an nan ka zuba musu mai, ka keɓe su, ka tsarkake su domin su zama firistoci masu yi mini aiki.

42 Sai kuma ku yi musu mukurai na lilin don su rufe tsiraicinsu daga kwankwaso zuwa cinya.

43 Haruna da 'ya'yansa maza za su sa su sa'ad da suke shiga alfarwa ta sujada ko kuwa sa'ad da suka kusaci bagade domin su yi aiki cikin Wuri Mai Tsarki domin kada su yi laifin da zai zama sanadin mutuwarsu. Wannan zai zama doka ga Haruna da zuriyarsa har abada.”

29

1 “Abin da za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa ke nan don ka keɓe su su zama firistoci masu yi mini aiki. Za ka ɗauki ɗan bijimi da raguna biyu marasa lahani,

2 da abinci marar yisti, da waina wadda aka cuɗe da mai, wadda aka yi da garin alkama mai laushi.

3 Ka sa waɗannan abu cikin kwando, sa'an nan ka kawo su cikin kwandon, ka kuma kawo ɗan bijimin da raguna biyu ɗin.

4 “Ka kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar alfarwar ta sujada, ka yi musu wanka.

5 Sa'an nan ka kawo tufafin, ka sa wa Haruna zilaikar, da taguwar falmaran, da falmaran ɗin, da ƙyallen maƙalawa a ƙirji, sa'an nan ka ɗaura masa ɗamarar falmaran wadda aka yi mata saƙar gwaninta.

6 Za ka naɗa masa rawanin, sa'an nan ka ɗora kambi mai tsarki a bisa rawanin.

7 Ka kuma ɗauki man keɓewa, ka zuba masa a ka domin ka keɓe shi.

8 “Sa'an nan ka kawo 'ya'yansa maza, ka sa musu zilaikun.

9 Ka kuma ɗaura musu ɗamara, ka sa musu hulunan. Aikin firist kuwa zai zama nasu har abada bisa ga dokar. Haka za ka keɓe Haruna da 'ya'yansa maza.

10 “A kuma kawo bijimin a ƙofar alfarwa ta sujada. Haruna da 'ya'yansa maza za su ɗora hannuwansu a kan bijimin.

11 Za ka yanka bijimin a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada.

12 Za ka ɗibi jinin bijimin ka sa a bisa zankayen bagaden da yatsanka. Sauran jinin kuwa ka zuba a gindin bagaden.

13 Ka cire dukan kitsen da yake rufe da kayan cikin, da kitsen da yake manne da hanta, da wanda yake manne a ƙoda biyu ɗin. Ka ƙone su a bisa bagaden.

14 Amma naman bijimin da fatarsa, da tarosonsa, za ka ƙone da wuta a bayan zango, wannan hadaya ce don zunubi.

15 “Sai a kawo rago ɗaya, Haruna kuwa da 'ya'yansa maza su ɗora hannuwansu a bisa ragon.

16 Sa'an nan ka yanka ragon, ka ɗibi jininsa, ka yayyafa shi kewaye a kan bagaden.

17 Ka kuma yanyanka rago gunduwa-gunduwa, ka wanke kayan cikinsa, da ƙafafunsa, ka haɗa su da gunduwoyin, da kan.

18 Sa'an nan ka ƙone ragon duka a bisa bagaden don ya ba da ƙanshi. Wannan hadaya ta ƙonawa ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, wato hadayar da aka ƙone da wuta.

19 “A kuma kawo ɗayan ragon, Haruna kuma da 'ya'yansa maza su ɗora hannuwansu a bisa ragon.

20 Sa'an nan ka yanka ragon, ka ɗibi jininsa ka shafa bisa leɓatun kunnen Haruna na dama, da bisa leɓatun kunnuwan 'ya'yansa maza na dama, da a kan manyan yatsotsin hannuwansu na dama, da kuma a kan manyan yatsotsin ƙafafunsu na dama. Sauran jinin kuwa, sai ka yayyafa shi a kewaye a kan bagaden.

21 Ka ɗiba daga cikin jinin da yake bisa bagaden, da man keɓewa, ka yayyafa wa Haruna da tufafinsa, da bisa 'ya'yansa maza, da tufafinsu don a tsarkake Haruna, da 'ya'yansa maza, da tufafinsu.

22 “Sai ka ɗebe kitsen ragon, ka yanke wutsiyarsa mai kitse, ka kuma ɗebe kitsen da yake rufe da kayan ciki, da dunƙulen kitsen da yake a bisa hanta, da ƙoda biyu ɗin da kitsensu, da cinyar dama, gama ragon na keɓewa ne.

23 Daga cikin kwandon abinci marar yistin da yake a gaban Ubangiji, sai ka ɗauki malmala ɗaya, da waina ɗaya da aka yi da mai, da ƙosai ɗaya.

24 Za ka sa waɗannan duka a hannun Haruna da na 'ya'yansa maza. Sai su kaɗa su domin hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.

25 Sa'an nan za ka karɓe su daga hannunsu, ka ƙone su a bisa bagaden kamar hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Ita hadaya ce ta ƙonawa da wuta ga Ubangiji.

26 “Za ka ɗauki ƙirjin ragon da aka yanka don keɓewar Haruna, ka kaɗa shi don hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. Wannan ƙirji zai zama rabonka.

27 Za ka tsarkake ƙirji na hadaya ta kaɗawa, da cinya ta hadaya ta ɗagawa da za a kaɗa a kuma ɗaga na ragon keɓewa, wanda yake na Haruna da wanda yake na 'ya'yansa maza.

28 Wannan zai zama rabon Haruna da na 'ya'yansa maza daga wurin Isra'ilawa. Gama wannan hadaya ta ɗagawa ce daga cikin hadayu na salama da Isra'ilawa za su miƙa wa Ubangiji.

29 “Keɓaɓɓun tufafin nan na Haruna za su zama na 'ya'yansa maza bayan rasuwarsa. Da tufafin nan ne za a zuba musu mai, a keɓe su.

30 Ɗan da ya gāje shi a matsayin firist shi ne zai sa su har kwana bakwai, lokacin da ya shiga alfarwa ta sujada, domin ya yi aiki a Wuri Mai Tsarki.

31 “Sai ka ɗauki naman ragon keɓewa, ka dafa shi a wuri mai tsarki.

32 Haruna da 'ya'yansa maza za su ci naman da abinci da yake a cikin kwandon a ƙofar alfarwa ta sujada.

33 Za su ci abubuwan nan da aka yi kafara da su a lokacin tsarkakewarsu da keɓewarsu. Ba wanda zai ci, sai su kaɗai, gama abubuwan nan tsarkaka ne.

34 Amma idan naman keɓewar ko abincin ya ragu har safiya, sai ka ƙone abin da ya ragu, kada a ci, gama tsattsarka ne.

35 “Haka nan za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa maza bisa ga dukan abin da na umarce ka. Kwana bakwai za ka ɗauka domin keɓewarsu.

36 A kowace rana za ka miƙa bijimi na hadaya domin zunubi ta yin kafara. Za ka tsarkake bagaden lokacin da ka yi kafara dominsa. Ka zuba masa mai, ka keɓe shi.

37 Kwana bakwai za ka ɗauka na yin kafara don bagaden, ka keɓe shi, haka kuwa bagaden zai zama mafi tsarki. Duk abin da ya taɓa bagaden zai tsarkaka.”

38 “Wannan shi ne abin da za a miƙa a bisa bagaden kullum, 'yan raguna biyu bana ɗaya ɗaya.

39 Za a miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya kuma da maraice.

40 Haɗe da rago na fari, za a miƙa mudun gari mai laushi garwaye da rubu'in moɗa na tataccen mai, da rubu'in moɗa na ruwan inabi domin hadaya ta sha.

41 Ɗaya ragon kuma a miƙa shi da maraice. Za a miƙa shi tare da hadaya ta gari, da hadaya ta sha kamar wadda aka yi da safe ɗin domin ta ba da ƙanshi mai daɗi, gama hadaya ce wadda aka ƙone da wuta ga Ubangiji.

42 Wannan hadaya ta ƙonawa za a riƙa yinta dukan zamananku a bakin ƙofar alfarwa ta sujada a gaban Ubangiji, inda ni zan sadu da kai in yi magana da kai.

43 Nan ne zan sadu da Isra'ilawa in tsarkake wurin da ɗaukakata.

44 Zan tsarkake alfarwa ta sujada da bagaden, zan kuma tsarkake Haruna da 'ya'yansa maza don su zama firistoci masu yi mini aiki.

45 Zan zauna tare da Isra'ilawa, in zama Allahnsu.

46 Za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu wanda ya fisshe su daga Masar don in zauna tare da su. Ni ne Ubangiji Allahnsu.”

30

1 “Za ku yi bagaden ƙona turare. Za ku yi shi da itacen ƙirya.

2 Tsawonsa da fāɗinsa kamu guda guda ne, zai zama murabba'i, amma tsayinsa ya zama kamu biyu. Za a haɗa zankayensa su zama ɗaya da shi.

3 Za ku dalaye shi, da bisansa, da gyaffansa, da zankayensa da zinariya tsantsa. Ku kuma yi masa dajiyar zinariya.

4 Za ku yi masa ƙawanya biyu na zinariya a ƙarƙashin dajiyar gefe da gefe, daura da juna. Ƙawanen za su zama inda za a zura sandunan ɗaukarsa.

5 Za ku yi sandunan da itacen ƙirya, ku dalaye su da zinariya.

6 Sai ku ajiye bagaden a gaban labulen akwatin alkawari da murfin akwati inda zan sadu da kai.

7 Haruna kuwa zai ƙona turare mai ƙanshi a bisansa kowace safiya lokacin da yake gyarta fitilun.

8 Zai kuma ƙona turaren sa'ad da ya kunna fitilun da almuru. Za a riƙa ƙona turare kullum a gaban Ubangiji dukan zamananku.

9 Ba za a ƙona wani irin turare dabam ba a bisansa, ba kuma za a miƙa hadaya ta ƙonawa, ko ta gari, ko ta sha, a bisansa ba.

10 Sau ɗaya a shekara Haruna zai yi kafara a bisa zankayensa. Zai yi kafara a bisansa da jinin hadaya don zunubi ta yin kafara. Za a riƙa yin wannan dukan zamananku, gama bagaden mai tsarki ne ga Ubangiji.”

11 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa,

12 “A sa'ad da za ku ƙidaya Isra'ilawa, sai ko wannensu ya biya fansar kansa ga Ubangiji domin kada annoba ta buge su lokacin da za ku ƙidaya su.

13 Dukan wanda aka lasafta shi cikin ƙidayar kuwa zai biya kuɗi bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. Tilas kowanne ya biya wannan, gama sadaka ce ga Ubangiji.

14 Duk wanda aka lasafta shi cikin ƙidayar tun daga mai shekara ashirin ko fi, zai ba da wannan sadaka ga Ubangiji.

15 Lokacin da kuke ba da wannan sadaka ga Ubangiji saboda kafarar rayukanku, mai samu ba zai zarce ba, matalauci kuma ba zai ba da abin da ya gaza abin da aka ƙayyade ba.

16 Za ku karɓi kuɗin nan na kafara daga wurin Isra'ilawa, ku ajiye shi domin aiki a alfarwa ta sujada. Zai zama abin tunawa ga Isra'ilawa a gaban Ubangiji, don su yi kafarar kansu.”

17 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,

18 “Sai ku yi daro da tagulla don wanka. Ku yi masa gammo da tagulla, ku ajiye shi tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, ku zuba ruwa a ciki.

19 A wurin ne Haruna da 'ya'yansa maza za su wanke hannuwansu da ƙafafunsu.

20 Sa'ad da suke shiga cikin alfarwa ta sujada ko sa'ad da suke kusatar bagade don su miƙa hadaya ta ƙonawa da wuta ga Ubangiji, sai su yi wanka don kada a kashe su.

21 Su wanke hannuwansu da ƙafafunsu don kada su mutu. Yin wannan zai zama musu da zuriyarsu farilla dukan zamanansu.”

22 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

23 “Ɗauki kayan yaji masu kyan gaske, ruwan mur na shekel ɗari biyar, da kirfa mai daɗin ƙanshi na shekel ɗari biyu da hamsin, da turaren wuta mai ƙanshi na shekel ɗari biyu da hamsin,

24 da kashiya na shekel ɗari biyar bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi, da moɗa ɗaya na man zaitun.

25 Da waɗannan za ku yi man keɓewa mai tsarki yadda mai yin turare yake yi, zai zama man keɓewa mai tsarki.

26 Za a shafa wa alfarwa ta sujada da akwatin alkawari wannan mai.

27 A kuma shafa wa teburin da kayayyakinsa, da alkukin da kayayyakinsa, da bagaden ƙona turare,

28 da bagaden hadaya ta ƙonawa da kayayyakinsa, da daron da gammonsa.

29 Ta haka za a tsarkake su domin su zama masu tsarki sosai. Duk abin da ya taɓa su zai tsarkaka.

30 Za ka zuba wa Haruna da ya'yansa maza mai, ka keɓe su domin su zama firistocina masu yi mini aiki.

31 Sai ka faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Wannan mai, mai tsarki ne a gare ni domin keɓewa a dukan zamananku.

32 Ba za a shafa wa kowa ba, ba kuma za a yi wani mai irinsa ba, gama man tsattsarka ne, saboda haka zai kasance tsattsarka a gare ku.

33 Duk wanda ya yi wani irinsa ko kuwa ya shafa wa wani, za a raba shi da jama'arsa.”’

34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ɗauki kayan yaji masu ƙanshi, su stakte, da onika, da galbanum tare da lubban. Su zama daidai wa daida.

35 Da waɗannan za a yi turare yadda mai yin turare yake yi, a sa masa gishiri, ya zama tsabtatacce, tsarkakakke.

36 A ɗauki kaɗan daga ciki, a niƙa, sa'an nan a ɗiba daga ciki, a ajiye a gaban akwatin alkawari a cikin alfarwa ta sujada a inda zan sadu da kai. Wannan turare zai zama muku mafi tsarki.

37 Irin turaren nan da za ku yi, ba za ku yi wa kanku irinsa ba. Zai zama abu mai tsarki a gare ku, gama na Ubangiji ne.

38 Duk wanda ya yi irin turaren nan don amfanin kansa, za a raba shi da jama'arsa.”

31

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

2 “Ga shi, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza.

3 Na cika shi da Ruhuna, da hikima, da basira, da ilimi, da fasaha,

4 don ya yi fasalin abubuwa na zinariya, da azurfa, da tagulla,

5 da yankan duwatsu masu tamani na jerawa, da sassaƙa itace, da kowane irin aikin fasaha.

6 Ga shi kuma, ni da kaina, na sa Oholiyab ɗan Ahisamak na kabilar Dan tare da shi, na kuma sa hikima a zukatan masu hikima, don su yi dukan abin da na umarce ka

7 a kan alfarwar ta sujada da akwatin alkawari, da murfin da yake bisansa, da dukan kayayyakin da yake cikin alfarwar,

8 da teburin da kayayyakinsa, da alkuki na zinariya tsantsa tare da dukan kayayyakinsa, da bagaden ƙona turare,

9 da bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayayyakinsa, da daron da gammonsa,

10 da saƙaƙƙun tufafi, wato da tsarkakakkun tufafin Haruna da na 'ya'yansa maza domin aikin firistoci,

11 da man keɓewa, da turaren nan mai ƙanshi domin Wuri Mai Tsarki. Za su yi su duka kamar yadda na umarce ka.”

12 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

13 “Faɗa wa Isra'ilawa, ‘Sai ku kiyaye Asabar domin shaida tsakanina da ku da zuriyarku har abada, domin ku sani ni ne Ubangiji wanda ya keɓe ku.

14 Ku kiyaye ranar Asabar gama tsattsarkar rana ce a gare ku. Duk wanda ya tozarta ta, za a kashe shi, duk wanda ya yi aiki kuma a cikinta za a raba shi da jama'arsa.

15 A kwana shida za a yi aiki, amma rana ta bakwai ranar hutawa ce tsattsarka ta saduda ga Ubangiji, don haka duk wanda ya yi kowane irin aiki a cikinta za a kashe shi.

16 Domin wannan fa Isra'ilawa za su kiyaye ranar Asabar, su kiyaye ta dukan zamanansu, gama madawwamin alkawari ne.

17 Ranar za ta zama dawwamammiyar shaida tsakanina da Isra'ilawa, cewa a kwana shida ni Ubangiji na yi sama da ƙasa, amma a rana ta bakwai na ajiye aiki, na huta.”’

18 Sa'ad da ya gama magana da Musa a kan Dutsen Sina'i, sai ya ba shi alluna biyu na shaida, allunan duwatsu rubatattu da yatsan Allah.

32

1 Da mutane suka ga Musa ya yi jinkirin saukowa daga dutsen, sai suka taru wurin Haruna, suka ce masa, “Tashi, ka yi mana allahn da zai shugabance mu, gama ba mu san abin da ya faru da Musa ɗin wanda ya fisshe mu daga ƙasar Masar ba.”

2 Haruna ya ce musu, “Ku tuttuɓe zobban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na 'ya'yanku maza da mata, ku kawo mini.”

3 Sai jama'a duka suka tuttuɓe zobban zinariya da suke a kunnuwansu, suka kawo wa Haruna.

4 Ya karɓi zobban a hannunsu, sai ya narkar da su, ya sassaƙa shi da kurfi, ya siffata ɗan maraƙi. Da jama'a suka gani, sai suka ce, “Allahnku ke nan, ya Isra'ila, wanda ya fisshe ku daga Masar.”

5 Sa'ad da Haruna ya gani, ya gina bagade a gaban siffar maraƙin, ya yi shela, ya ce, “Gobe akwai idi ga Ubangiji.”

6 Kashegari da sassafe, suka tashi, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama. Jama'ar kuma suka zauna su ci su sha, suka kuma tashi suna rawa.

7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama jama'arka da ka fito da su daga ƙasar Masar sun ƙazantar da kansu.

8 Sun yi saurin kaucewa daga hanyar da na umarce su. Sun yi wa kansu ɗan maraƙi na zubi, sun yi masa sujada, sun miƙa masa hadaya, sun kuma ce, ‘Ya Isra'ila, wannan shi ne allahn da ya fisshe ka daga ƙasar Masar.”’

9 Ya kuma ce wa Musa, “Na ga jama'an nan suna da taurinkai.

10 Yanzu dai, ka bar ni kawai fushina ya yi ƙuna a kansu, ya cinye su, amma kai zan maishe ka babbar al'umma.”

11 Amma Musa ya roƙi Ubangiji Allahnsa, ya ce, “Ya Ubangiji, me ya sa ka husata da mutanenka waɗanda ka fisshe su da ƙarfin ikonka mai girma daga ƙasar Masar?

12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, don ƙeta ce ya fitar da su, don ya kashe su cikin duwatsu, ya shafe su sarai daga duniya?’ Ka janye zafin fushinka, kada kuma ka jawo wa jama'arka masifa.

13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, waɗanda kai da kanka ka rantse musu, ka ce, ‘Zan riɓaɓɓanya zuriyarku kamar taurarin sama, in kuma ba ku wannan ƙasa duka da na alkawarta zan bayar ga zuriyarku. Za su kuwa gāje ta har abada.”’

14 Ubangiji kuwa ya huce, ya janye niyyarsa ta jawo masifa a kan jama'arsa.

15 Musa ya sauko daga kan dutsen da allunan dutsen nan biyu na shaida a hannunsa. Allunan rubutattu ne ciki da baya.

16 Allunan kuwa aikin Allah ne, rubutun kuma na Allah ne da ya zāna a kan allunan.

17 A sa'ad da Joshuwa ya ji hayaniyar jama'ar, sai ya ce wa Musa, “Akwai hargowar yaƙi a zangon.”

18 Musa kuwa ya ce, “Ai, wannan ba hargowar nasara ba ce, ba kuma ta waɗanda yaƙi ya ci ba ce, amma hayaniyar waƙa nake ji.”

19 Yana kusato zango, sai ya ga siffar ɗan maraƙi, mutane na ta rawa. Musa kuwa ya harzuƙa, ya watsar da allunan da suke hannunsa a gindin dutsen, suka farfashe.

20 Ya ɗauki siffar ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone ta, ya niƙe, ta zama gari, ya barbaɗa a ruwa, ya sa Isra'ilawa su sha.

21 Musa ya ce wa Haruna, “Me waɗannan mutane suka yi maka, da ka jawo musu babban zunubi?”

22 Haruna kuwa ya amsa, ya ce, “Ya shugabana, kada ka ji haushina, ka san jama'an nan sarai da irin halinsu na son aikata mugunta.

23 Sun ce mini, ‘Yi mana allahn da zai shugabance mu, gama Musa, mutumin da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya same shi ba.’

24 Ni kuwa sai na ce musu, ‘Bari duk wanda yake da zinariya ya tuɓe.’ Waɗanda suke da ita, suka tuɓe, suka kawo mini, ni kuwa na zuba su cikin wuta, daga nan wannan maraƙi ya fito.”

25 Musa ya ga jama'ar sun sangarce, domin Haruna ya sa su sangarce, ya bar su su bauta wa gunki har suka zama abin kunya a gaban magabtansu.

26 Musa ya tsaya a ƙofar zango, ya ce, “Duk wanda yake wajen Ubangiji ya zo wurina.” Sai Lawiyawa suka tattaru a wurinsa.

27 Ya ce musu, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Kowane mutum ya rataya takobinsa, ya kai ya kawo daga ƙofa zuwa ƙofa cikin zango duka, kowa ya kashe ɗan'uwansa, kowa ya kashe zumunsa, kowa ya kashe maƙwabcinsa.”’

28 Lawiyawa kuwa suka yi yadda Musa ya faɗa. A ranan nan aka kashe mutum wajen talata (3,000).

29 Sai Musa ya ce, “Yau kun ba da kanku ga Ubangiji, gama kowane mutum ya kashe ɗansa da ɗan'uwansa, ta haka kuka jawo wa kanku albarka yau.”

30 Kashegari, Musa ya ce wa mutane, “Kun aikata babban zunubi. Yanzu kuwa zan tafi wurin Ubangiji, watakila zan iya yin kafara domin zunubanku.”

31 Musa ya koma wurin Ubangiji, ya ce, “Kaito, mutanen nan sun aikata zunubi mai girma, sun yi wa kansu gunkin zinariya.

32 Amma ina roƙonka ka gafarta zunubansu, in kuwa ba haka ba, ina roƙonka ka shafe sunana daga cikin littafin da ka rubuta.”

33 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ai, dukan wanda ya yi mini zunubi, shi ne zan shafe sunansa daga cikin littafina.

34 Yanzu fa, sai ka tafi, ka bi da mutanen zuwa wurin da zan faɗa maka, ga shi, mala'ikana zai wuce gabanka. Duk da haka a ranar da zan waiwaye ku, zan hukunta su saboda zunubinsu.”

35 Sai Ubangiji ya aika wa mutanen da annoba saboda ɗan maraƙin da suka sa Haruna ya yi musu.

33

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi, ka kama hanya, kai da jama'ar da ka fisshe su daga ƙasar Masar, zuwa ƙasar da na rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, na ce, ‘Ga zuriyarka zan ba da ita.’

2 Zan kuwa aiki mala'ika a gabanka. Zan kuma kori Kan'aniyawa da Amoriyawa, da Hittiyawa, da Farizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa.

3 Ka kama hanya zuwa ƙasa mai yalwar abinci, amma fa ba zan tafi tare da ku ba, gama ku mutane ne masu taurin kai, domin kada in hallaka ku a hanya.”

4 Da jama'ar suka ji wannan mugun labari, sai suka yi nadama. Ba wanda ya sa kayan ado.

5 Gama Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa Isra'ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurin kai. In na yi tafiya tare da ku, nan da nan zan hallaka ku. Domin haka fa, yanzu, ku tuɓe kayan adonku, domin in san abin da zan yi da ku.”’

6 Domin haka Isra'ilawa suka tuɓe kayan adonsu tun daga dutsen Horeb har zuwa gaba.

7 Musa ya ɗauki alfarwa, ya kafa ta a bayan zango, nesa da zango. Ya kuwa sa mata suna, Alfarwa ta Sujada. Duk wanda yake neman Ubangiji, sai ya tafi alfarwa ta sujada, wanda yake a bayan zango.

8 Duk sa'ad da Musa ya tafi wurin alfarwar, jama'a duka sukan tashi tsaye, kowa ya tsaya a ƙofar alfarwarsa, ya kallaci Musa, har ya shiga alfarwar.

9 Sa'ad da Musa ya shiga alfarwar, al'amudin girgije ya sauko ya tsaya bisa ƙofar alfarwar, Ubangiji kuma ya yi magana da Musa.

10 A sa'ad da jama'a suka ga al'amudin girgijen nan na tsaye a ƙofar alfarwar, sai jama'ar duka su tashi su yi sujada, kowa a ƙofar alfarwarsa.

11 Ta haka Ubangiji ya riƙa yin magana da Musa baki da baki, kamar yadda mutum yakan yi magana da amininsa. Sa'ad da Musa ya koma cikin zango kuma, baransa, Joshuwa, ɗan Num, saurayi, ba zai fita daga cikin alfarwar ba.

12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Ga shi, ka faɗa mini cewa, ‘Ka fito da mutanen nan,’ amma ba ka sanar da ni wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi kuma, ka ce, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a gare ni.’

13 Yanzu ina roƙonka idan na sami tagomashi a gare ka, ka nuna mini hanyoyinka domin in san ka, in kuma sami tagomashi a wurinka, ka kuma tuna, wannan al'umma jama'arka ce.”

14 Ubangiji kuwa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma hutashe ka.”

15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za ka tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.

16 Yaya zan sani ko na sami tagomashi a wurinka, ni da jama'arka, in ba ka tafi tare da mu ba? Yaya ni da jama'arka, za a bambanta mu da sauran jama'ar da suke a duniya?”

17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka ce, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”

18 Musa kuwa ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini kanka.”

19 Sai Ubangiji ya ce masa, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda nā yi wa alheri, in nuna jinƙai ga wanda nā yi wa jinƙai.”

20 Ya kuma ce, “Ba za ka iya ganin fuskata ba, gama mutum ba zai gan ni ba, ya rayu.”

21 Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.

22 A sa'ad da zatina yake wucewa, zan sa ka a tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har in wuce,

23 sa'an nan in ɗauke hannuna, za ka kuwa ga bayana, amma ba za ka ga fuskata ba.”

34

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farkon, ni kuwa in rubuta kalmomin da suke cikin alluna na farko da ka farfasa.

2 Da safe ka shirya, ka zo Dutsen Sina'i ka gabatar da kanka gare ni a kan dutsen.

3 Kada wani mutum ya zo tare da kai, kada a ga kowane mutum a ko'ina a kan dutsen, kada a bar garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu su yi kiwo kusa da dutsen.”

4 Sai Musa ya sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ya tashi da sassafe, ya hau Dutsen Sina'i, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya riƙe allunan nan biyu na dutse a hannunsa.

5 Ubangiji kuwa ya sauko cikin girgije ya tsaya tare da shi a can, ya yi shelar sunansa.

6 Ya kuma gifta a gaban Musa, ya ce, “Ni ne Ubangiji, Ubangiji Allah mai jinƙai, mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna, mai gaskiya.

7 Ni ne mai nuna ƙauna ga dubbai, mai gafarta mugunta, da laifi, da zunubi, wanda ba zai kuɓutar da mai mugunta ba, amma saboda laifin iyaye nakan hukunta 'ya'ya da jikoki har tsara ta uku da ta huɗu.”

8 Sai Musa ya hanzarta, ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya yi sujada.

9 Ya ce, “Idan na sami tagomashi a gare ka, ya Ubangiji, ina roƙonka, ka yi tafiya tare da mu, ko da yake jama'a masu taurinkai ne, ka gafarta laifinmu, da zunubinmu, ka sa mu zama abin gādonka.”

10 Allah kuwa ya ce, “Ga shi, na yi alkawari, cewa a gaban dukan jama'a zan aikata al'ajabai irin waɗanda ba a taɓa aikatawa a duniya ba, ko cikin wata al'umma. Dukan mutanen da kuke zaune tare da su za su ga aikina, gama zan aikata abin bantsoro a cikinku.

11 Ku kiyaye abin da na umarce ku a wannan rana. Ga shi, zan kora muku Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa.

12 Ku fa kula da kanku, kada ku kuskura, ku ƙulla alkawari da mazaunan ƙasar inda za ku tafi, don kada su zama muku alƙalai.

13 Sai ku rurrushe bagadansu, ku farfashe al'amudansu, ku sassare gumakansu.

14 “Ba za ku yi wa wani allah sujada ba, sai dai ni, gama sunana Mai Kishi, gama ni Allah mai kishi ne.

15 Kada ku ƙulla alkawari da mazaunan ƙasar don kada sa'ad da suke shagulgulan bidi'arsu ga allolinsu, suna miƙa musu hadaya, waninsu ya gayyace ku ku ci abin hadayarsa.

16 Kada kuma ku auro wa 'ya'yanku maza 'yan matansu 'ya'ya matansu kuma su yi shagulgulan bidi'ar allolinsu, har su sa 'ya'yanku su bi allolinsu.

17 “Kada ku yi wa kanku alloli na zubi.

18 “Sai ku kiyaye idin abinci marar yisti har kwana bakwai a ƙayyadadden lokacinsa a watan Abib, gama a watan Abib kuka fito Masar. A lokacin za ku ci abinci marar yisti kamar yadda na umarce ku.

19 “Kowane ɗan farin mutum, ko na dabba nawa ne, duk da 'ya'yan farin dabbobinku, wato ɗan farin saniya da na tunkiya.

20 Ɗan farin jaki kuwa za ku fansa da ɗan rago, in kuwa ba za ku fansa da ɗan rago ba, sai ku karya wuyansa. Za ku fanshi kowane ɗan fari. Kada a sami wanda ya zo gabana hannu wofi.

21 “Cikin kwana shida za ku yi aiki, amma a kan rana ta bakwai sai ku huta, ko lokacin noma ne, ko lokacin girbi sai ku huta.

22 “Ku kuma kiyaye idin mako, wato idin girbin nunan fari na alkama, da idin gama tattara amfanin gonaki a ƙarshen shekara.

23 “Sau uku cikin shekara mazajenku duka za su hallara a gabana, ni Ubangiji Allah na Isra'ila.

24 Gama zan kori al'ummai daga gabanku, in fāɗaɗa kan iyakarku. Ba wanda zai yi ƙyashin ƙasarku a lokatan nan uku na shekara da kukan hallara a gaban Ubangiji Allahnku.

25 “Ba za ku miƙa jinin hadayata tare da abinci mai yisti ba, kada kuma a bar hadaya ta Idin Ƙetarewa ta kwana.

26 “Sai ku kawo nunan farin amfanin gonarku a cikin gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya da madarar uwarsa.”

27 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, “Rubuta waɗannan kalmomi, gama daidai suke da kalmomin alkawarin da suke tsakanina, da kai, da Isra'ila.”

28 Musa kuwa yana tare da Ubangiji yini arba'in da dare arba'in, bai ci ba, bai sha ba. Sai ya rubuta kalmomin alkawarin a kan allunan, wato dokokin nan goma.

29 Sa'ad da Musa ya sauko daga Dutsen Sina'i da alluna biyu na alkawarin a hannunsa, ashe, bai sani ba, amma fuskarsa tana annuri saboda zaman da ya yi a gaban Ubangiji.

30 Sa'ad da Haruna da dukan jama'ar Isra'ila suka ga fuskar Musa tana annuri, suka ji tsoro su kusace shi.

31 Sai Musa ya kirawo Haruna tare da shugabannin jama'ar duka, suka zo wurinsa, shi kuwa ya yi magana da su.

32 Daga nan jama'ar Isra'ila duka suka matsa kusa, Musa kuwa ya ba su dukan dokoki waɗanda Ubangiji ya ba shi a bisa Dutsen Sina'i.

33 Da Musa ya gama magana da su, sai ya lulluɓe fuskarsa.

34 Amma duk lokacin da ya je gaban Ubangiji domin ya yi magana da shi, sai ya kware lulluɓin, har lokacin da ya fito. Idan ya fito, sai ya faɗa wa jama'ar Isra'ila abin da aka umarce shi.

35 Jama'ar Isra'ila kuwa sukan ga fuskar Musa tana annuri. Sa'an nan Musa ya sāke lulluɓe fuskarsa, har lokacin da ya shiga don ya yi magana da Ubangiji.

35

1 Sai Musa ya tattara dukan taron jama'ar Isra'ila, ya ce musu, “Waɗannan su ne abubuwan da Ubangiji ya umarce ku ku yi.

2 Cikin kwana shida za a yi aiki, amma rana ta bakwai Asabar ce tsattsarka ta Ubangiji ta hutawa sosai. Duk wanda ya yi kowane irin aiki a cikinta, sai a kashe shi.

3 Ba za ku hura wuta a ranar Asabar a wuraren zamanku ba.”

4 Musa kuma ya ce wa taron jama'ar Isra'ila duka, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta,

5 ku karɓi sadaka daga cikinku saboda Ubangiji. Duk wanda ya yi niyya, bari ya kawo wa Ubangiji sadaka ta zinariya, da azurfa, da tagulla,

6 da zane na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin, da gashin awaki,

7 da fatun raguna da aka rina suka zama ja, da fatun awaki, da itacen ƙirya,

8 da man fitila, da kayan yaji domin man keɓewa da turaren ƙonawa,

9 da duwatsu masu tamani, da duwatsun da za a mammanne a falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.”

10 “Bari dukan wanda yake da fasaha a cikinku ya zo, ya yi aikin da Ubangiji ya umarta a yi,

11 wato aikin alfarwa ta sujada, da alfarwarta da murfinta, da maratayai, da katakanta da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta,

12 da akwati da sandunansa, da murfinsa, da labulen ƙofar.

13 Da tebur da sandunansa, da kayayyakinsa duka, da gurasar ajiyewa,

14 da alkuki don haske, da kayayyakinsa, da fitilunsa, da man fitila,

15 da bagaden turaren ƙonawa da sandunansa, da man keɓewa mai ƙanshi, da turaren ƙonawa, da labulen ƙofar alfarwa ta sujada,

16 da bagaden ƙona hadaya da ragarsa ta tagulla da sandunansa, da kayayyakinsa duka, da daro da gammonsa,

17 da labulen farfajiya da dirkokinsa da kwasfansu, da labulen ƙofar farfajiyar,

18 da turakun alfarwa, da turakun farfajiyar, da igiyoyinsu,

19 da saƙaƙƙun tufafi na yin aiki a Wuri Mai Tsarki, da tsarkakakkun tufafin Haruna firist, da tufafin 'ya'yansa maza na aikin firist.”

20 Sa'an nan dukan taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga wurin Musa.

21 Duk wanda ya yi niyya, da wanda ruhunsa ya iza shi ya kawo wa Ubangiji sadaka don yin alfarwa ta sujada, da dukan ayyukansa, da tsarkakakkun tufafi.

22 Sai dukan mata da maza waɗanda suke da niyya, suka kawo kayayyakin ƙawanya, wato da 'yan kunne, da ƙawane, da mundaye, da kayayyakin zinariya iri iri. Kowane mutum ya ba da sadaka ta zinariya ga Ubangiji.

23 Kowane mutum da aka iske shi yana da shuɗi, ko shunayya, ko mulufi, ko lallausan lilin, ko gashin awaki, ko fatun raguna da aka rina suka zama ja, ko fatun awaki, ya kawo su.

24 Kowane ne wanda ya iya, ya ba da sadaka ta azurfa, da ta tagulla ga Ubangiji. Duka kuma wanda aka iske shi yana da itacen ƙirya wanda zai yi amfani a cikin aikin, ya kawo shi.

25 Dukan mata masu hikima suka kaɗa zare da hannuwansu, suka kawo zaren da suka kaɗa na shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin.

26 Sai kuma dukan mata masu hikima, waɗanda zuciyarsu ta iza su, suka kaɗa zare da gashin awaki.

27 Su shugabanni suka kawo duwatsu masu daraja da za a jera a kan falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

28 Suka kuma kawo kayan yaji, da man fitila, da man keɓewa, da turaren ƙonawa.

29 Sai dukan mata da maza na Isra'ilawa waɗanda zuciyarsu ta iza su, suka kawo kowane irin abu domin yin aikin da Ubangiji ya umarci Musa. Suka kawo sadaka ta yardar rai ga Ubangiji.

30 Sai Musa ya ce wa Isra'ilawa, “Ga shi, Ubangiji ya zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza.

31 Ya cika shi da ruhu na hikima, da basira, da sani, da fasaha na iya yin kowane irin aiki.

32 Domin ƙirƙiro zāne-zāne na gwaninta, waɗanda za a yi da zinariya, da azurfa, da tagulla.

33 Haka kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa, da sassaƙar itace, da kowane irin aiki na gwaninta.

34 Ubangiji ya ba Bezalel, da Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, hikimar koya wa waɗansu sana'a.

35 Gama ya cika su da hikima ta yin kowane irin aiki na sassaƙa da na zāne-zāne, da na yin ɗinke-ɗinke da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin, da na yin saƙa. Sun iya yin kowane irin aiki da yin zāne-zāne.

36

1 “Da Bezalel da Oholiyab, da kowane mutum mai hikima, waɗanda Ubangiji ya ba su hikima da basira na sanin yin kowane irin aiki, za su shirya Wuri Mai Tsarki kamar yadda Ubangiji ya umarta.”

2 Sai Musa ya kirayi Bezalel, da Oholiyab, da kowane mutum mai hikima wanda Ubangiji ya ba shi hikima a zuciya, da duk wanda zuciyarsa ta iza shi ya zo, ya yi aikin.

3 Su kuwa suka karɓa daga wurin Musa dukan sadaka ta yardar rai da Isra'ilawa suka kawo don yin aikin alfarwa ta sujada. Jama'a suka yi ta kawo masa sadaka ta yardar rai kowace safiya.

4 Sai masu hikiman da suke yin aiki na alfarwa ta sujada suka ɗan dakatar da aiki suka tafi wurin Musa.

5 Suka ce masa, “Jama'a suna ta kawo sadaka fiye da abin da ake bukata domin aikin da Ubangiji ya umarta a yi.”

6 Sai Musa ya umarce su su yi shela a zango cewa, “Kada wata mace ko wani namiji ya sāke kawo sadaka don aikin alfarwa ta sujada.” Sai jama'a suka daina kawowa.

7 Gama abin da aka kawo ya isa yin aikin, har da ragi.

8 Sai dukan mutane masu gwaninta daga cikin ma'aikatan, suka yi alfarwa da labule goma. An yi labulen da lallausan zaren lilin na shuɗi, da shunayya, da mulufi. Aka yi wa labulen zānen kerubobi na gwaninta.

9 Tsawon kowane labule kamu ashirin da takwas, fāɗinsa kuma kamu huɗu ne. Dukan labulen girmansu ɗaya ne.

10 Ya ɗinɗinke labule biyar a harhaɗe, haka kuma ya yi da sauran labule biyar.

11 Sai ya sa shuɗɗan hantuna a karbun labule na fari da na biyu.

12 Ya sa hantuna hamsin a karbun labule na fari, haka kuma ya sa na biyun. Dukan hantunan suna daura da juna.

13 Ya kuma yi maɗauri hamsin na zinariya, ya harhaɗa labule da juna da maɗauran domin alfarwa ta zama ɗaya.

14 Ya kuma yi labule goma sha ɗaya da gashin awaki domin ya rufe alfarwa.

15 Tsawon kowane labule kamu talatin, fāɗinsa kuma kamu huɗu ne. Labule goma sha ɗayan nan girmansu ɗaya ne.

16 Ya harhaɗa labule biyar wuri ɗaya, shida kuma ya harhaɗa su wuri ɗaya.

17 Sai ya yi hantuna hamsin, ya sa a karbu na bisa na labule na farin, haka kuma ya sa hantuna hamsin a karbun sama na labule na biyu.

18 Ya kuma yi maɗaurai da tagulla waɗanda zai harhaɗa hantuna da su don alfarwa ta zama ɗaya.

19 Ya yi wa alfarwa murfi da fatun raguna da aka rina ja, ya kuma yi wani abin rufewa da fatuna da aka jeme.

20 Ya kuma yi katakan alfarwa da itacen ƙirya.

21 Tsawon kowane katako kamu goma ne, kaurinsa kuma kamu ɗaya da rabi ne.

22 Kowane katako an fiƙe bakinsa biyu don a harhaɗa su tare, haka ya yi da dukan katakan alfarwa.

23 Yadda ya yi da katakan alfarwa ke nan, ya kafa katakai ashirin a fuskar kudu.

24 Sai ya yi kwasfa arba'in da azurfa domin katakai ashirin. Kowane katako yana da kwasfa biyu saboda bakinsa biyu da aka fiƙe.

25 A fuska ta biyu ta wajen arewa ta alfarwa, ya kafa katakai ashirin.

26 Ya kuma yi kwasfa arba'in na azurfa. Kowane katako yana da kwasfa biyu.

27 Ya yi katakai shida a bayan alfarwa a fuskar yamma.

28 Ya kuma yi katakai biyu don kusurwar baya ta alfarwa.

29 Aka haɗa katakai daga ƙasa har zuwa sama inda aka haɗa su a ƙawanya ta fari, haka ya yi da su a kusurwoyin nan biyu.

30 Akwai katako takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida. Kowane katako yana da kwasfa biyu.

31 Sai ya yi sanduna na itacen ƙirya, sanduna biyar domin katakan gefe ɗaya na alfarwa,

32 sanduna biyar kuma domin katakan ɗaya gefen na alfarwa, biyar kuma domin katakan da yake baya na alfarwa wajen yamma.

33 Ya sa sandan da yake a tsakiya ya wuce daga wannan gefe zuwa wancan gefe.

34 Ya dalaye katakai da zinariya. Ya yi musu ƙawane na zinariya inda za a sarƙafa sandunan. Ya kuma dalaye sandunan da zinariya.

35 Ya kuma yi labule da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin, ya kuma yi wa labulen zānen kerubobi na gwaninta.

36 Ya yi wa labulen dirkoki huɗu da itacen ƙirya. Sai ya dalaye su da zinariya. Ya kuma yi musu maratayai da zinariya. Ya yi wa dirkokin nan kwasfa huɗu da azurfa.

37 Ya yi wa ƙofar alfarwa labulen da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. Ya yi wa labulen ado.

38 Ya haɗa labulen da dirkokinsa biyar, da maratayansu. Ya dalaye kawunansu da maɗauransu da zinariya, amma ya dalaye kwasfansu guda biyar da tagulla.

37

1 Bezalel ya yi akwati da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.

2 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje, ya kuma yi masa dajiya da zinariya kewaye da shi.

3 Ya sa masa ƙawanya huɗu na zinariya a kan kusurwoyinsa huɗu, ƙawane biyu a wannan gefe, biyu kuma a wancan gefe.

4 Ya kuma yi sandunan da itacen ƙirya, ya dalaye su da zinariya.

5 Sai ya zura sandunan cikin ƙawanen da suke a gyaffan akwatin don ɗaukarsa.

6 Ya yi murfin da zinariya tsantsa, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.

7 Ya kuma ƙera siffofin kerubobi biyu da zinariya, ya maƙala su a gefe biyu na murfin.

8 Kerub ɗaya a wannan gefe, ɗaya kuma a wancan gefe. Ya yi su a haɗe da murfin a gefe biyu na murfin.

9 Kerubobin suka buɗe fikafikansu sama, suka inuwantar da murfin da fikafikansu. Fuskokinsu kuma na duban juna, suna kuma fuskantar murfin.

10 Sai kuma ya yi tebur da itacen ƙirya, tsawsonsa kamu biyu, fāɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.

11 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, ya yi masa dajiya da zinariya.

12 Ya yi masa dajiya mai fāɗin tafin hannu kewaye da shi, ya kuma yi wata dajiya da zinariya kewaye da ita.

13 Ya yi wa tebur ɗin ƙawane huɗu na zinariya, ya manna ƙawane a kusurwoyi huɗu na ƙafafunsa.

14 Ƙawanen suna kusa da dajiyar inda za a zura sanduna na ɗaukar teburin.

15 Ya yi sanduna da itacen ƙirya don ɗaukar teburin. Sa'an nan ya dalaye su da zinariya.

16 Ya yi kayan teburin da zinariya tsantsa, wato farantansa, da kwanonin tuya, da kwanoninsa, da butoci domin yin hadaya ta sha.

17 Ya yi alkuki da zinariya tsantsa. An yi gindinsa da gorar jikinsa da ƙerarriyar zinariya. Ƙoƙunan alkukin da mahaɗansa, da furanninsa, a haɗe aka yi su da alkukin.

18 Akwai rassan fitila guda shida, uku a wannan gefe, uku kuma a wancan.

19 A kowane reshe na alkukin akwai ƙoƙuna uku masu kamar tohon almond, akwai kuma mahaɗai da furanni.

20 A bisa alkukin kuma akwai ƙoƙuna guda huɗu da aka yi su kamar tohon almond, da mahaɗai, da furanni.

21 Akwai mahaɗi kuma a ƙarƙashin kowane reshe biyu biyu na dukan rassan guda shida, a miƙe daga alkukin.

22 An ƙera mahaɗai da rassan alkuki a haɗe. Da ƙerarriyar zinariya aka yi alkukin da dukan kome nasa a haɗe.

23 Da zinariya tsantsa ya yi fitilu bakwai, da hantsuka da farantansa.

24 Da zinariya tsantsa na talanti ɗaya ya yi alkukin da kayayyakinsa duka.

25 Ya yi bagaden ƙona turare da itacen ƙirya, tsawonsa kamu ɗaya, fāɗinsa kamu ɗaya, shi murabba'i ne, tsayinsa kuma kamu biyu ne, zankayensa kuwa a haɗe suke da shi.

26 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, da bisansa, da kewayen gyaffansa, da zankayensa. Ya kewaye shi kuma da dajiya ta zinariya.

27 Ya sa masa ƙawane biyu na zinariya a gyaffansa a ƙarkashin dajiya daura da juna don a zura sandunan ɗaukarsa.

28 Ya kuma yi sanduna biyu da itacen ƙirya, sa'an nan ya dalaye su da zinariya.

29 Ya yi tsattsarkan mai na keɓewa da kuma turare mai ƙanshi yadda mai yin turare yakan yi.

38

1 Ya kuma yi bagaden ƙona hadaya da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyar, fāɗinsa kamu biyar, murabba'i ke nan, tsayinsa kuwa kamu uku.

2 Ya yi masa zankaye a kusurwoyinsa huɗu. Zankayen a haɗe suke da shi. Ya dalaye bagaden da tagulla.

3 Da tagulla ya yi duk kayayyakin bagaden, da kwanoni, da babban cokali, da daruna, da cokula masu yatsotsi, da farantan wuta.

4 Ya yi wa bagaden raga da tagulla, ya sa ta a tsakiya.

5 Ya sa ƙawane huɗu a kusurwoyi huɗu na ragar tagulla don zura sanduna.

6 Ya kuma yi sanduna da itacen ƙirya, ya dalaye su da tagulla.

7 Sai ya zura sandunan cikin ƙawane na gyaffan bagaden don ɗaukarsa. Ya yi bagaden da itace sa'an nan ya robe cikinsa.

8 Ya yi daron wanka da tagulla, da gammonsa na tagulla, daga madubai na mata masu yin aiki a ƙofar alfarwa ta sujada.

9 Ya kuma yi farfajiya. Ya yi labulenta na gefen kudu da lallausan zaren lilin, tsawonsu kamu ɗari ne.

10 Da tagulla aka yi dirkokinsa ashirin, da kwasfan dirkoki guda ashirin, amma da azurfa aka yi maratayan dirkoki da maɗaurai.

11 Tsawon labule na wajen gefen arewa kamu ɗari ne. An yi dirkokinsa guda ashirin da kwasfansu ashirin da tagulla, amma an yi maratayan dirkoki da maɗaurai da azurfa.

12 Labule na gefen yamma kamu hamsin ne, dirkokinsa kuwa guda goma ne, da kwasfansu guda goma. An yi maratayan dirkoki, da maɗaurai da azurfa.

13 Tsawon gefen gabas kamu hamsin ne.

14 Labule na gefe ɗaya na ƙofar, kamu goma sha biyar ne, da dirkokinsu guda uku da kwasfan dirkoki guda uku.

15 Akwai kuma labule mai kamu goma sha biyar a gefe biyu na ƙofar farfajiyar. Labulen yana da dirkoki guda uku da kwasfan dirkoki guda uku.

16 Duk labulen da yake kewaye da farfajiya an yi shi da lallausan zaren lilin.

17 An yi kwasfan dirkoki duka da tagulla, amma maratayan dirkoki da maɗauransu an yi su da azurfa. An dalaye kawunansu da azurfa. Dirkokin farfajiya duka suna da maɗaurai na azurfa.

18 An yi wa labulen ƙofar farfajiya ado na ɗinki da na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin. Tsawonsa kamu ashirin, tsayinsa kamu biyar daidai da labulen farfajiya.

19 An yi dirkokin labulen guda huɗu, da kwasfan dirkoki guda huɗu da tagulla, amma da azurfa aka yi maratayan dirkokin. An dalaye kawunansu da maɗauransu da azurfa.

20 An yi turakun alfarwa ta sujada da na farfajiya duka da tagulla.

21 Wannan shi ne lissafin abubuwan da aka yi alfarwa ta sujada da su, yadda aka lasafta bisa ga umarnin Musa domin aikin Lawiyawa a ƙarƙashin jagorar Itamar, ɗan Haruna firist.

22 Sai Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza, ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa.

23 Tare da shi kuma ga Oholiyab ɗan Ahisamak na kabilar Dan, gwani ne cikin aikin zāne-zāne, da ɗinki na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin.

24 Dukan zinariya da aka yi aikace-aikacen da ita na alfarwa ta sujada sadaka ce talanti ashirin da tara ne da shekel ɗari bakwai da talatin bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi.

25 Azurfar da aka samu daga ƙidayar taron jama'a talanti ɗari ne, da shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai da saba'in da biyar (1,775) bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi.

26 Kowane mutum da aka ƙidaya ya ba da rabin shekel. Duk mai shekara ashirin ko fi an ƙidaya shi, aka sami maza dubu ɗari shida da dubu uku da ɗari biyar da hamsin (603,550).

27 An mori azurfa talanti ɗari don yin kwasfa na alfarwa, da kwasfa na labule. An yi kwasfa ɗari da azurfa talanti ɗari, wato kwasfa ɗaya talanti ɗaya ke nan.

28 An yi maratayan dirkoki da azurfa shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai da saba'in da biyar (1,775), sa'an nan an dalaye kawunansu, an kuma yi musu maɗaurai.

29 Tagullar da aka bayar kuwa, talanti saba'in da shekel dubu biyu da ɗari huɗu (2,400).

30 Da tagullar ce ya yi kwasfan ƙofar alfarwa ta sujada, da bagade, da ragarsa, da dukan kayayyakin bagaden.

31 Da tagullar kuma aka yi kwasfan farfajiya, da kwasfan ƙofar farfajiya, da dukan turakun alfarwar da na farfajiyar.

39

1 An yi wa firistoci tufafi masu kyau na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, domin yin aiki a Wuri Mai Tsarki. Suka yi wa Haruna tsarkakan tufafi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

2 Ya yi falmaran da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin.

3 An kuma buga zinariya fake-fake, suka yanyanka ta zare-zare don su yi saƙa da ita tare da zane na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan lilin, aikin gwani mai fasaha.

4 Suka yi wa falmaran kafaɗu, sa'an nan suka haɗa su a gefenta biyu na sama.

5 Gwanin masaƙi ya saƙa abin ɗamarar falmaran. Da irin kayan da aka saƙa falmaran ne aka saƙa abin ɗamarar, wato da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da zaren lallausan lilin kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

6 Sai aka gyaggyarta duwatsu masu daraja aka jera su cikin tsaiko na zinariya. Aka zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a kan duwatsun kamar yadda akan yi hatimi.

7 Aka sa su a kan kafaɗun falmaran don su zama duwatsun tunawa da Isra'ila kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

8 Aka kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji da gwaninta kamar yadda aka yi wa falmaran aiki da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin.

9 Ƙyallen maƙalawa a ƙirji murabba'i ne, aka ninka shi biyu, tsawonsa da fāɗinsa kamu ɗaya ɗaya ne.

10 Sai suka sa jeri huɗu na duwatsu masu daraja a bisansa. A jeri na fari aka sa yakutu, da tofaz, da zumurrudu.

11 A jeri na biyu aka sa turkos, da saffir, da daimon.

12 A jeri na uku aka sa yakinta, da idon mage, da ametis.

13 A jeri na huɗu aka sa beril, da onis, da yasfa. Aka sa su cikin tsaiko na zinariya.

14 An zana sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu a kan duwatsu masu daraja kamar yadda akan yi hatimi.

15 Sai suka yi tukakkun sarƙoƙi na zinariya tsantsa a kan ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

16 Suka yi tsaiko biyu na zinariya da ƙawane biyu na zinariya. Sai suka sa ƙawanen nan biyu a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

17 Suka kuma zura sarƙoƙin nan biyu na zinariya a ƙawanen nan biyu na zinariya na gyaffan ƙyallen maƙalawa a ƙirji.

18 Sai suka maƙala waɗancan bakin sarƙoƙin zinariya a tsaikon nan biyu, sa'an nan suka rataya su a kafaɗun falmaran daga gaba.

19 Suka kuma yi ƙawane biyu na zinariya, suka sa su a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji daga ciki kusa da falmaran.

20 Suka yi waɗansu ƙawane biyu na zinariya, suka maƙala su daga ƙasa a gaban kafaɗu biyu na falmaran kusa da mahaɗin a bisa abin ɗamarar falmaran.

21 Sai suka ɗaure ƙawanen ƙyallen maƙalawa a ƙirjin a ƙawanen falmaran da shuɗiyar igiya don ƙyallen maƙalawa a ƙirji ya kwanta lif a bisa kan abin ɗamarar falmaran don kada ya kwance daga falmaran, sun yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

22 Ya kuma saƙa taguwa ta falmaran da shuɗi duka.

23 An yi wa taguwar wuyan wundi kamar sulke, aka daje wuyan don kada ya kece.

24 A karbun taguwar, suka yi fasalin 'ya'yan rumman da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin.

25 Suka kuma yi ƙararrawa da zinariya tsantsa, suka sa su a tsakankanin fasalin 'ya'yan rumman kewaye da karbun taguwa.

26 An jera su bi da bi, wato fasalin rumman yana biye da ƙararrawa. Haka aka jera su kewaye da karbun taguwar yin aiki, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

27 Suka saƙa zilaika da lallausan zaren lilin don Haruna da 'ya'yansa.

28 Suka kuma yi rawani, da huluna, da mukurai da lallausan lilin.

29 Sun kuma yi abin ɗamara da lallausan lilin mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. Aka yi mata ɗinkin ado kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

30 Suka yi allo tsattsarka da zinariya tsantsa suka zāna rubutu irin na hatimi a kansa haka, “MAI TSARKI GA UBANGIJI.”

31 Suka ɗaura shi da shuɗiyar igiya a gaban rawanin kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

32 Haka kuwa aka gama dukan aiki na alfarwa ta sujada. Isra'ilawa suka yi shi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

33 Sai suka kawo wa Musa alfarwa da dukan kayayyakinta, wato da maratayanta, da katakanta, da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta,

34 da murfi na fatun raguna da na awaki, da labulen,

35 da akwatin alkawari da sandunansa, da murfinsa,

36 da tebur, da kayayyakinsa duka, da gurasar ajiyewa,

37 da alkuki na zinariya tsantsa da fitilunsa da dukan kayayyakinsa, da man fitila,

38 da bagade na zinariya, da man keɓewa, da turare mai ƙanshi, da labulen ƙofar alfarwar,

39 da bagade na tagulla da ragarsa ta tagulla, da sandunansa da dukan kayayyakinsa, da daro da gammonsa,

40 da labulen farfajiya da dirkokinta, da kwasfanta, da labulen ƙofarta, da igiyoyinta, da turakunta, da dukan kayayyakin yin aiki a alfarwa ta sujada,

41 da tufafin ado na aiki a Wuri Mai Tsarki, wato tsarkakan tufafin Haruna firist, da tufafin 'ya'yansa maza don su yi aikin firistoci.

42 Isra'ilawa sun yi dukan aiki kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

43 Da Musa ya duba dukan aikin, ga shi kuwa, sun yi shi daidai, kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Musa ya sa musu albarka.

40

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa,

2 “A kan rana ta fari ga wata na fari za ka kafa alfarwa ta sujada.

3 Sai ka sa akwatin alkawari a cikinta sa'an nan ka kāre shi da labule.

4 Ka shigar da tebur ɗin, ka shirya kayayyakinsa daidai. Ka kuma shigar da alkukin, ka sa fitilu a bisansa.

5 Ka ajiye bagade na zinariya na ƙona turare a gaban akwatin alkawari, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar alfarwa.

6 Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar alfarwa ta sujada,

7 ka kuma ajiye daro tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, sa'an nan ka zuba ruwa a ciki.

8 Sai ka yi farfajiya ka kewaye wurin sa'an nan ka rataya labulen ƙofar farfajiyar.

9 “Ka ɗauki man keɓewa, ka shafa wa alfarwa da dukan abin da yake cikinta, domin ka tsarkake ta da kayayyakinta duka, za ta kuwa zama tsarkakakkiya.

10 Ka shafa wa bagade na ƙona hadaya da kayayyakinsa duka man domin ka tsarkake shi, bagaden kuma zai zama mafi tsarki.

11 Ka kuma shafa wa daron da gammonsa man keɓewa, da haka za ka tsarkake shi.

12 “Ka kuma kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar alfarwa ta sujada, ka yi musu wanka da ruwa.

13 Sa'an nan ka sa wa Haruna tufafi tsarkaka ka shafa masa man domin ka tsarkake shi ya yi mini aiki na firist.

14 Sai ka kawo 'ya'yan Haruna maza, ka kuma sa musu taguwoyi.

15 Sa'an nan ka shafa musu mai kamar yadda ka shafa wa mahaifinsu domin su yi mini aiki a matsayin firistoci. Shafa musu man zai sa su zama firistoci din din din dukan zamanansu.”

16 Haka kuwa Musa ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarce shi.

17 A rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu, aka kafa alfarwa.

18 Sai musa ya kafa alfarwa, ya kafa kwasfanta, ya jera katakanta, ya sa mata sandunanta, ya kakkafa dirkokinta.

19 Sa'an nan ya shimfiɗa murfi a bisa alfarwa ya rufe alfarwar kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

20 Sai ya ɗauki dokoki goma ɗin, ya sa a akwatin, ya kuma zura sandunan a ƙawanen akwatin, sa'an nan ya sa murfin a bisansa.

21 Ya kawo akwatin a cikin alfarwa, sa'an nan ya sa labulen don kāre akwatin alkawari, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

22 Musa ya sa teburin cikin alfarwa ta sujada, a wajen gefen arewa na alfarwa, a gaban labulen.

23 Sa'an nan ya jera gurasa daki-daki a bisa teburin a gaban Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

24 Ya kuma sa alkukin a cikin alfarwa ta sujada daura da teburin a wajen gefen kudu na alfarwa.

25 Ya kunna fitilun a gaban Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

26 Ya kuma sa bagade na zinariya a cikin alfarwa ta sujada daga gaban labulen.

27 Sai ya ƙona turare mai ƙanshi a bisansa kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

28 Ya sa labule a ƙofar alfarwa.

29 Ya kuma sa bagade na ƙona hadaya a ƙofar alfarwa ta sujada, sa'an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da ta gari kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

30 Ya kuma sa daro a tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, sa'an nan ya zuba ruwa a ciki don wanka.

31 A cikinsa Musa da Haruna da 'ya'yansa maza sukan wanke hannuwansu da ƙafafunsu,

32 sa'ad da suke shiga cikin alfarwa ta sujada, da sa'ad da sukan kusaci bagaden kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

33 Ya kuma yi farfajiya kewaye da alfarwa da bagaden, ya sa labulen ƙofar farfajiyar. Da haka Musa ya gama aikin.

34 Sa'an nan girgije ya rufe alfarwa ta sujada, ɗaukakar Ubangiji kuma ta cika alfarwa.

35 Musa kuwa bai iya shiga alfarwa ta sujada ba domin girgijen yana zaune a bisanta, ɗaukakar Ubangiji kuma ta cika alfarwa.

36 Cikin tafiyar Isra'ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa'ad da girgijen ya tashi daga kan alfarwa.

37 Idan girgijen bai tashi ba, su kuma ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.

38 Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan alfarwa da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra'ilawa su gani.