1 Ubangiji kuwa ya yi magana da Yusha'u ɗan Beyeri a zamanin mulkin Azariya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuza, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yehowash, Sarkin Isra'ila.
2 Sa'ad da Ubangiji ya fara yin magana da Yusha'u ya ce masa, “Tafi ka auro karuwa, ka haifi 'ya'yan karuwanci, gama ƙasar tana yin fasikanci sosai, wato ta bar bin Ubangiji.”
3 Sai ya tafi ya auri Gomer, 'yar Diblayim. Ta yi ciki, ta haifi masa ɗa namiji.
4 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Yezreyel, gama ba da daɗewa ba zan ziyarci gidan Yehu da hukunci saboda jinin da ya zubar a Yezreyel. Zan sa mulkin Isra'ila ya ƙare.
5 A wannan rana zan karya bakan Isra'ila a kwarin Yezreyel.”
6 Gomer ta kuma ɗauki ciki, ta haifi 'ya mace. Ubangiji kuma ya ce wa Yusha'u, “Ka raɗa mata suna Bajinƙai, gama ba zan ƙara yi wa jama'ar Isra'ila jinƙai ba, har da zan gafarta mata.
7 Amma zan yi wa mutanen Yahuza jinƙai. Ni kaina zan cece su ba da baka ba, ba kuwa da takobi, ko da yaƙi, ka da dawakai, ko da sojojin dawakai ba.”
8 Sa'ad da ta yaye Ba-jinƙai, ta sāke ɗaukar ciki, ta haifi ɗa namiji.
9 Ubangiji kuma ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Ba-mutanena-ba-ne, gama ku ba mutanena ba ne,ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 “Duk da haka yawan mutanen Isra'ila Zai zama kamar yashi a bakin teku, Wanda ba za a iya aunawa ko ƙidayawa ba. Maimakon kuma a ce, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ Za a ce, ‘Ku mutanen Allah ne mai rai.’
11 Mutanen Yahuza da mutanen Isra'ila za su haɗu su zama ɗaya, Za su zaɓa wa kansu shugaba ɗaya. Za su shugabanci ƙasar Gama ranar Yezreyel babba ce.”
1 “Ka ce wa 'yan'uwanka maza, ‘Ku mutanena ne,’ ka kuma ce wa 'yar'uwarka, ‘Kin sami jinƙai!’
2 Ku roƙi uwarku, Gama ita ba matata ba ce, Ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta ta daina karuwancinta, Ta rabu da masu rungumar mamanta.
3 In ba haka ba, sai in yi mata tsiraici, In bar ta kamar ran da aka haife ta. In maishe ta kamar jeji, In bar ta kamar busasshiyar ƙasa, In kashe ta da ƙishi.
4 Ba zan yi wa 'ya'yanta jinƙai ba, Domin su 'ya'yan karuwanci ne
5 Gama uwarsu ta yi karuwanci. Ita wadda ta haife su ta yi abin kunya. Gama ta ce, ‘Zan bi samarina Waɗanda suke ba ni ci da sha, Da ulu, da lilin, da mai, da ruwan inabi.’
6 “Don haka zan shinge hanyarta da ƙaya, Zan gina mata garu don kada ta sami hanyar fita.
7 Za ta bi samarinta, amma ba za ta tarar da su ba. Za ta neme su, amma ba za ta same su ba. Sa'an nan za ta ce, ‘Zan koma wurin mijina na fari, Gama zamana na dā ya fi na yanzu!’
8 “Amma ba ta sani ni nake ba ta hatsi, da ruwan inabi, da mai, Da azurfa, da zinariya da yawa Waɗanda suka bauta wa gunkin nan Ba'al da su ba.
9 Don haka zan hana mata hatsi a kakarsa, Da ruwan inabi a kakarsa, da kuma ulu da lilin Waɗanda suka zama abin rufe tsiraicinta.
10 Yanzu zan buɗe tsiraicinta A idon samarinta, Ba kuwa wanda zai cece ta daga hannuna.
11 Zan sa ta daina farin cikinta, Da idodinta, da kiyaye lokatan amaryar wata, Da hutawar ranar Asabar, Da ƙayyadaddun idodinta.
12 Zan ɓata inabinta da itatuwan ɓaure Waɗanda take cewa, ‘Waɗannan su ne hakkina Wanda samarina suka ba ni.’ Zan sa su zama kurmi, Namomin jeji su cinye su.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin idodin gunkin nan Ba'al. A kwanakin nan takan ƙona musu turare, Ta yi ado da zobe da lu'ulu'ai, Ta bi samarinta, amma ta manta da ni.” In ji Ubangiji.
14 “Don haka, ga shi, zan rarrashe ta, In kai ta cikin jeji, In ba ta magana.
15 Can zan ba ta gonar inabi, In mai da kwarin Akor, wato wahala, ƙofar bege. A can za ta amsa mini kamar a kwanakin ƙuruciyarta, Kamar lokacin da ta fito daga ƙasar Masar.
16 Ni Ubangiji na ce, a waccan rana Za ta ce da ni, ‘Mijina,’ ba za ta ƙara ce da ni Ba'al ba.
17 Zan kawar da sunayen Ba'al daga bakinta. Ba za a ƙara kiransu da sunayensu ba.
18 “A waccan rana zan yi alkawari Da namomin jeji, da tsuntsaye, Da abubuwa masu rarrafe saboda Isra'ila. Zan kuma kakkarya baka da takobi, In kuma sa yaƙi ya ƙare a ƙasar, Sa'an nan za su yi zamansu lami lafiya.
19 Zan ɗaura auren da yake cikin adalci, Da bisa kan ka'ida, da ƙauna.
20 Zan ɗaura auren da yake cikin aminci, Za ki kuwa sani, ni ne Ubangiji.
21 “A waccan rana, zan amsa wa sammai, Su kuma za su amsa wa ƙasa.
22 Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, da ruwan inabi, da mai, Su ma za su amsa wa Yezreyel.
23 Zan dasa ta a ƙasa domin kaina. Zan kuma yi wa ‘Ba-jinƙai,’ jinƙai, In kuma ce wa ‘Ba-mutanena ba,’ ‘Mutanena!’ Su ma za su ce, ‘Kai ne Allahna!’ ”
1 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka sāke tafiya, ka ƙaunaci karuwa wadda take tare da kwartonta. Ka ƙaunace ta kamar yadda ni Ubangiji nake ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da yake suna bin gumaka, suna ƙaunar wainar zabibi da aka miƙa wa gumaka.”
2 Sai na ba da sadakinta a bakin tsabar azurfa goma sha biyar, da buhu biyu na sha'ir.
3 Sa'an nan na ce mata, “Ki keɓe kanki kwanaki da yawa domina, kada ki yi kwartanci, ki kwana da wani, ni kuma ba zan shiga wurinki ba.”
4 Gama mutanen Isra'ila za su zauna kwanaki da yawa ba sarki, ba shugaba, ba sadaka, ba al'amudi, ba falmaran, ba kan gida.
5 Bayan wannan mutanen Isra'ila za su komo su nemi Ubangiji Allahnsu, da Dawuda, sarkinsu. Da tsoro za su komo zuwa wurin Ubangiji domin alheransa a kwanaki na ƙarshe.
1 Ya ku mutanen Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji, Gama Ubangiji yana da shari'a da ku, ku mazaunan ƙasar. “Gama ba gaskiya, ko ƙauna, Ko sanin Ubangiji a ƙasar.
2 Akwai rantsuwa, da ƙarya, da kisankai, da sata, da zina, Da kama-karya, da zub da jini a kai a kai.
3 Saboda haka ƙasar za ta yi makoki, Dukan waɗanda yake zaune a cikinta za su yi yaushi. Namomin jeji kuma, da tsuntsaye, da kifaye za su ƙare.
4 “Duk da haka kada wani ya sa wa mutum laifi, Kada wani kuma ya tsautar. Da ku nake magana, ku firistoci.
5 Za ku yi tuntuɓe da rana, Annabi kuma zai yi tuntuɓe tare da kai da dare, Ni kuwa zan hallaka mahaifiyarku.
6 Mutanena sun lalace saboda jahilci. Tun da yake sun ƙi ilimi, Ni ma na ƙi ku da zaman firist ɗina. Tun da yake kun manta da umarnan Allahnka, Ni ma zan manta da 'ya'yanku.
7 “Yawan ƙaruwar firistoci, yawan ƙaruwar zunubi. Zan sāke darajarsu ta zama kunya.
8 Suna ciyar da kansu da zunubin mutanena, Suna haɗamar ribar muguntarsu.
9 Kamar yadda mutane suke, haka firistocin suke, Zan hukunta su saboda al'amuransu, Zan sāka musu gwargwadon ayyukansu.
10 Za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Za su yi karuwanci, amma ba za su ƙaru ba. Gama sun rabu da Ubangiji don su bauta wa gumaka.
11 “Karuwanci, da ruwan inabi, Da ruwan inabin da bai sa hauka ba sukan kawar da hankali.
12 Mutanena sukan yi tambaya a wurin abin da aka yi da itace, Sandansu yakan faɗa musu gaiɓu, Gama ruhun karuwanci ya ɓad da su, Sun rabu da Allahnsu don su yi karuwanci.
13 Suna miƙa sadaka a bisa ƙwanƙolin duwatsu. Suna yin hadaya a bisa tuddai, Da kuma a gindin itacen oak, da aduruku, da katambiri, Domin suna da inuwa mai kyau. Don haka 'ya'yanku mata suke karuwanci, Surukanku mata suke yin zina.
14 Ba zan hukunta 'ya'yanku mata sa'ad da suka yi karuwanci ba, Ko kuwa surukanku mata sa'ad da suka yi zina ba, Gama mazan da kansu sukan shiga wurin karuwai. Sukan miƙa sadaka tare da karuwai a Haikali, Mutane marasa fahimi za su lalace.
15 “Ko da yake mutanen Isra'ila suna karuwanci, Kada kuma mutanen Yahuza su yi laifi. Kada ku tafi Gilgal, Ko ku haura zuwa Bet-awen. Kada ku yi rantsuwa da cewa, ‘Har da zatin Ubangiji!’
16 Mutanen Isra'ila masu taurinkai ne kamar alfadari. Ta yaya Ubangiji zai yi kiwonsu Kamar 'ya'yan tumaki a makiyaya mai fāɗi?
17 Mutanen Ifraimu sun haɗa kai da gumaka, Sai a rabu da su.
18 Su taron mashaya ne kawai, Karuwai ne kuma. Suna ƙaunar abin kunya.
19 Iska ta ƙunshe su cikin fikafikanta. Za su ji kunyar bagadansu.”
1 “Ku ji wannan, ya ku firistoci! Ku saurara, ya mutanen Isra'ila! Ku kasa kunne, ya gidan sarki! Gama za a yi muku hukunci, Domin kun zama tarko a Mizfa, Da ragar da aka shimfiɗa a bisa Tabor.
2 Sun tayar, sun yi zurfi cikin zunubi, Zan hore su duka.
3 Na san Ifraimu, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. Gama Ifraimu ta yi aikin karuwanci, Isra'ila kuma ta ƙazantu.
4 “Ayyukansu ba su bar su Su koma wurin Allahnsu ba, Gama halin karuwanci yana cikinsu, Don haka kuma ba su san Ubangiji ba.
5 Girmankan mutanen Isra'ila yana ba da shaida a kansu. Mutanen Ifraimu za su yi tuntuɓe cikin laifinsu. Mutanen Yahuza kuma za su yi tuntuɓe tare da su.
6 Da garkunan tumaki da na awaki, da na shanunsu Za su tafi neman Ubangiji, Amma ba za su same shi ba, Gama ya rabu da su.
7 Sun ci amanar Ubangiji. Su haifi shegu. Yanzu amaryar wata za ta cinye su da gonakinsu.
8 “Ku busa ƙaho cikin Gibeya, Ku busa kakaki cikin Rama, Ku yi gangami cikin Bet-awen, Ku yi rawar yaƙi, ya ku Biliyaminu!
9 Ifraimu za ta zama kango a ranar hukunci. A kabilan Isra'ila na sanar da abin da zai faru, ba makawa.
10 “Shugabannin Yahuza sun zama kamar masu cin iyaka, Zan zubo musu da fushina kamar ruwa.
11 An danne Ifraimu, shari'a ta murƙushe ta, Domin ta ƙudura ta bi banza.
12 Domin haka na zama kamar asu ga Ifraimu, Kamar ruɓa ga mutanen Yahuza.
13 “Sa'ad da Ifraimu ta ga ciwonta, Yahuza kuma ta ga rauninta, Sai Ifraimu ta aika zuwa Assuriya, Wurin babban sarki. Amman ba zai iya warkar da ciwonki, ko rauninki ba.
14 Zan zama kamar zaki ga Ifraimu, Kamar sagarin zaki ga mutanen Yahuza. Ni kaina zan yayyage, in yi tafiyata. Zan ɗauka, in tafi, ba wanda zai yi ceto.
15 “Zan koma wurin zamana Sai lokacin da suka yarda sun yi zunubi, su neme ni. A cikin ƙuncinsu za su neme ni.”
1 Mutane sun ce, “Zo, mu koma wurin Ubangiji, Gama shi ne ya yayyaga, Shi ne kuma zai warkar. Shi ne ya yi mana rauni, Shi ne kuma zai ɗaure raunin da maɗauri.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu. A rana ta uku kuwa zai tashe mu Mu yi zammanmu a gabansa.
3 Mu nace domin mu san Ubangiji Zuwansa tabbatacce ne kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, Kamar ruwan bazara da yake shayar da ƙasa.”
4 Ubangiji ya ce, “Me zan yi da ke, ya Ifraimu? Me zan yi da ke, ya Yahuza? Ƙaunarku tana kama da ƙāsashi, Kamar kuma raɓar da take watsewa da wuri.
5 Domin haka na sassare su ta wurin annabawansu, Na karkashe su da maganar bakina. Hukuntaina suna kama da hasken da yake ketowa.
6 Gama ƙauna nake so, ba sadaka ba, Sanin Allah kuma fiye da hadayu na ƙonawa.
7 “Amma sun ta da alkawarina kamar Adamu, Sun ci amanata.
8 Gileyad gari ne na masu aikata mugunta. Tana da tabban jini.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, Haka nan firistoci suka haɗa kansu Don su yi kisankai a hanyar Shekem, Ai, sun aikata mugayen abubuwa.
10 Na ga abin banƙyama a cikin Isra'ila, Karuwancin Ifraimu yana wurin, Isra'ila ta ƙazantar da kanta.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuza, an shirya muku ranar girbi, A lokacin da zan mayar wa mutanena da dukiyarsu.”
1 “Sa'ad da zan warkar da mutanen Isra'ila, Sai zunubin Ifraimu da muguntar Samariya su bayyana, Gama suna cin amana. Ɓarawo yakan fasa, ya shiga, 'Yan fashi suna fashi a fili,
2 Amma ba su tunani, Cewa zan tuna da dukan muguntarsu. Yanzu ayyukansu sun kewaye su, Ina ganinsu.
3 “Suna faranta zuciyar sarki da muguntarsu, Na shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
4 Dukansu mazinata ne, Suna kama da tanda da aka zafafa, Wadda matoyi ya daina iza mata wuta, Tun daga lokacin cuɗe kullu Har zuwa lokacin da yisti ya tasar da shi.
5 A ranar bikin sarki, Sukan sa sarki da shugabanni su bugu da ruwan inabi. Yakan yi cuɗanya da shakiyai.
6 Zukatansu suna ƙuna da ƙullaƙulle kamar tanderu. Fushinsu na ci dare farai, Da safe fushinsu yana ci bal-bal kamar harshen wuta.
7 “Dukansu suna da zafi kamar tanderu. Suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sun faɗi. Ba wanda ya kawo mini kuka.”
8 Ubangiji ya ce, “Mutanen Ifraimu sun haɗa kansu da al'ummai, Sun zama kamar wainar da ba a juya ba.
9 Baƙi sun cinye ƙarfinsu, su kuwa ba su sani ba, Furfura ta faso musu, amma ba su sani ba.
10 Girmankan mutanen Isra'ila ya kai ƙararsu, Duk da haka ba wanda ya komo wurin Ubangiji Allahnsu, Ba su kuwa neme shi ba.
11 Ifraimu kamar kurciya take, marar wayo, marar hankali, Takan tafi Masar da Assuriya neman taimako.
12 Lokacin da suke tafiya, zan shimfiɗa musu ragata, Zan saukar da su ƙasa kamar yadda akan yi wa tsuntsun da yake tashi sama. Zan hukunta su saboda mugayen ayyukansu.
13 “Tasu ta ƙare, gama sun ratse, sun rabu da ni. Halaka za ta auka musu domin sun tayar mini. Ko da yake zan cece su, duk da haka suna faɗar karya a kaina.
14 Ba su yi kuka gare ni da zuciya ɗaya ba, Sa'ad da suke kuka a gadajensu, Sun tsattsaga jikinsu domin abinci da ruwan inabi. Sun yi mini tawaye.
15 Ko da yake na horar da su, na ƙarfafa damatsansu, Duk da haka suna shirya mini maƙarƙashiya.
16 Sun juya mini baya, suna bin gunkin nan Ba'al. Suna kama da tankwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi Saboda maganganunsu na fariya. Za su zama abin ba'a a ƙasar Masar.”
1 Ubangiji ya ce, “Ki sa ƙaho a bakinki, Kamar gaggafa, haka maƙiyi ya kawo sura a kan ƙasar Ubangiji, Domin mutanena sun ta da alkawarina, Sun kuma keta dokokina.
2 Sun yi kuka a wurina, Suna cewa, ‘Ya Allah, mu Isra'ila mun san ka!’
3 Isra'ila ta ƙi abin da yake mai kyau, Don haka abokan gāba sun fafare ta.
4 “Suna naɗa sarakuna, amma ba da iznina ba. Suna naɗa shugabanni amma ba da yardata ba. Suna ƙera gumaka da azurfarsu da zinariyarsu, Wannan kuwa zai zama sanadin halakarsu.
5 Ya mutanen Samariya, ina ƙin maraƙinku na siffa. Ina jin haushinsu ƙwarai! Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 Ai, mai aikin hannu ne ya yi shi a Isra'ila! Gunki ne ba Allah ba ne. Za a farfashe siffar maraƙin Samariya.
7 Gama sun shuka iska Don haka zu su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da zangarniya, Ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci,
8 Isra'ila kamar kowace al'umma ce. Suna cikin al'ummai Kamar kaskon da ba shi da amfani,
9 Gama sun haura zuwa Assuriya, Kamar jakin jeji da yake yawo shi kaɗai. Mutanen Ifraimu sun yi ijara da abokan tsafinsu.
10 Ko da yake sun yi ijara da abokai daga cikin al'ummai, Yanzu zan tattara su, in hukunta su. Sa'an nan za su fara ragowa, Ta wurin tunanin nawayar Sarkin sarakuna.
11 “Da yake Ilfraimu ta yawaita bagadan zunubi, Sun zama mata bagadai na yin zunubi.
12 Ko da na rubuta mata dokokina sau da yawo, Za ta ɗauke su wani baƙon abu ne kawai.
13 Suna jin daɗin miƙa hadayu don cin naman, Amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Ubangiji zai tuna da muguntarsu, Zai hukunta su saboda zunubansu. Za su koma Masar.
14 “Gama mutanen Isra'ila sun manta da Mahaliccinsu, Sai sun gina manyan gidaje masu daraja. Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu, Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu, Ta ƙone fādodinsu.”
1 Kada ku yi farin cikin, ya mutanen Isra'ila! Kada ku yi murna kamar sauran mutane! Gama kun yi karuwanci, kun rabu da Allahnku. Kuna ƙaunar ijarar karuwanci a kowane masussuka.
2 Masussuka da wurin matsa ruwan inabi ba za su ciyar da su ba. Sabon ruwan inabi kuma ba zai ishe su ba.
3 Ba za su zauna a ƙasar Ubangiji ba, Amma mutanen Ifraimu za su koma Masar. Za su ci haramtaccen abinci a Assuriya.
4 Ba za su yi wa Ubangiji hadaya ta sha ba. Ba za su faranta zuciyarsa da sadakoki ba. Abincinsu zai zama irin na masu makoki. Duk wanda ya ci shi zai haramta. Gama abincinsu zai yi musu maganin yunwa ne kawai, Ba za su kai shi Haikalin Ubangiji ba.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar idi? Da a ranar idin Ubangiji?
6 Ga shi kuma, suna tafiya zuwa halaka, Masar za ta tattara su, Memfis za ta binne su. Ƙayayuwa za su mallaki abubuwan tamaninsu na azurfa. Sarƙaƙƙiya za ta tsiro a cikin alfarwansu.
7 Ranar hukunci ta zo, ranar ramako ta iso, Isra'ila za ta sani! An ce annabi wawa ne, Mutumin da yake da ruhu kuwa mahaukaci ne, Saboda yawan muguntarku da ƙiyayyarku.
8 Ifraimu mai tsaro ne a gaban Allahna, annabi kuwa, Duk da haka sun zama kamar mai kafa tarkon kama tsuntsu, a farkon kaka. Akwai ƙiyayya a cikin Haikalin Allahnsu.
9 Sun yi zurfi cikin rashin gaskiya Kamar a kwanakin Gibeya, Ubangiji zai tuna da muguntarsu. Zai hukunta su saboda zunubansu.
10 Ubangiji ya ce, “Na iske Isra'ila a jeji kamar inabi, Na ga kakanninku kamar nunan fari na 'ya'yan ɓaure, Amma da suka zo Ba'al-feyor, sai suka keɓe kansu ga Ba'al. Suka zama abin ƙyama kamar abin da suke ƙauna.
11 Darajar Ifraimu za ta tashi kamar tsuntsu, Ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki!
12 Ko sun goyi 'ya'ya, Zan sa su mutu tun ba su balaga ba. Tasu ta ƙare sa'ad da na rabu da su!”
13 Ya Ubangiji, na ga yadda Ifraimu Ta mai da 'ya'yanta ganima Tana fitar da su zuwa wurin yanka.
14 Ya Ubangiji, me zan ce ka ba su? Me za ka ba su? Ka ba su cikin da ba ya haihuwa da busassun mama.
15 Ubangiji ya ce, “Kowace irin muguntarsu tana a Gilgal, A can na ƙi su! Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga ƙasata, Ba kuma zan ƙaunace su ba. Dukan shugabanninsu 'yan tayarwa ne.
16 An ka da mutanen Ifraimu, saiwarsu ta bushe. Ba za su yi 'ya'ya ba. Ko ma sun haihu, zan kashe 'ya'yan nan nasu waɗanda suke ƙauna.”
17 Allahna zai ƙi su Domin ba su yi masa biyayya ba. Za su zama masu yawo cikin al'ummai.
1 Isra'ila kurangar inabi ce mai bansha'awa Wadda yake ba da 'ya'ya da yawa. Ƙara yawan arzikinsu, Ƙara gina bagadansu. Ƙara yawan wadatar ƙasarsu. Ƙara kyautata ginshiƙansu.
2 Zuciyarsu ta munafunci ce, Yanzu tilas za su ɗauki hakkin laifinsu, Ubangiji zai farfashe bagadansu da ginshiƙansu.
3 Gama yanzu za su ce, “Ba mu da sarki, Domin ba mu ji tsoron Ubangiji ba. Amma me sarki zai yi mana?”
4 Surutai kawai suke yi, Suna yin alkawaran ƙarya, Don haka hukunci zai zaburo kamar muguwar ciyawa mai dafi a kunyoyin gona.
5 Mazaunan Samariya suna rawar jiki Domin ɗan maraƙin Bet-awen, Mutane za su yi makoki dominsa, Firistoci matsafa, za su yi kururuwa dominsa, Da kuma darajarsa wadda ta rabu da shi.
6 Za a kai ɗan maraƙin a Assuriya Don a biya wa sarki haraji. Za a kunyatar da Ifraimu, Isra'ila kuwa za ta ji kunya saboda shawararta.
7 Sarakunan Samariya za su ɓace, Kamar kumfa a bisa ruwa.
8 Za a hallaka masujadan tuddai na Awen inda Isra'ila suke yin zunubi, Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma a bagadansu. Za su ce wa manyan duwatsu, “Ku rufe mu!” Su ce wa tuddai, “Ku faɗo bisa kanmu!”
9 Ubangiji ya ce, “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra'ila! Tun daga wancan lokaci kuka yi ta ci gaba. Ashe, yaƙi ba zai tarshe su a Gibeya ba?
10 Zan fāɗa wa waɗannan mutane masu zunubi, in hukunta su. Za a tattara al'ummai, su yi gāba da su, Za a hukunta su saboda yawan zunubansu.
11 “Ifraimu horarriyar karsana ce, Wadda yake jin daɗin yin sussuka, Amma na sa wa kyakkyawan wuyanta karkiya, Na sa Yahuza ta ja garmar noma, Yakubu kuwa za ta ja garmar bajiya.
12 Ku shuka wa kanku adalci, Ku girbe albarkun ƙauna, Ku yi kautun saurukanku, Gama lokacin neman Ubangiji ya yi, Domin ya zo, ya koya muku adalci.
13 Kun shuka mugunta, Kun girbe rashin adalci, Kun ci amfanin ƙarya. “Da yake dogara ga hanyarku da ɗumbun sojojinku,
14 Domin haka hayaniyar yaƙi za ta tashi a tsakanin jama'arku. Dukan kagaranku za a hallaka su. Kamar yadda Shalmanesar ya hallaka Bet-arbel a ranar yaƙi. An fyaɗa uwaye da 'ya'yansu a ƙasa.
15 Haka za a yi muku, ya mutanen Betel, saboda yawan muguntarku. Da asuba za a datse Sarkin Isra'ila.”
1 “A lokacin da Isra'ila yake yaro, na ƙaunace shi, Daga cikin Masar na kirawo ɗana.
2 Yawan kiransu, yawan tayarwar da suke yi mini, Sai ƙara miƙa wa Ba'al sadaka suke yi, Suna ƙona turare ga gumaka.
3 Ko da yake ni ne na koya wa Ifraimu tafiya. Na ɗauke su a hannuna, Amma ba su sani ni ne na lura da su ba.
4 Na bishe su da linzamin alheri da ragamar ƙauna, Na zama musu kamar wanda yake ɗauke musu karkiya daga muƙamuƙansu. Na sunkuya, na ciyar da su.
5 “Ba su koma ƙasar Masar ba, Amma Assuriya za ta zama sarkinsu Gama sun ƙi yarda su koma wurina.
6 Takobi zai ragargaje biranensu, Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu, Zai cinye su domin muguwar shawararsu.
7 Mutanena sun himmantu su rabu da ni, Ko da yake an kira su ga Ubangiji, Ba wanda ya girmama shi.
8 “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu? Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra'ila? Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma? Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim? Zuciyata tana motsawa a cikina, Juyayina ya huru.
9 Ba zan aikata fushina mai zafi ba, Ba zan ƙara hallaka Ifraimu ba, Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Maitsarki wanda yake tsakiyarku, Ba zan zo wurinku da hasala ba.
10 “Za su bi Ubangiji, Zai yi ruri kamar zaki, hakika zai yi ruri 'Ya'yansa za su zo da rawar jiki da yamma.
11 Da sauri za su zo kamar tsuntsaye daga Masar, Kamar kurciyoyi daga ƙasar Assuriya, Zan komar da su gidajensu, ni Ubangiji na faɗa.”
12 Ubangiji ya ce, “Ifraimu ta kewaye ni da ƙarairayi, Jama'ar Isra'ila kuwa ta kewaye ni da munafuncinta, Yahuza kuma ta tayar wa Allah, Wato tana gāba da Mai Tsarki, mai aminci.
1 Ifraimu tana kiwon iska, Tana ta bin iskar gabas dukan yini. Tana riɓaɓɓanya ƙarya da kamakarya. Tana ƙulla yarjejeniya da Assuriya, Tana kai mai a Masar.”
2 Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza, Zai hukunta Isra'ila saboda hanyoyinta, Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta.
3 A cikin mahaifa kakansu Yakubu ya kama diddigen ɗan'uwansa, Sa'ad da ya zama baligi ya yi kokawa da Allah.
4 Ya yi kokawa da mala'ika ya yi rinjaye. Ya yi kuka, ya roƙi albarka. Ya sadu da Allah a Betel, A can Allah ya yi magana da shi.
5 Ubangiji Allah Mai Runduna, Sunansa Ubangiji,
6 Sai ku koma wurin Allahnku, Ku yi alheri, ku yi adalci, Ku saurari Allahnku kullayaumin.
7 Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda yake da ma'aunin algus a hannunsa. Yana jin daɗin yin zalunci.
8 Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai, Mun samar wa kanmu dukiya. A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’
9 Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar, Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai, Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi.
10 “Na yi magana da annabawa, Ni ne na ba da wahayi da yawa, Da misalai kuma ta wurin annabawa.
11 Idan akwai laifi a Gileyad, Hakika za su zama wofi. A Gilgal ana sadaka da bijimai, Bagadansu za su zama kamar tsibin duwatsu A gyaffan kunyoyin gona.”
12 Kakanmu Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram, A can Isra'ila ya yi barantaka saboda mace, Saboda mace ya yi kiwon tumaki.
13 Ta wurin annabi Ubangiji ya fito da mutanen Isra'ila daga Masar, Ta wurin annabi kuma ya kiyaye su.
14 Mutanen Ifraimu sun yi muguwar tsokana mai ta da fushi, Domin haka Ubangiji zai ɗora musu hakkin jini a kansu, Zai saka musu cin mutuncin da suka yi.
1 Sa'ad da Ifraimu ta yi magana, mutane suka yi rawar jiki. An ɗaukaka ta cikin Isra'ila, Amma ta yi laifi ta wurin bauta gunkin nan Ba'al, Ta kuwa mutu.
2 Har yanzu suna ta ƙara yin zunubi, Suna yi wa kansu gumaka na zubi, Da gwaninta sukan yi gumaka da azurfarsu, Dukansu aikin hannu ne. Sukan ce, “Ku miƙa wa waɗannan hadayu!” Mutane sukan sumbaci siffofin maruƙa.
3 Don haka za su zama kamar ƙāsashin da akan yi da safe, Ko kuwa kamar raɓa mai kakkaɓewa da wuri. Za su zama kamar ƙaiƙayi wanda ake shiƙarsa cikin iska a masussuka, Ko kuwa kamar hayaƙin da yake fita ta bututu.
4 Ubangiji ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku Tun daga ƙasar Masar. Banda ni ba ku san wani Allah ba, Banda ni kuma ba wani mai ceto.
5 Ni ne wanda ya san ku a cikin jeji, A ƙasar da take da ƙarancin ruwan sama.
6 Sa'ad da suka sami wurin kiwo, suka ƙoshi, Sai suka yi girmankai, Suka manta da ni.
7 Zan zama musu kamar zaki, Kamar damisa zan yi kwanto a gefen hanya.
8 Zan auka musu kamar beyar, Wadda aka ƙwace mata 'ya'ya. Zan yage ƙirjinsu, in cinye su kamar zaki, Kamar mugun naman jeji zan yayyage su.
9 “Zan hallaka ku, ya mutanen Isra'ila! Wane ne zai taimake ku?
10 Yanzu ina sarkinku da zai cece ku? Ina kuma dukan shugabanninku da za su kāre ku? Su waɗanda kuka roƙa, kun ce, ‘Ku naɗa mana sarki da shugabanni.’
11 Da fushina na naɗa muku sarki, Da hasalata kuma na tuɓe shi.
12 “An ƙunshe muguntar Ifraimu, Zunubinsa kuwa an ajiye shi a rumbu.
13 Naƙudar haihuwarsa ta zo, Amma shi wawan yaro ne, Bai fito daga mahaifar ba.
14 Zan fanshe su daga ikon lahira. Zan fanshe su daga mutuwa. Ya mutuwa, ina annobanki? Ya kabari, ina halakarka? Kan kawar da juyayi daga wurina.
15 Ko da yake Isra'ila tana bunƙasa kamar ciyayi, Iskar gabas, wato iskar da za ta zo daga jeji, Za ta busar da maɓuɓɓugarsu da idon ruwansu, Za ta lalatar da abubuwa masu amfani da yake cikin taskarsu.
16 Samariya za ta ɗauki hakkin zunubinta, Gama ta tayar wa Allahnta. Za a kashe mutanenta da takobi. Za a fyaɗa jariranta a ƙasa, A kuma tsage matanta masu ciki.”
1 Ya mutanen Isra'ila, ku komo wurin Ubangiji Allahnku, Gama zunubinku ya sa kun yi tuntuɓe.
2 Ku komo wurin Ubangiji, ku roƙe shi, Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu, Ka karɓe mu saboda alherinka, Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu.
3 Assuriya ba za ta cece mu ba, Ba kuwa za mu hau dawakai ba. Ba za mu kuma ƙara ce da aikin hannuwanmu, ‘Kai ne Allahnmu,’ ba. A wurinka ne maraya yakan sami jinƙai.”
4 Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu. Zan kuma ƙaunace su sosai, Gama fushina zai huce.
5 Zan zama kamar raɓa ga Isra'ila, Isra'ila za ta yi fure kamar lili, Saiwarta za ta shiga kamar itacen al'ul.
6 Tohonta zai buɗo, Kyanta zai zama kamar itacen zaitun, Ƙashinta kuwa kamar itacen al'ul na Lebanon.
7 Waɗanda za su komo, za su zauna a inuwarta, Za su yi noman hatsi da yawa. Za su yi fure kamar kurangar inabi. Ƙanshinsu zai zama kamar ruwan inabi na Lebanon.
8 Ya mutanen Ifraimu, me zan yi da gumaka? Ni ne wanda yake amsa muku, mai lura da ku kuma. Ni kamar itacen fir ne mai ganyaye kore shar. Daga gare ni, kuke samun 'ya'ya.”
9 Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan. Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan, Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne, Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu, Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.