1

1 Ga waƙar Sulemanu mafi daɗi.

2 Leɓunanka sun lulluɓe ni da sumba, Ƙaunarka ta fi ruwan inabi zaƙi.

3 Akwai ƙanshi kuma kewaye da kai, Jin amon sunanka yana tunasar da ni. Ba wata matar da za ta ƙi ƙaunarka.

4 Ka ɗauke ni mana, mu gudu, Ka zama sarkina, ka kai ni ɗakinka. Da yake kana nan za mu yi farin ciki, Za mu sha ruwan inabi, mu yi murna da ƙaunarki. Ya dace a ƙaunace ka!

5 Rana ta sa na zama akawala kyakkyawa. Matan Urushalima, bisa ga launi, ni ƙasa ƙasa ce, Kamar alfarwar hamada, Kamar labulen fādar Sulemanu.

6 Kada ka raina ni saboda launina, Domin rana ta dafe ni. 'Yan'uwana suna fushi da ni, Sun sa ni aiki a gonar inabi. Ba ni da zarafin da zan lura da kaina.

7 Faɗa mini, ƙaunataccena, Ina za ka kai garkenka kiwo? Ina za su huta sa'ad da rana ta take? Ina zan neme ka a cikin garkunan makiyaya?

8 Mafi kyau cikin mata, ashe, ba ki san wurin ba? Tafi, ki bi garken, Ki samar wa awakinki wurin kiwo Kusa da alfarwan makiyaya.

9 Ke ƙaunatacciyata, kina ɗauke hankalina Kamar yadda goɗiya take ɗauke hankalin ingarmun karusan Fir'auna.

10 Kitsonki yana da kyau a kumatunki, Ya sauka a wuyanki kamar lu'ulu'ai.

11 Mu kuma za mu ƙera miki sarƙar zinariya, A yi miki ado da azurfa.

12 A sa'ad da sarki yake kan kujerarsa, Yana jin daɗin ƙanshin turarena ƙwarai.

13 Ƙaunataccena yana da ƙanshin mur Lokacin da yake kwance a ƙirjina.

14 Ƙaunataccena kamar furen jeji yake Wanda yake huda a gonar inabi a En-gedi.

15 Ke kyakkyawa ce ƙwarai, kyakkyawa ce ke, ya ƙaunatacciyata, Idonki suna haskaka da ƙauna.

16 Kai kyakkyawa ne ƙwarai, ya ƙaunataccena, kana da bansha'awa. Koriyar ciyawa ita ce gadonmu.

17 Itatuwan al'ul su ne jigajigan gidanmu, Itatuwan fir su ne rufin gidan.

2

1 Ni fure ce na Sharon, Furen bi-rana na cikin kwari.

2 Kamar yadda furen bi-rana yake a cikin ƙayayuwa, Haka ƙaunatacciyata take a cikin sauran mata.

3 Kamar yadda itacen gawasa yake a cikin itatuwan jeji, Haka ƙaunataccena yake a cikin sauran maza. Da farin ciki na zauna a inuwarsa, Ina jin daɗin halinsa ƙwarai.

4 Ya kai ni babban ɗakin da ake liyafa, Ƙauna ita ce tutarsa a gare ni.

5 Ka ciyar da ni da wainar zabibi, Ka ba ni 'ya'yan gawasa in sha in wartsake! Gama na cika da sha'awarka.

6 Bari ka ta da kaina da hannun hagunka, Ka rungume ni da hannun damanka.

7 Ku 'yan matan Urushalima, Ku rantse da bareyi, da batsiyoyi, Ba za ku shiga tsakaninmu ba, Ku bar ta kurum.

8 Na ji muryar ƙaunataccena! Ya zo a guje daga kan tuddai, Ya sheƙo daga tuddai zuwa wurina.

9 Ƙaunataccena kamar barewa yake, Kamar sagarin kishimi. Ga shi can, yana tsaye a bayan katangarmu. Yana leƙe ta tagogi, Yana kallona ta cikin asabari.

10 Ƙaunataccena ya yi magana da ni. Tashi mu tafi, ƙaunatacciyata, kyakkyawa.

11 Gama lokacin sanyi ya wuce, Ruwa kuma ya ɗauke.

12 Furanni suna hudowa a itatuwa ko'ina. Lokacin raira Waƙoƙi ya yi, Lokacin da kurciyoyi suke kuka ya yi.

13 'Ya'yan ɓaure sun nuna, Tohon inabi yana ƙanshi. Tashi mu tafi, ƙaunatacciyata, kyakkyawa!

14 Ya kurciyata kina zaune a kogon dutse mai tsayi. Bari in ga fuskarki, in kuma ji muryarki, Gama muryarki tana da daɗin ji, Fuskarki kuma tana da kyan gani.

15 Ku kama mana 'yan ƙananan diloli Waɗanda suke ɓata gonakin inabi, Gama gonakin inabinmu sun yi fure.

16 Ƙaunataccena nawa ne, ni ma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin furannin bi-rana,

17 Har hurowar iskar safiya, Sa'ad da duhu ya kawu. Komo ya ƙaunataccena, yi kamar barewa, Kamar sagarin kishimi a kan duwatsu.

3

1 Ina kwance a gadona dukan dare, Ina mafarki da ƙaunataccena, Na neme shi, amma ban same shi ba. Na kira shi, amma ba amsa.

2 Bari in tashi yanzu in shiga birni, In bi titi-titi, in bi dandali-dandali, In nemi wanda raina yake ƙauna. Na neme shi, amma ban same shi ba.

3 Da matsaran da suke kai da kawowa cikin birni suka gan ni, Sai na tambaye su ko sun ga ƙaunataccena.

4 Rabuwata da matsaran ke nan, Sai na yi kaciɓis da ƙaunataccena. Na riƙe shi, ban sake shi ba, Na kai shi gidanmu, har ɗakin mahaifiyata.

5 Ku 'yan matan Urushalima, Ku rantse da bareyi da batsiyoyi, Ba za ka shiga tsakaninmu ba, Ku bar ta kurum.

6 Wane ne wannan da yake fitowa daga cikin jeji, Kamar tunnuƙewar hayaƙi cike da kayan ƙanshi iri iri na fatake?

7 Ai, duba suna ɗauke da karaga wadda aka shirya domin Sulemanu, Dakarai sittin na kewaye da karagar, Zaɓaɓɓun sojoji daga cikin Isra'ila.

8 Dukansu gwanayen yaƙi da takobi ne, gogaggu ne na aikin soja, Kowannensu yana da takobi, Suna tsaro don kada a hume su da dare.

9 Ana ɗauke da sarki Sulemanu a karagar da aka shirya da itace mafi kyau.

10 An dalaye ginshiƙanta da azurfa, An rufe ta da zane da aka yi wa ado da zinariya. An lulluɓe wurin zama da zanen shunayya. Matan Urushalima sun yi mata irin yayin da ake yi na ƙauna.

11 Matan Sihiyona, ku fito ku ga sarki Sulemanu Ya sa kambin sarauta, Wanda uwarsa ta sa masa, a ranar aurensa, A ranarsa ta murna da farin ciki.

4

1 Kyakkyawa ce ke ƙaunatacciyata. Idonki kamar na kurciya, suna haskakawa daga cikin lulluɓi. Gashinki yana zarya kamar garken awaki Da yake gangarowa daga tuddan Gileyad.

2 Haƙoranki farare fat kamar tunkiyar da aka yi mata sausaya, Aka yi mata wanka nan da nan. Ba giɓi, suna nan shar. An jera su tantsai.

3 Leɓunanki ja wur kamar kin shafa jan-baki. Maganarki tana faranta zuciya. Kumatunki suna haske bayan lulluɓi.

4 Wuyanki kamar hasumiyar Dawuda yake, kewayayye sumul sumul, Inda aka rataye garkuwoyi dubu na jarumawa.

5 Mamanki kamar bareyi biyu ne, Wato tagwayen barewa, suna kiwo cikin furen bi-rana.

6 Har iskar safiya ta huro, Duhu kuma ya kawu, Zan zauna a kan tudun mur, Wato tudun kayan ƙanshi.

7 Ke kyakkyawa ce ƙaunatacciyata, Ba wanda zai kushe ki!

8 Amaryata, ki taho daga Dutsen Lebanon, Taho daga Lebanon. Ki taho daga ƙwanƙolin Dutsen Amana, Da Dutsen Senir da Harmon, Inda zakuna da damisoshi suke zaune.

9 Kallon idonki, budurwata, amaryata, Da duwatsun da suke wuyanki Sun sace zuciyata.

10 Ƙaunarki abar murna ce, ya budurwata, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi. Ƙanshinki ya fi kowane irin turare ƙanshi.

11 Zaƙin leɓunanki kamar zuma ne, ya budurwata, A gare ni harshenki madara ne da zuma. Tufafinki suna ƙanshi kamar turaren da yake cikin Dutsen Lebanon.

12 Budurwata, amaryata, ke asirtaccen lambu ce, Lambu mai katanga, asirtacciyar maɓuɓɓuga.

13 Shuke-shuke suna girma sosai. Suna girma kamar gonar itatuwan rumman. Suna ba da 'ya'ya mafi kyau Da kayan shafe-shafe kamar su lalle da nardi.

14 Nardi, da asfaran, da kalamus, da kirfa, Da dukan itatuwan da suke ba da kayan ƙanshi, Da mur, da aloyes, da dukan turare mafi ƙanshi.

15 Maɓuɓɓugai suna ba lambun ruwa, ruwan rafuffuka suna gudu, Ƙoramu suna bulbulo ruwa daga Dutsen Lebanon.

16 Farka, ya iskar arewa. Ki hura a kan lambuna, ke iskar kudu. Iska ta cika da ƙanshi. Bari ƙaunataccena ya zo lambunsa, Ya ci 'ya'yan itatuwa mafi kyau.

5

1 Na shiga cikin lambuna, budurwata, amaryata, Ina tattara mur da ƙaro. Ina shan zuma da kakinsa. Ina shan ruwan inabi da madara kuma. Ƙaunatattuna, ku ci ku sha, har ku bugu da ƙauna!

2 Ina barci, amma zuciyata na a farke, Sai na ji ƙaunataccena yana ƙwanƙwasa ƙofa. Buɗe mini in shigo, ƙaunatacciyata, budurwata, kurciyata, Wadda ba wanda zai kushe ki. Kaina ya jiƙe da raɓa, Gashina ya yi danshi da laimar ƙāsashi.

3 Na riga na tuɓe tufafina, in sāke sa su kuma? Na wanke ƙafafuna, in sāke ɓata su?

4 Ƙaunataccena ya janye hannunsa daga ƙofa, Zuciyata kuwa tana kansa.

5 Sai na tashi don in buɗe wa ƙaunataccena, ya shigo. Hannuna sharkaf da mur, Yatsuna suna ɗiga da mur sa'ad da na kama hannun ƙofar.

6 Na buɗe wa ƙaunataccena ƙofa, amma ya riga ya tafi! Na so in ji muryarsa ƙwarai! Na neme shi, amma ban same shi ba. Na yi kiransa, amma ba amsa.

7 Matsara masu kai da kawowa cikin birni suka same ni, Suka doke ni suka yi mini rauni. Matsaran da suke kan garu suka fige gyalena.

8 Ku yi mini alkawari ku matan Urushalima, Idan kun ga ƙaunataccena, Ku faɗa masa na yi suwu saboda ƙauna.

9 Ke mafi kyau cikin mata, Ki faɗi yadda ƙaunatacce naki yake. Wane abin sha'awa take gare shi, Har da za mu yi miki alkawari?

10 Ƙaunataccena kyakkyawa ne ƙaƙƙarfa kuma, Da ƙyar a sami ɗaya irinsa a cikin dubu goma.

11 Gashin kansa dogaye ne suna zarya, Baƙi wulik kamar jikin shaya. Kansa ya fi zinariya daraja.

12 Idanunsa kamar na kurciyoyi a bakin ƙorama, Waɗanda suka yi wanka da madara suna tsaye a bakin rafi.

13 Kumatunsa kyawawa ne kamar lambu, Wanda yake cike da tsire-tsire da kayan yaji. Leɓunansa kamar furen bi-rana ne, suna bulbulo da mur.

14 Hannuwansa kyawawa ne, Saye da ƙawanen da aka yi musu ado da duwatsu masu daraja. Ƙugu nasa sumul sumul ne kamar hauren giwa da aka manne da yakutu.

15 Cinyoyinsa kamar ginshiƙan da aka yi da dutsen alabasta, Aka kafa su a cikin kwasfar zinariya. Kamanninsa kamar Dutsen Lebanon ne, Da itatuwan al'ul ɗinsa mafi kyau.

16 Bakinsa yana da daɗin sumbata, Kome nasa yana faranta mini rai. Matan Urushalima, yadda ƙaunataccena yake ke nan.

6

1 Ke mafi kyau cikin matan, Ina ƙaunatacce naki ya tafi? Wace hanya ƙaunatacce naki ya bi? Za mu taimake ki nemansa.

2 Ƙaunataccena ya tafi lambunsa inda fangulan furanninsa suke. Yana kiwon garkensa a lambun, yana tattara furannin bi-rana.

3 Ƙaunataccena nawa ne, ni kuma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin bi-rana.

4 Ƙaunatacciyata, kina kyakkyawa kamar Urushalima, Kyakkyawa kuma kamar birnin Tirza, Kina da shiga rai kamar ɗaya daga cikin biranen nan.

5 Ki daina dubana gama idanunki suna rinjayata, Gashinki yana zarya kamar garken awaki Da yake gangarowa daga tuddan Gileyad.

6 Haƙoranki farare fat kamar tunkiyar da aka yi mata sausaya Aka yi mata wanka nan da nan. Ba giɓi, suna nan shar. An jera su tantsai.

7 Kumatunki suna haske bayan lulluɓi.

8 Ina da matan aure sittin, kowace kuwa sarauniya ce, Da ƙwaraƙwarai tamanin, da 'yan mata kuwa ba a magana!

9 Amma ɗaya kaɗai nake ƙauna, Ita kyakkyawa ce kamar kurciya. Tilo ce ga mahaifiyarta, 'yar lele ce ga mahaifiyarta. Mata duk sukan dube ta, su yaba. Matan sarki da ƙwaraƙwaransa suka raira waƙa suka yabe ta.

10 Wace ce wannan, kamar ketowar alfijir? Ita kyakkyawa ce mai haske, kamar hasken rana, Ko na wata mai kashe ido.

11 Na gangara zuwa cikin itatuwan almond Domin in ga ƙananan itatuwan da suke a kwarin, Domin in ga ganyayen inabi Da furannin itatuwan rumman.

12 Ina karkaɗuwa, don kin sa in ƙosa saboda ƙauna, Kamar mai korar dawakan karusar yaƙi.

13 Komo, ki komo, ke Bashulamiya, Ki komo, ki komo domin mu ƙara dubanki. Me ya sa kuke so ku dubi Bashulamiya, Sa'ad da take taka rawar zamanin dā?

7

1 Ƙafafunki suna da kyau da takalmi, Ke mafificiyar budurwa! Tsarin cinyoyinki kamar aikin gwanin sassaƙa ne.

2 Cibinki kamar finjali ne, wanda bai taɓa rasa gaurayayyen ruwan inabi a ciki ba. Kwankwasonki kamar damin alkama ne a tsakiyar bi-rana.

3 Mamanki kamar bareyi biyu ne, wato tagwayen barewa ne.

4 Wuyanki kamar hasumiyar hauren giwa ne. Idonki kamar tafki ne cikin birnin Heshbon, Kusa da ƙofar Bat-rabbim. Hancinki kyakkyawa ne kamar hasumiyar Lebanon ta tsaron Dimashƙu.

5 Kin ɗaga kanki sama kamar Dutsen Karmel. Kitsattsen gashin kanki kamar shunayya mafi kyau ne, Yakan kama hankalin sarki.

6 Ke kyakkyawa ce ƙaunatacciyata, Kina sa ni jin daɗi a rai.

7 Kina da kyan gani kamar itacen dabino, Mamanki kamar nonnan dabino.

8 Zan hau itacen dabino in tsinko 'ya'yan. Mamanki kamar nonnan inabi suke a gare ni. Numfashinki kamar ƙanshin gawasa ne.

9 Bakinki kamar ruwan inabi mafi kyau ne. Idan haka ne bari ya bulbulo sosai zuwa ga ƙaunataccena, Ya gangara leɓunan masu barci.

10 Ni ta ƙaunataccena ce, yana bukatata.

11 Zo saurayina, bari mu tafi waje, Mu kwana a karkara.

12 Za mu tashi da sassafe, mu duba kurangun inabi, Mu ga ko sun fara tohowa, Ko furanni sun fara buɗewa. Mu ga ko itatuwan rumman sun yi fure. A can zan bayyana maka ƙaunata.

13 Za ka ji ƙanshin shuke-shuke Da na dukan 'ya'yan itatuwa masu daɗi. Na adana maka jin daɗi na dā da na yanzu, ya ƙaunataccena.

8

1 Da ma a ce kai ɗan'uwana ne, wanda mahaifiyata ta goya, Da in na gamu da kai a titi, Sai in sumbace ka, ba wanda zai kula.

2 Sai in kai ka gidan mahaifiyata, In ba ka gaurayayyen ruwan inabina wanda aka yi da rumman, ka sha.

3 In ta da kai da hannun hagunka, Ka rungume ni da hannun damanka.

4 Ku yi mini alkawari, ku matan Urushalima, Ba za ku shiga tsakaninmu ba.

5 Wace ce take zuwa daga cikin jeji, Kafaɗa da kafaɗa da ƙaunataccenta? A ƙarƙashin itacen gawasa na farkar da ke, A wurin da aka haife ki, Wurin da mahaifiyarki ta haife ki.

6 Kada ki ƙaunaci kowa sai ni, Kada ki rungume kowa sai ni. Ikon ƙauna kamar na mutuwa ne, Ƙarfin kishin ƙauna kamar na mutuwa ne. Yakan kama kamar wuta, Yakan ci kamar gagarumar wuta.

7 Kome yawan ruwa ba zai iya kashe ta ba. Ba rigyawar da za ta nutsar da ita. Duk wanda ya ce zai iya sayen ƙauna da dukiya, Ba abin da zai same shi sai tashin hankali.

8 Muna da 'yar'uwa ƙunƙuma. Me za mu yi idan wani saurayi ya ce yana sonta?

9 Da a ce ita bango ce, da mun gina mata hasumiyar azurfa. Da a ce ita ƙofa ce, da mun yi mata ƙyaure da itacen al'ul.

10 Ni bango ce, doguwa, mamana tantsai tantsai, Na sami kwarjini wurin ƙaunataccena.

11 Sulemanu yana da gonar inabi A Ba'al-hamon, wato wuri mai yawan albarka. Ya yi ijara da waɗansu zaɓaɓɓun manoma. Kowannensu yana biyansa kuɗi, azurfa dubu.

12 Ni ma ina da gonar inabi ta kaina. Kai Sulemanu zan ba ka kuɗi azurfa dubu, Sauran ma'aikata kuma zan ba kowanne ɗari biyu.

13 Aminaina suna kasa kunne ga ƙaunataccena. Ina so in ji muryarka daga cikin lambun.

14 Ya ƙaunataccena, ka zo wurina da sauri, kamar batsiya, Ko sagarin kishimi a kan duwatsu inda kayan yaji yake tsirowa.