1

1 Ana nan sai Ubangiji ya yi magana da Yunusa, ɗan Amittai, ya ce,

2 “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka faɗakar da su, gama na ga irin muguntarsu.”

3 Amma maimakon Yunusa yă tafi, sai ya gudu daga wurin Ubangiji zuwa Tarshish. Ya tafi Yafa, nan ya sami jirgin ruwa yana gab da tashi zuwa Tarshish, ya kuwa biya kuɗinsa, ya shiga tare da masu jirgin zuwa can don yă tsere wa Ubangiji.

4 Amma Ubangiji ya aika da iska mai ƙarfi a tekun, hadirin ya tsananta ƙwarai har jirgin yana bakin farfashewa.

5 Dukan matuƙan jirgin suka firgita, sai kowannensu ya shiga roƙon allahnsa. Suka yi ta jefar da kayan da suke cikin jirgin a ruwa don su sami sauƙi. Yunusa kuwa yana can cikin jirgi, a kwance, yana ta sharar barci.

6 Can shugaban jirgin ya iske shi, ya ce masa, “Me ya sa kake barci? Tashi ka roƙi allahnka, watakila allahnka zai ji tausayinmu, yă cece mu.”

7 Matuƙan jirgin kuwa suka ce wa junansu, “To, bari mu jefa kuri'a mu gani ko alhakin wane ne ya jawo mana wannan bala'i da muke ciki.” Sai suka jefa kuri'a, kuri'ar kuwa ta fāɗa a kan Yunusa.

8 Suka ce masa, “Ka faɗa mana, laifin wane ne ya jawo mana wannan masifa? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Daga wace al'umma kake?”

9 Sai Yunusa ya ce, “Ni Ba'ibrane ne, ina bin Ubangiji Allah na Sama, wanda ya yi teku da ƙasa.”

10 Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” Sun sani ya gudu ne daga wurin Ubangiji, gama ya riga ya faɗa musu.

11 Hadirin kuwa sai ƙaruwa yake ta yi. Matuƙan jirgin kuwa suka ce masa, “Me za mu yi maka domin tekun ya lafa?”

12 Yunusa ya ce, “Sai ku ɗauke ni ku jefa ni cikin tekun, sa'an nan hadirin zai lafa. Gama na sani saboda ni ne wannan hadiri mai banrazana ya auko muku.”

13 Matuƙan jirgin kuwa suka yi ta tuƙi da iyakar ƙarfinsu don su kai gaɓa, amma suka kāsa domin hadirin yana ta ƙaruwa.

14 Suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Ya Ubangiji, muna roƙonka kada ka bar mu mu halaka saboda ran mutumin nan, kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka yi abin da ya gamshe ka.”

15 Sai suka ɗauki Yunusa suka jefa shi cikin teku, nan take teku ta lafa.

16 Sai matuƙan jirgin suka ji tsoron Ubangiji ƙwarai, har suka ba da sadaka, suka kuma yi wa'adi ga Ubangiji.

17 Ubangiji kuwa ya umarci wani babban kifi ya haɗiye Yunusa. Yunusa kuwa ya yi yini uku da dare uku a cikin cikin kifin.

2

1 Sai Yunusa ya yi addu'a ga Ubangiji Allah a cikin cikin kifin,

2 ya ce, “A cikin wahalata na yi kira gare ka, ya Ubangiji, Ka a kuwa amsa mini. Daga can cikin lahira na yi kira, Ka kuwa ji muryata.

3 Ka jefa ni cikin zurfi, Can cikin tsakiyar teku, Inda igiyoyin ruwa suka kewaye ni, Kumfa da raƙuman ruwanka suka bi ta kaina.

4 Na ce, an kore ni daga wurinka, Duk da haka zan sāke ganin Haikalinka mai tsarki.

5 Ruwa ya sha kaina, Tekun ta rufe ni ɗungum. Tsire-tsiren teku suka naɗe kaina.

6 Na tafi can ƙasa ƙarƙashin tussan duwatsu. Ƙasar da ƙofarta take rufe har abada, Amma ka fitar da ni daga cikin ramin, ya Ubangiji Allahna.

7 Sa'ad da na ji raina yana rabuwa da ni, Sai na tuna da kai, ya Ubangiji. Addu'ata kuwa ta kai gare ka a Haikalinka tsattsarka.

8 Su waɗanda suke yin sujada ga gumaka marasa amfani Sun daina yi maka biyayya.

9 Amma ni zan raira yabbai gare ka, Zan miƙa maka sadaka, Zan cika wa'adin da na yi. Ceto daga wurin Ubangiji yake.”

10 Ubangiji kuwa ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunusa a gaɓar teku.

3

1 Ubangiji kuma ya sāke ce wa Yunusa,

2 “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi musu shelar saƙon da zan faɗa maka.”

3 Sai Yunusa ya tashi ya tafi Nineba kamar yadda Ubangiji ya faɗa masa. Nineba kuwa babban birni ne. Zai kai mutum tafiyar kwana uku kafin yă ƙure birnin.

4 Sai Yunusa ya kama tafiya yana ratsa birnin, da ya yi tafiyar yini guda, sai ya yi shela ya ce, “Nan da kwana arba'in za a hallaka Nineba.”

5 Sai mutanen Nineba suka gaskata Allah, suka tsai da shawara, cewa kowa da kowa ya yi azumi. Dukan mutane kuwa babba da yaro, suka sa tufafin makoki.

6 Sa'ad da Sarkin Nineba ya ji labarin, sai ya sauka daga kursiyinsa, ya tuɓe rigarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.

7 Sai ya aika wa mutanen Nineba da sanarwa cewa, “Wannan doka ce daga sarki da majalisarsa. Kada kowa ya ci wani abu, mutane, da shanu, da tumaki, da awaki duka, kada kowa ya ci, ko ya sha ruwa.

8 Sai dukan mutane da dabbobi su sa tufafin makoki. Kowa ya roƙi Allah da gaske, kowa kuma ya bar mugayen ayyukan da yake yi.

9 Kila Allah zai dakatar da nufinsa, fushinsa ya huce, ya bar mu mu tsira daga mutuwa!”

10 Allah kuwa ya ga abin da suka yi, ya ga yadda suka bar mugayen ayyukansu, sai ya dakatar da nufinsa, bai hallaka su ba.

4

1 Zuciyar Yunusa ta ɓaci ƙwarai a kan wannan abu, har ya yi fushi.

2 Saboda haka ya yi addu'a ga Ubangiji ya ce, “Ina roƙonka, ya Ubangiji, ashe, dā ma can ban faɗa ba, kafin in bar gida, cewa irin abin da za ka yi ke nan? Ai, dalilin da ya sa na yi iyakar ƙoƙarina in gudu zuwa Tarshish ke nan. Na sani kai mai taushin hali ne, mai jinƙai, mai haƙuri. Kai kullum mai alheri ne, a shirye kake kuma ka dakatar da nufinka na yin hukunci.

3 Domin haka fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka ɗauki raina, gama yanzu gara in mutu da in zauna da rai.”

4 Ubangiji kuwa ya amsa ya ce, “Daidai ne ka yi fushi?”

5 Yunusa ya fita daga birnin, ya yi wajen gabas, ya zauna. Ya yi wa kansa rumfa, ya zauna a inuwarta, yana jira ya ga abin da zai sami birnin.

6 Sai Ubangiji ya sa wata 'yar kuranga ta tsiro ta yi girma a inda Yunusa yake, don ta inuwantar da shi, ya ji daɗi. Yunusa kuwa ya yi murna da wannan 'yar kuranga ƙwarai.

7 Amma kashegari da fitowar rana, sai Allah ya sa tsutsa ta cinye 'yar kurangar har ta mutu.

8 A sa'ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro. Yunusa ya ji kamar zai suma saboda zafin rana da take bugun kansa. Sai ya so ya mutu, ya ce, “Gara in mutu da ina zaune da rai.”

9 Amma Allah ya ce masa, “Daidai ne ka yi fushi saboda 'yar kurangar?” Yunusa ya amsa, “Hakika, daidai ne a gare ni in yi fushi, har ma in yi fushin da ya isa in mutu!”

10 Ubangiji kuma ya amsa, ya ce masa, “Ai, wannan 'yar kurangar dare ɗaya ta girma, kashegari kuma ta mutu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓaci saboda ita!

11 Ashe, dole ne ni kuma in ji tausayin Nineba, babban birni mai 'yan yara fiye da dubu ɗari da dubu ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa.”