1

1 Adamu ya haifi Shitu, Shitu ya haifi Enosh,

2 Enosh ya haifi Kenan, Kenan ya haifi Mahalalel, Mahalalel ya haifi Yared,

3 Yared ya haifi Anuhu, Anuhu ya haifi Metusela, Metusela ya haifi Lamek.

4 Lamek ya haifi Nuhu, Nuhu ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.

5 'Ya'yan Yafet, maza ke nan, Gomer, da Magog, da Madai, da Yawan, da Tubal, da Meshek, da Tiras.

6 'Ya'yan Gomer, maza, su ne Ashkenaz, da Rifat, da Togarma.

7 'Ya'yan Yawan, maza, su ne Elisha, da Tarshish, da Kittim, da Rodanim.

8 'Ya'yan Ham, maza, su ne Kush, da Mizrayim, da Fut, da Kan'ana.

9 'Ya'yan Kush, maza, su ne Seba, da Hawila, da Sabta, da Ra'ama, da Sabteka. 'Ya'yan Ra'ama, maza, su ne Sheba da Dedan.

10 Kush shi ne mahaifin Lamirudu wanda shi ne ya fara ƙasaita a duniya.

11 Mizrayim shi ne mahaifin jama'ar Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Naftuhawa,

12 da Fatrusawa, da Kasluhawa tushen Filistiyawa ke nan, da Kaftorawa.

13 Kan'ana shi ne mahaifin Sidon ɗan farinsa, da Het,

14 da Yebusiyawa, da Amoriyawa, da Girgashiyawa,

15 da Hiwiyawa, da Arkiyawa, da Siniyawa,

16 da Arwadiyawa, da Zemariyawa, da Hamatiyawa.

17 'Ya'yan Shem, maza, su ne Elam, da Asshur, da Arfakshad, da Lud, da Aram, da Uz, da Hul, da Geter, da Meshek.

18 Arfakshad shi ne mahaifin Shela, Shela kuma shi ne mahaifin Eber.

19 'Ya'ya biyu maza ne aka haifa wa Eber. Sunan ɗayan Feleg, saboda a lokacinsa ne aka karkasa duniya, sunan ɗan'uwansa kuwa Yokatan.

20 Yokatan shi ne mahaifin Almoda, da Shelef, da Hazarmawet, da Yera,

21 da Adoniram, da Uzal, da Dikla,

22 da Ebal, da Abimayel, da Sheba,

23 da Ofir, da Hawila, da Yobab. Waɗannan duka su ne 'ya'yan Yokatan, maza.

24 Shem ya haifi Arfakshad, Arfakshad ya haifi Shela,

25 Shela ya haifi Eber, Eber ya haifi Feleg, Feleg ya haifi Reyu,

26 Reyu ya haifi Serug, Serug ya haifi Nahor, Nahor ya haifi Tera,

27 Tera ya haifi Abram, wato Ibrahim ke nan.

28 'Ya'yan Ibrahim, maza, su ne Ishaku da Isma'ilu.

29 Ga zuriyarsu. Nabayot shi ne ɗan farin Isma'ilu, sa'an nan sai Kedar, da Abdeyel, da Mibsam,

30 da Mishma, da Duma, da Massa, da Hadad, da Tema,

31 da Yetur, da Nafish, da Kedema. Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'ilu, maza.

32 'Ya'ya maza na Ketura, wato ƙwarƙwarar Ibrahim, su ne Zimran, da Yokshan, da Medan, da Madayana, da Yisbak, da Shuwa. 'Ya'yan Yokshan, maza, su ne Sheba, da Dedan.

33 'Ya'yan Madayana, maza, su ne Efa, da Efer, da Hanok, da Abida, da Eldaya. Waɗannan duka su ne 'ya'yan Ketura, maza.

34 Ibrahim shi ne mahaifin Ishaku. 'Ya'yan Ishaku, maza, su ne Isuwa da Isra'ila.

35 'Ya'yan Isuwa, maza, su ne Elifaz, da Reyuwel, da Yewush, da Yalam da Kora.

36 'Ya'yan Elifaz, maza, su ne Teman, da Omar, da Zeho, da Gatam, da Kenaz, da Tima, da Amalek.

37 'Ya'yan Reyuwel, maza kuwa, su ne Nahat, da Zera, da Shamma, da Mizza.

38 'Ya'yan Seyir, maza kuma, su ne Lotan, da Shobal, da Zibeyon, da Ana, da Dishon, da Ezer, da kuma Dishan.

39 'Ya'yan Lotan, maza, su ne Hori, da Hemam. Timna ce 'yar'uwar Lotan.

40 'Ya'yan Shobal, maza, su ne Alwan, da Manahat, da Ebal, da Sheho, da Onam. 'Ya'yan Zibeyon, maza su ne Aiya da Ana.

41 Dishon shi ne ɗan Ana. 'Ya'yan Dishon, maza kuwa, su ne Hemdan, da Eshban, da Yitran, da Keran.

42 'Ya'yan Ezer, maza, su ne Bilhan, da Zayawan, da Akan. 'Ya'yan Dishan, maza, su ne Uz da Aran.

43 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi sarauta a ƙasar Edom kafin wani Sarkin Isra'ila ya ci sarauta. Bela ɗan Beyor, sunan birninsa kuwa Dinhaba Yobab ɗan Zera na Bozara Husham na ƙasar Teman Hadad ɗan Bedad na Awit, wanda ya kori Madayanawa a filin Mowab Samla na Masrek Shawul na Rehobot wadda take bakin Kogin Yufiretis Ba'al-hanan ɗan Akbor Hadad na Fau, sunan matarsa kuma Mehetabel 'yar Matred, wato jikar Mezahab

44

45

46

47

48

49

50

51 Hadad kuwa ya rasu. Sarakunan Edom su ne Timna, da Alwa, da Yetet,

52 da Oholibama, da Ila, da Finon,

53 da Kenaz, da Teman, da Mibzar,

54 da Magdiyel, da Iram.

2

1 Waɗannan su ne 'ya'yan Isra'ila, maza, Ra'ubainu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza, da Issaka, da Zabaluna,

2 da Dan, da Yusufu, da Biliyaminu, da Naftali, da Gad, da Ashiru.

3 'Ya'yan Yahuza, maza, su ne Er, da Onan, da Shela. Waɗannan uku Batshuwa Bakan'aniya, ita ce ta haifa masa su. Amma Er, ɗan farin Yahuza, mugu ne a gaban Ubangiji, don haka Ubangiji ya kashe shi.

4 Surukarsa Tamar, matar ɗansa kuma ta haifa masa Feresa da Zera. Yahuza yana da 'ya'ya maza biyar.

5 'Ya'yan Feresa, maza kuwa, su ne Hesruna da Hamul.

6 'Ya'yan Zera, maza, su ne Zabdi da Etan, da Heman, da Kalkol, da Darda. Su biyar ke nan.

7 Karmi shi ne mahaifin Akan wanda ya jawo wa Isra'ila wahala a kan abin da aka haramta.

8 Etan yana da ɗa guda ɗaya, shi ne Azariya.

9 'Ya'yan Hesruna, maza, waɗanda aka haifa masa, su ne Yerameyel, da Arama, da kuma Kalibu.

10 Arama shi ne mahaifin Amminadab. Amminadab kuma shi ne mahaifin Nashon, shugaban 'ya'yan Yahuza.

11 Nashon shi ne mahaifin Salmon. Salmon kuwa shi ne mahaifin Bo'aza.

12 Bo'aza kuma shi ne mahaifin Obida. Obida shi ne mahaifin Yesse.

13 Yesse shi ne mahaifin Eliyab ɗan farinsa, sa'an nan sai Abinadab da Shimeya,

14 da Netanel, da Raddai,

15 da Ozem, da Dawuda. Su 'ya'ya maza bakwai ke nan.

16 'Yan'uwansu mata kuwa su ne Zeruya da Abigail. 'Ya'yan Zeruya, maza, su ne Abishai, da Yowab, da Asahel, su uku ke nan.

17 Abigail ta haifi Amasa. Mahaifin Amasa shi ne Yeter daga zuriyar Isma'ilu.

18 Azuba, matar Kalibu ɗan Hesruna ta haifa masa 'ya'ya maza. Matarsa Yeriyot kuma ta haifi 'ya'ya maza, su ne Yesher, da Shobab, da Ardon.

19 Sa'ad da Azuba ta rasu sai Kalibu ya auri Efrata wadda ta haifa masa Hur.

20 Hur shi ne mahaifin Uri, Uri kuwa shi ne mahaifin Bezalel.

21 Bayan haka sai Hesruna ya shiga wurin 'yar Makir mahaifin Gileyad, wadda ya aura sa'ad da yake da shekara sittin da haihuwa. Ta haifa masa Segub.

22 Segub shi ne mahaifin Yayir wanda yake da birane ashirin da uku a ƙasar Gileyad.

23 Amma sai Geshur da Aram suka ƙwace garuruwan Hawwotyayir ɗin daga gare su, har da Kenat da ƙauyukanta, garuruwa sittin. Duk waɗannan su ne zuriyar Makir mahaifin Gileyad.

24 Bayan rasuwar Hesruna, Abaija, matarsa, ta haifa masa Ashur, mahaifin Tekowa.

25 'Ya'yan Yerameyel ɗan farin Hesruna, su ne Arama ɗan fari, sa'an nan Buna, da Oren, da Ozem, da Ahaija.

26 Sai Yerameyel ya auro wata mace, sunanta Atara. Ita ce mahaifiyar Onam.

27 'Ya'yan Arama, ɗan farin Yerameyel, su ne Ma'az, da Yamin, da Eker.

28 'Ya'yan Onam, maza, su ne Shammai da Yada. 'Ya'yan Shammai, maza, su ne Nadab da Abishur.

29 Sunan matar Abishur Abihail, ta haifa masa Aban da Molid.

30 'Ya'yan Nadab, maza, su ne Seled da Affayim, amma Seled ya rasu bai bar 'ya'ya ba.

31 Ɗan Affayim shi ne Ishi. Ɗan Ishi kuwa shi ne Sheshan. Ɗan Sheshan shi ne Alai.

32 'Ya'yan Yada, maza, ɗan'uwan Shammai, su ne Yeter da Jonatan. Amma Yeter ya rasu bai bar 'ya'ya ba.

33 'Ya'yan Jonatan su ne Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yerameyel.

34 Sheshan ba shi da 'ya'ya maza, sai dai 'ya'ya mata. Amma yana da wani bara Bamasare mai suna Yarha.

35 Sai Sheshan ya aurar wa Yarha baransa da 'yarsa, ita kuwa ta haifar masa Attai.

36 Attai shi ne mahaifin Natan, Natan kuma shi ne mahaifin Zabad.

37 Zabad kuwa shi ne mahaifin Eflal, Eflal shi ne ya haifi Obida.

38 Obida shi ne mahaifin Yehu, Yehu kuma shi ne mahaifin Azariya.

39 Azariya shi ne mahaifin Helez, Helez shi ne mahaifin Eleyasa.

40 Eleyasa shi ne mahaifin Sisamai, Sisamai shi ne mahaifin Shallum.

41 Shallum shi ne mahaifin Yekamiya, Yekamiya shi ne mahaifin Elishama.

42 Ɗan Kalibu, ɗan'uwan Yerameyel, shi ne Mesha ɗan farinsa wanda ya haifi Zif. Zif ya haifi Maresha wanda ya haifi Hebron.

43 'Ya'yan Hebron, maza, su ne Kora, da Taffuwa, da Rekem, da Shema.

44 Shema shi ne mahaifin Raham wanda ya kafa Yorkeyam. Rekem kuwa shi ne mahaifin Shammai.

45 Shammai shi ne mahaifin Mayon, Mayon kuwa shi ne mahaifin Bet-zur.

46 Efra ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Haran, da Moza, da Gazez. Haran shi ne mahaifin Gazez.

47 'Ya'yan Yadai, maza, su ne Regem, da Yotam, da Geshan, da Felet, da Efa, da Sha'af.

48 Ma'aka, ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Sheber da Tirhana.

49 Ta kuma haifi Sha'af mahaifin Madmanna, da Shewa mahaifin Makbena, da mahaifin Gibeya. 'Yar Kalibu ita ce Aksa.

50 Waɗannan su ne zuriyar Kalibu, maza. 'Ya'yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, su ne Shobal wanda ya kafa Kiriyat-yeyarim,

51 da Salma, shi kuwa ya kafa Baitalami, da Haref ɗansa kuma wanda ya kafa Bet-gader.

52 Shobal yana da waɗansu 'ya'ya maza, su ne Rewaiya da wanda yake kakan rabin Manahatiyawa,

53 da iyalan da suke a Kiriyat-yeyarim, da na Itiriyawa, da na Futiyawa, da na Shumatiyawa, da na Mishraiyawa. Daga waɗannan ne Zoratiyawa da Eshtawoliyawa suka fito.

54 Salma, wanda ya kafa Baitalami, shi ne kakan mutanen Netofa, da na Atarot-bet-yowab, da rabin Manahatiyawa, da Zoratiyawa.

55 Iyalan gwanayen rubutu waɗanda suka zauna a Yabez, su ne Tiratiyawa, da Shimeyatiyawa, da Sukatiyawa. Su ne Keniyawa na Hammat, Hammat kuwa shi ne mahaifin mutanen Rekab.

3

1 Waɗannan su ne 'ya'yan Dawuda, maza, waɗanda aka haifa masa a Hebron. Amnon wanda Ahinowam Bayezreyeliya ta haifa masa. Kileyab wanda Abigail Bakarmeliya ta haifa masa. Absalom ɗan Ma'aka 'yar Talmai, Sarkin Geshur. Adonaija ɗan Haggit. Shefatiya wanda Abital ta haifa. Itireyam wanda Egla ta haifa.

2

3

4 Dukansu shida an haife su ne a Hebron inda ya yi sarauta shekara bakwai da wata shida. Ya yi sarauta a Urushalima shekara talatin da uku.

5 Waɗanda aka haifa masa a Urushalima, su ne Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu, su huɗu ke nan waɗanda Bat-sheba 'yar Ammiyel ta haifa masa.

6 Yana da waɗansu 'ya'ya kuma, su ne Ibhar, da Elishuwa da Elifelet,

7 da Noga, da Nefeg, da Yafiya,

8 da Elishama, da Eliyada, da kuma Elifelet, su tara ke nan.

9 Waɗannan duka su ne 'ya'yan Dawuda, maza, banda 'ya'yan ƙwaraƙwarai. Tamar ita ce 'yar'uwarsu.

10 Waɗannan su ne zuriyar Sulemanu, daga Rehobowam, sai Abaija, da Asa, da Yehoshafat,

11 da Yoram, da Ahaziya, da Yowash,

12 da Amaziya, da Azariya, da Yotam,

13 da Ahaz, da Hezekiya da Manassa,

14 da Amon, da Yosiya.

15 'Ya'yan Yosiya, maza, su ne Yohenan ɗan farinsa, na biyu shi ne Eliyakim, na uku shi ne Zadakiya, na huɗu shi ne Yehowahaz,

16 Eliyakim yana da 'ya'ya biyu maza, su ne Yekoniya, da Zadakiya.

17 'Ya'yan Yekoniya wanda aka kama, su ne Sheyaltiyel,

18 da Malkiram, da Fedaiya, da Shenazzar, da Yekamiya, da Hoshama, da Nedabiya.

19 Fedaiya yana da 'ya'ya biyu maza, su ne Zarubabel da Shimai. 'Ya'yan Zarubabel, maza, su ne Meshullam, da Hananiya, da Shelomit 'yar'uwarsu,

20 da Hashuba, da Ohel, da Berikiya, da Hasadiya, da Yushab-hesed, su biyar ke nan.

21 'Ya'yan Hananiya, maza, su ne Felatiya, da Yeshaya, da 'ya'yan Refaya, maza, da 'ya'yan Arnan, maza, da 'ya'yan Obadiya, maza, da 'ya'yan Shekaniya, maza.

22 Ɗan Shekaniya shi ne Shemaiya. 'Ya'yan Shemaiya, maza, su ne Hattush, da Igal, da Bariya da Neyariya, da Shafat, su shida ke nan.

23 'Ya'yan Neyariya, maza, su ne Eliyehoyenai, da Hezekiya, da Azrikam, su uku ne nan.

24 'Ya'yan Eliyehoyenai, maza, su ne Hodawiya, da Eliyashib, da Felaya, da Akkub, da Yohenan, da Dalaya, da Anani, su bakwai ke nan.

4

1 'Ya'yan Yahuza, maza, su ne Feresa, da Hesruna, da Karmi, da Hur, da Shobal.

2 Rewaiya ɗan Shobal, shi ne mahaifin Yahat. Yahat shi ya haifi Ahumai, da Lahad. Waɗannan su ne iyalin Zoratiyawa.

3 Waɗannan kuma su ne 'ya'yan Itam, Yezreyel, da Ishma, da Idbasha, da 'ya ɗaya, ita ce Hazzelelfoni.

4 Feniyel shi ne mahaifin Gedor, Ezer kuwa shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne 'ya'yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, zuriyarsa ne suka kafa Baitalami.

5 Ashur, wanda ya kafa Tekowa, yana da mata biyu, su ne Hela, da Nayara.

6 Nayara ta haifa masa Ahuzzam, da Hefer, da Temeni, da Hayahashtari. Waɗannan su ne 'ya'yan Nayara, maza.

7 'Ya'yan Hela, maza, su ne Zeret, da Izhara, da Etnan.

8 Hakkoz shi ne mahaifin Anub, da Zobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.

9 Yabez ya fi sauran 'yan'uwansa kwarjini saboda haka mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, wato da wahala ta haife shi.

10 Yabez ya roƙi Allah na Isra'ila, ya ce, “Ka sa mini albarka, ka faɗaɗa kan iyakata, hannunka kuma ya kasance tare da ni, ka kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni.” Allah kuwa ya biya masa bukatarsa.

11 Kalibu ɗan'uwan Shuwa, shi ne mahaifin Mehir wanda ya haifi Eshton.

12 Eshton kuwa shi ne ya haifi Bet-rafa, da Faseya, da Tehinna wanda ya kafa birnin Ir-nahash, zuriyar waɗannan mutane kuwa su suka zauna a Reka.

13 'Ya'yan Kenaz, maza, su ne Otniyel da Seraiya. Yana kuma da waɗansu 'ya'ya maza, su ne Hatata da Meyonotai.

14 Meyonotai kuwa shi ne mahaifin Ofra. Seraiya shi ne ya haifi Yowab, Yowab ya kafa kwarin Ge-harashim, saboda su masu sana'a ne.

15 'Ya'yan Kalibu, maza, ɗan Yefunne, su ne Airu, da Ila, da Na'am. Ila shi ya haifi Kenaz.

16 'Ya'yan Yehallelel, maza, su ne Zif, da Zifa, da Tiriya, da Asarel.

17 'Ya'yan Ezra, maza, su ne Yeter, da Mered, da Efer, da Yalon. Bitiya 'yar Fir'auna, wadda Mered ya aura, ta haifi waɗannan, Maryamu, da Shammai, da Ishaba wanda ya haifi Eshtemowa. Mered kuma ya auri wata daga kabilar Yahuza, ta haifi Yered wanda ya kafa garin Gedor. Eber kuma ya kafa garin Soko, Yekutiyel kuwa ya kafa garin Zanowa.

18

19 'Ya'ya maza na matar Hodiya 'yar'uwar Naham, su ne suka zama kakannin Kaila, Bagarme, da Eshtemowa da suke zaune a Ma'aka.

20 'Ya'yan Shimon, maza, su ne Amnon, da Rinna, da Ben-hanan, da Tilon. 'Ya'yan Ishi, maza kuwa, su ne Zohet da Ben-zohet.

21 'Ya'yan Shela, maza, ɗan Yahuza, su ne Er wanda ya kafa garin Leka, da La'ada wanda ya kafa garin Maresha, da iyalan gidan masu aikin lilin da suke zaune a Bet-ashbeya,

22 da Yokim, da mutanen da suke zaune a Kozeba, da Yowash, da Saraf, waɗanda suka yi sarauta a Mowab, sa'an nan suka zauna a Baitalami. (Waɗannan labaru na tun dā ne.)

23 Su ne maginan tukwane, waɗanda suke zaune a Netayim da Gedera. Sun zauna tare da sarki don su yi masa aiki.

24 'Ya'yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin, da Zohar, da Shawul,

25 da Shallum ɗansa, da Mibsam jīkansa, da Mishma jīkan ɗansa.

26 'Ya'yan Mishma, maza, su ne Hammuwel, da Zakkur, da Shimai.

27 Shimai yana da 'ya'ya maza goma sha shida, da 'ya'ya mata shida, amma 'yan'uwansa ba su da 'ya'ya da yawa kamarsa. Iyalin Saminu ba su kai yawan na Yahuza ba.

28 Suka zauna a waɗannan garuruwa, wato Biyer-sheba, da Molada, da Hazar-shuwal,

29 da Bilha, da Ezem, da Eltola,

30 da Betuwel, da Horma, da Ziklag,

31 da Bet-markabot, da Hazarsusa, da Bet-biri, da Shayarim. Waɗannan su ne biranensu tun kafin Dawuda ya yi sarauta.

32 Sun kuwa zauna a waɗansu wurare guda biyar, wato Itam, da Ayin, da Rimmon, da Token, da Ashan, da ƙauyukan da suke kewaye, har zuwa kudu maso gabas da garin Ba'al: Ga lissafin iyalansu da wuraren da suka zauna.

33

34 Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya, Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya, wato jīkan Seraiya, ɗan Asiyel, Eliyehoyenai, da Ya'akoba, da Yeshohaya, da Asaya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benaiya, Ziza ɗan Shifi, wato jīkan Allon, zuriyar Yedaiya, da Shimri ɗan Shemaiya.

35

36

37

38 Waɗannan da aka jera sunayensu, su ne shugabannin iyalansu da gidajen kakanninsu. Sun ƙaru ƙwarai.

39 Suka yi tafiya har zuwa mashigin Gedor, zuwa gabashin kwarin don nemar wa garkunansu makiyaya.

40 A can suka sami makiyaya mai kyau mai dausayi. Ƙasar kuwa tana da faɗi, babu fitina, sai salama, gama mazaunan wurin a dā Hamawa ne.

41 Waɗannan da aka lasafta sunayensu, su ne suka zo a kwanakin Hezekiya Sarkin Yahuza, suka fāɗa wa alfarwai da bukkoki waɗanda suka tarar a can, suka hallaka su sarai, sa'an nan suka maye wurinsu saboda akwai makiyaya domin garkunansu a wurin.

42 Waɗansu daga cikinsu, mutum ɗari biyar daga zuriyar Saminu, suka tafi wajen gabashin Edom. Waɗanda suka shugabance su kuwa, su ne 'ya'yan Ishi, wato Felatiya, da Neyariya, da Refaya, da Uzziyel.

43 A can suka karkashe sauran Amalekawan da suka ragu, sa'an nan suka zauna a can har wa yau.

5

1 Ra'ubainu shi ne ɗan farin Isra'ila, amma saboda ya ƙazantar da gadon mahaifinsa aka ba 'ya'yan Yusufu, maza, ɗan Isra'ila, gādonsa na ɗan fari. Don haka ba a lasafta shi a kan matsayin ɗan fari ba.

2 Ko da yake Yahuza ya rinjayi 'yan'uwansa, har daga gare shi aka sami shugaba, duk da haka matsayin ɗan farin na Yusufu ne.

3 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, wato ɗan farin Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi.

4 'Ya'yan Yowel, maza, su ne Shemaiya, da Gog, da Shimai,

5 da Mika, da Rewaiya, da Ba'al,

6 da Biyera wanda Tiglat-filesar Sarkin Assuriya ya kai bauta. Shi ne shugaban Ra'ubainawa.

7 Danginsa bisa ga iyalansu da asalinsu a zamaninsu, su ne sarki Yehiyel, da Zakariya,

8 da Bela ɗan Azaz, wato jīkan Shema, ɗan Yowel, wanda ya zauna a Arower har zuwa Nebo da Ba'al-meyon.

9 Ya kuma zauna wajen gabas, har zuwa goshin jejin da yake wajen Kogin Yufiretis, saboda shanunsu sun ƙaru a ƙasar Gileyad.

10 Zuriyar Ra'ubainu suka yi yaƙi da Hagarawa a kwanakin Saul. Suka ci Hagarawa, saboda haka suka zauna a ƙasar da take gabashin Gileyad.

11 'Ya'yan Gad, maza, suka zauna a ƙasar Bashan, daura da Ra'ubainawa har zuwa Salka.

12 Yowel ne sarki, Shafam kuwa shi ne na biyun, da Yanai, da Shafat, su ne tushen Bashan.

13 Danginsu bisa ga gidajen kakanninsu, su ne Maikel, da Meshullam, da Sheba, da Yorai, da Jakan, da Ziya, da Eber, su bakwai ke nan.

14 Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Abihail ɗan Huri. Ga yadda kakanninsu suke, wato Abihail, ɗan Huri ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Maikel, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.

15 Ahi ɗan Abdiyel, wato jīkan Guni, shi ne shugaban gidan kakanninsu.

16 Suka zauna a Gileyad, da Bashan, da garuruwanta, da dukan iyakar makiyayar Sharon.

17 (An rubuta waɗannan duka bisa ga asalinsu a zamanin Yotam, Sarkin Yahuza, da Yerobowam Sarkin Isra'ila.)

18 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa suna da jarumawa masu riƙon garkuwa da takobi, masu harbi kuma da baka. Gwanayen yaƙi ne, su dubu arba'in da huɗu, da ɗari bakwai da sittin ne (44,760).

19 Suka yi yaƙi da Hagarawa, da Yetur, da Nafish, da Nodab.

20 Aka taimake su yin yaƙi da abokan gābansu, sai aka ba da Hagarawa da duk waɗanda suke tare da su a hannunsu, saboda suka yi roƙo ga Allah a cikin yaƙin, Allah kuwa ya amsa musu roƙonsu saboda sun dogara gare shi.

21 Sai suka kwashe dabbobinsu, raƙuma dubu hamsin (50,000), da tumaki dubu ɗari biyu da dubu hamsin (250,000), da jakuna dubu biyu (2,000), da kuma mutane dubu ɗari (100,000).

22 Aka karkashe mutane da yawa, domin yaƙin na Allah ne. Sai suka gāje wurin zamansu, har lokacin da aka kai su bauta.

23 Mutanen rabin kabilar Manassa suna da yawa, sun zauna a ƙasar, daga Bashan har zuwa Ba'al-harmon, da Senir, da Dutsen Harmon.

24 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu, Efer, da Ishi, da Eliyel, da Azriyel, da Irmiya, da Hodawiya, da Yadiyel. Su jarumawa ne na gaske, masu suna, su ne shugabannin gidajen kakanninsu.

25 Amma mutanen suka yi rashin gaskiya ga Allah na kakanninsu, suka bi gumakan mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.

26 Don haka Allah na Isra'ila ya zuga Ful, Sarkin Assuriya, wato Tiglat-filesar, ya zo ya kwashe su, ya kai su bauta, wato su Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa. Ya kai su Hala, da Habor, da Hara, har zuwa kogin Gozan, can suke har yau.

6

1 'Ya'yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari.

2 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel.

3 'Ya'yan Amram kuwa, su ne Haruna, da Musa, da Maryamu. 'Ya'yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.

4 Zuriyar Ele'azara daga tsara zuwa tsara, su ne Finehas, da Abishuwa,

5 da Bukki, da Uzzi,

6 da Zarahiya, da Merayot,

7 da Amariya, da Ahitub,

8 da Zadok, da Ahimawaz,

9 da Azariya, da Yohenan,

10 da Azariya wanda ya yi hidimar firist a Haikalin da Sulemanu ya gina a Urushalima.

11 Ga Amariya kuma da Ahitub,

12 da Zakok, da Meshullam,

13 da Hilkiya, da Azariya,

14 da Seraiya, da Yehozadak.

15 Sarki Nebukadnezzar ya kama Yehozadak, ya tafi da shi tare da sauran jama'a zuwa zaman talala, sa'ad da Ubangiji ya ba da su a hannun Nebukadnezzar don su yi zaman talala.

16 'Ya'yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari.

17 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Gershon, maza, Libni da Shimai.

18 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel.

19 'Ya'yan Merari, maza kuwa, su ne Mali da Mushi. Waɗannan su ne iyalan Lawiyawa bisa ga gidajen kakanninsu.

20 Zuriyar Gershon bi da bi, su ne Libni, da Yahat, da Zimma,

21 da Yowa, da Iddo, da Zera, da Yewaterai.

22 Zuriyar Kohat bi da bi, su ne Izhara, da Kora, da Assir,

23 da Elkana, da Ebiyasaf, da Assir,

24 da Tahat, da Uriyel, da Azariya, da Shawul.

25 'Ya'yan Elkana, maza, su ne Amasai da Ahimot.

26 Zuriyar Ahimot bi da bi, su ne Elkana, da Zofai, da Nahat,

27 da Eliyab, da Yeroham, da Elkana.

28 'Ya'yan Sama'ila, maza, su ne Yowel ɗan farinsa, na biyun shi ne Abaija.

29 Zuriyar Merari bi da bi, su ne Mali, da Libni, da Shimai, da Uzza,

30 da Shimeya, da Haggiya, da Asaya.

31 Waɗannan su ne waɗanda Dawuda ya sa su su zama mawaƙa a Haikalin Ubangiji, sa'ad da aka kawo akwatin alkawari a cikin Haikalin.

32 Suka yi ta raira waƙoƙi a gaban wurin zama na alfarwa ta taruwa tun kafin Sulemanu ya gina Haikalin Ubangiji a Urushalima. Suka yi hidima bisa ga matsayinsu ta yadda aka tsara.

33 Waɗannan su ne waɗanda suka yi ta raira waƙoƙin, su da 'ya'yansu maza. Daga iyalin Kohat, Heman shi ne shugaban ƙungiyar farko ta mawaƙa, shi ɗan Yowel ne, ɗan Sama'ila,

34 ɗan Elkana, ɗan Yeroham, ɗan Eliyab, ɗan Mahat,

35 ɗan Zafai, ɗan Elkana, ɗan Mahat, ɗan Amasai,

36 ɗan Elkana, ɗan Shawul, ɗan Azariya, ɗan Uriyel,

37 ɗan Tahat, ɗan Assir, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora,

38 ɗan Izhara, ɗan Kohat, ɗan Lawi, ɗan Isra'ila.

39 Asaf kuma shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta biyu. Shi ɗan Berikiya ne, ɗan Shimeya,

40 ɗan Maikel, ɗan Ba'aseya, ɗan Malkiya,

41 ɗan Yewaterai, ɗan Zera, ɗan Iddo,

42 ɗan Yowa, ɗan Zimma, ɗan Shimai,

43 ɗan Yahat, ɗan Gershon, ɗan Lawi.

44 Etan na zuriyar Merari, shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta uku, asalinsa shi ɗan Kishi ne, ɗan Abdi, ɗan Malluki,

45 ɗan Hashabiya, ɗan Amaziya, ɗan Hilkiya,

46 ɗan Amzi, ɗan Bani, ɗan Shemer,

47 ɗan Mali, ɗan Mushi, ɗan Merari, ɗan Lawi.

48 Aka sa 'yan'uwansu, Lawiyawa, su yi dukan hidimomi a cikin Haikalin Ubangiji.

49 Amma Haruna da 'ya'yansa maza suka miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa, da kan bagaden ƙona turare, domin dukan aikin Wuri Mafi Tsarki, da kuma yin kafara domin Isra'ila bisa ga dukan abin da Musa, bawan Allah, ya umarta.

50 Waɗannan su ne zuriyar Haruna, maza, bi da bi, Ele'azara, da Finehas, da Abishuwa,

51 da Bukki, da Uzzi, da Zerahiya,

52 da Merayot, da Amariya, da Ahitub,

53 da Zadok da Ahimawaz.

54 Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna, na iyalin Kohat. Sun karɓi rabo na farko a ƙasar.

55 Rabonsu ya haɗu da Hebron ta yankin ƙasar Yahuza, da makiyayar da suke kewaye da ita.

56 Amma an ba Kalibu ɗan Yefunne saurukan birnin, tare da ƙauyukansa.

57 Suka ba 'ya'yan Haruna, maza, biranen mafaka, wato Hebron, da Libna tare da makiyayarta, da Yattir, da Eshtemowa tare da makiyayarta,

58 da Holon tare da makiyayarta, da Debir tare da makiyayarta,

59 da Ayin tare da makiyayarta, da Bet-shemesh tare da makiyayarta.

60 Daga kabilar Biliyaminu aka ba su Geba tare da makiyayarta, da Allemet tare da makiyayarta, da Anatot tare da makiyayarta. Dukan biranen iyalansu guda goma sha uku ne.

61 Aka ba sauran 'ya'yan Kohat, maza, garuruwa goma daga na rabin kabilar Manassa, ta hanyar kuri'a.

62 Aka kuma ba Gershonawa bisa ga iyalansu, birane goma sha uku daga na kabilar Issaka, da na kabilar Ashiru, da na kabilar Naftali, da na kabilar Manassa da take nan a Bashan.

63 Haka kuma aka ba 'ya'yan Merari, maza, bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga na kabilar Ra'ubainu, da na kabilar Gad, da na kabilar Zabaluna.

64 Haka fa, jama'ar Isra'ila suka ba Lawiyawa garuruwa duk da makiyayansu.

65 Daga na kabilar Yahuza, da na kabilar Saminu, da na kabilar Biliyaminu kuma aka ba da waɗannan garuruwan da aka ambaci sunayensu ta hanyar kuri'a.

66 Waɗansu daga cikin iyalan 'ya'yan Kohat, maza, sun sami garuruwa na yankinsu daga cikin kabilar Ifraimu.

67 Sai suka ba su waɗannan biranen mafaka, wato Shekem a ƙasar tudu ta Ifraimu duk da makiyayarta, da Gezer tare da makiyayarta,

68 da Yokmeyam duk da makiyayarta, da Bet-horon duk da makiyayarta,

69 da Ayalon duk da makiyayarta, da Gatrimmon duk da makiyayarta.

70 Daga cikin rabin kabilar Manassa kuma an ba su Ta'anak duk da makiyayarta, da Bileyam duk da makiyayarta. An ba da waɗannan ga sauran iyalai na 'ya'yan Kohat, maza.

71 Daga na rabin kabilar Manassa na gabas, an ba 'ya'yan Gershon, maza, Golan ta Bashan tare da makiyayarta, da Ashtarot duk da makiyayarta.

72 Daga na kabilar Issaka kuma an ba su Kishiyon duk da makiyayarta, da Daberat duk da makiyayarta,

73 da Ramot duk da makiyayarta, da Enganin duk da makiyayarta.

74 Daga cikin kabilar Ashiru kuma an ba da Mishal duk da makiyayarta, da Abdon duk da makiyayarta,

75 da Helkat duk da makiyayarta, da Rehob duk da makiyayarta.

76 Daga na kabilar Naftali kuma an ba da Kedesh ta Galili duk da makiyayarta, da Hammon duk da makiyayarta, da Kartan duk da makiyayarta.

77 Daga na kabilar Zabaluna, an ba sauran Lawiyawa, wato 'ya'yan Merari, maza, Rimmon duk da makiyayarta, da Tabor duk da makiyayarta.

78 Daga na kabilar Ra'ubainu a hayin Urdun a Yariko, wato gabashin Urdun, an ba da Bezer ta cikin jeji duk da makiyayarta, da Yahaza duk da makiyayarta,

79 da Kedemot duk da makiyayarta, da Mefayat duk da makiyayarta.

80 Daga na kabilar Gad kuma an ba da Ramot ta Gileyad duk da makiyayarta, da Mahanayim duk da makiyayarta,

81 da Heshbon duk da makiyayarta, da Yazar duk da makiyayarta.

7

1 'Ya'yan Issaka, maza, su huɗu ne, wato Tola, da Fuwa, da Yashub, da Shimron.

2 'Ya'yan Tola, maza, su ne Uzzi, da Refaya, da Yeriyel, da Yamai, da Ibsam, da Sama'ila, su ne shugabannin gidajen kakanninsu. 'Ya'yan Tola kuwa manyan mayaƙa ne a zamaninsu. Yawansu a zamanin Dawuda, su dubu ashirin da biyu ne da ɗari shida (22,600).

3 Ɗan Uzzi, shi ne Izrahiya. 'Ya'yan Izrahiya, maza, su ne Maikel, da Obadiya, da Yowel, da Isshiya. Su biyar duka manyan mutane ne.

4 A zamaninsu, bisa ga gidajen kakanninsu suna da sojoji dubu talatin da dubu shida (36,000) gama suna da mata da yara da yawa.

5 Mayaƙan da aka lasafta bisa ga asalinsu na dukan iyalan Issaka, su dubu tamanin da dubu bakwai ne (87,000), jarumawa ne sosai.

6 'Ya'yan Biliyaminu su uku ne, wato Bela, da Beker, da Yediyayel.

7 'Ya'yan Bela, maza, su biyar ne, wato Ezbon, da Uzzi, da Uzziyel, da Yerimot, da Iri. Su ne shugabannin gidajen kakanninsu, jarumawa ne su. An lasafta su bisa ga asalinsu, su dubu ashirin da biyu ne da talatin da huɗu (22,034).

8 'Ya'yan Beker, maza, su ne Zemira, da Yowash, da Eliyezer, da Eliyehoyenai, da Omri, da Yerimot, da Abaija da Anatot, da Alamet. Waɗannan duka 'ya'yan Beker ne, maza.

9 An lasafta su bisa ga asalinsu a zamaninsu, su dubu ashirin ne da ɗari biyu (20,200), jarumawa ne su sosai. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu.

10 Ɗan Yediyayel shi ne Bilhan. 'Ya'yan Bilhan, maza, su ne Yewush, da Biliyaminu, da Ehud, da Kena'ana, da Zetan, da Tarshish, da Ahishahar.

11 Duk waɗannan 'ya'yan Yediyayel, maza ne, bisa ga shugabannin gidajen kakanninsu. Su dubu goma sha bakwai ne da ɗari biyu (17,200), jarumawa ne sosai, shiryayyu don yaƙi.

12 Shuffim da Huffim su ne 'ya'yan Iri, maza. Hushim shi ne ɗan Ahiram.

13 Naftali yana da 'ya'ya huɗu, su ne Yazeyel, da Guni, da Yezer, da Shallum. Su ne zuriya daga Bilha.

14 'Ya'yan Manassa, maza, su ne Asriyel, wanda ƙwarƙwararsa Ba'aramiya ta haifa masa. Ta kuma haifi Makir mahaifin Gileyad.

15 Makir ya auro wa Huffim da Shuffim mata. Sunan 'yar'uwarsa Ma'aka, sunan ɗan'uwansa kuwa Zelofehad, Zelofehad yana da 'ya'ya mata kaɗai.

16 Sai Ma'aka matar Makir ta haifi ɗa, ta sa masa suna Feres, sunan ɗan'uwansa kuwa Sheres. 'Ya'yan Feres maza, su ne Ulam da Rakem.

17 Ɗan Ulam shi ne Bedan. Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Gileyad ɗan Makir, jīkan Manassa.

18 'Yar'uwarsa, Hammoleket ta haifi Ishodi, da Abiyezer, da Mala.

19 'Ya'yan Shemida, maza, su ne Ahiyan, da Shekem, da Liki, da Aniyam.

20 'Ya'yan Ifraimu, maza, daga tsara zuwa tsara, su ne Shutela, da Bered, da Tahat, da Eleyada, da Tahat,

21 da Zabad, da Shutela, da Ezer, da Eleyad waɗanda mutanen Gat, haifaffun ƙasar, suka kashe sa'ad da suka kai hari don su kwashe dabbobinsu.

22 Sai mahaifinsu, Ifraimu, ya yi ta makoki kwanaki da yawa. 'Yan'uwansu kuwa suka zo don su yi masa ta'aziyya.

23 Sa'an nan ya shiga wurin matarsa, ta kuwa sami juna biyu, ta haifi ɗa, ya raɗa masa suna Beriya saboda masifar da ta auko wa gidansa.

24 'Yarsa kuma ita ce Sheyera, wadda ta gina garin Bet-horon na kwari da na tudu, ta kuma gina Uzzen-sheyera.

25 Waɗansu zuriyarsa bi da bi, su ne Refa, da Reshe, da Tela, da Tahan,

26 da Ladan, da Ammihud, da Elishama,

27 da Nun, da Joshuwa.

28 Mallakarsu da wuraren zamansu, su ne Betel duk da garuruwanta, da Nayaran wajen gabas, da Gezer wajen yamma duk da garuruwanta, da Shekem duk da garuruwanta, har zuwa Ayya duk da garuruwanta.

29 Zuriyar Manassa sun mallaki Bet-sheyan, da Ta'anak, da Magiddo, da Dor duk da garuruwan da suke kewaye da su. A nan ne zuriyar Yusufu, ɗan Isra'ila, suka zauna.

30 'Ya'yan Ashiru, maza, su ne Yimna, da Yishuwa, da Yishwi, da Beriya, da 'yar'uwarsu Sera.

31 'Ya'yan Beriya, maza, su ne Eber, da Malkiyel wanda ya kafa garin Birzayit.

32 Eber shi ne mahaifin Yaflet, da Shemer, da Helem, da 'yar'uwarsu Shuwa.

33 'Ya'yan Yaflet, maza, su ne Fasak, da Bimhal, da Ashewat.

34 'Ya'yan Shemer maza, su ne Ahi, da Roga, da Yehubba, da Aram.

35 'Ya'ya maza na ɗan'uwansa Helem, su ne Zofa, da Imna, da Sheles da Amal.

36 'Ya'yan Zofa, su ne Suwa, da Harnefer, da Shuwal, da Beri, da Imra,

37 da Bezer, da Hod, da Shamma, da Shilsha, da Yeter, da Biyera.

38 'Ya'yan Yeter, su ne Yefunne, da Fisfa, da Ara.

39 'Ya'yan Ulla, maza, su ne Ara, da Haniyel, da Riziya.

40 Waɗannan duka su ne zuriyar Ashiru, su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu. Zaɓaɓɓun jarumawa ne su, manyan sarakuni. Yawansu da aka lasafta bisa ga asalinsu don yaƙi su dubu ashirin da dubu shida ne (26,000).

8

1 Biliyaminu yana da 'ya'ya biyar, su ne Bela, da Ashbel, da Ahiram,

2 da Noha, da Rafa.

3 Bela kuma yana da 'ya'ya maza, su ne Adar, da Gera da Abihud,

4 da Abishuwa, da Na'aman, da Ahowa,

5 da Gera, da Shuffim, da Huram.

6 Waɗannan kuma su ne 'ya'yan Ehud, maza. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Geba, waɗanda aka kai su bauta a Manahat.

7 Ga sunayensu, Na'aman, da Ahaija, da Gera wanda yake shugabansu lokacin da aka kai su bauta. Shi ne kuma mahaifin Uzza da Ahihud.

8 Shaharayim kuma yana da 'ya'ya maza a ƙasar Mowab bayan da ya saki matansa biyu, wato Hushim da Ba'ara.

9 Matarsa Hodesh ta haifa masa 'ya'ya maza, su ne Yobab, da Zibiya, da Mesha, da Malkam,

10 da Yuz, da Sakiya, da Mirma. Waɗannan su ne 'ya'yansa maza, shugabannin gidajen kakanninsu.

11 Hushim kuma ta haifa masa waɗansu 'ya'ya maza, su ne Abitub da Elfayal.

12 'Ya'yan Elfayal, su ne Eber, da Misham, da Shemed wanda ya gina Ono da Lod da ƙauyukansu, da

13 Beriya, da Shimai, su ne shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Ayalon waɗanda suka kori mazaunan Gat,

14 da Ahiyo, da Shashak, da Yeremot.

15 Zabadiya, da Arad, da Eder,

16 da Maikel, da Ishfa, da Yoha, su ne 'ya'yan Beriya, maza.

17 Zabadiya, da Meshullam, da Hizki, da Eber,

18 da Ishmerai, da Izliya, da Yobab, su ne zuriyar Elfayal.

19 Zuriyar Shimai, su ne Yakim, da Zikri, da Zabdi,

20 da Eliyenai, da Zilletai, da Eliyel,

21 da Adaya, da Beraiya, da Shimrat.

22 Zuriyar Shashak, su ne Isfan, da Eber, da Eliyel,

23 da Abdon, da Zikri, da Hanan,

24 da Hananiya, da Elam, da Antotiya,

25 da Ifediya, da Feniyel.

26 Zuriyar Yeroham, su ne Shemsherai, da Shehariya, da Ataliya,

27 da Yawareshiya, da Eliya, da Zikri.

28 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakanninsu a zamaninsu, waɗanda suka zauna a Urushalima.

29 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a can. Sunan matarsa Ma'aka.

30 Abdon ne ɗansa na fari, sa'an nan Zur, da Kish, da Ba'al, da Nadab,

31 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya,

32 da Miklot, mahaifin Shimeya. Waɗannan su ne suka zauna daura da 'yan'uwansu a Urushalima.

33 Ner shi ne mahaifin Kish, Kish kuma shi ne mahaifin Saul, Saul shi ne mahaifin Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet.

34 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika.

35 'Ya'yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz.

36 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza.

37 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel.

38 Azel ya haifi 'ya'ya maza su shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Ismayel, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.

39 'Ya'ya maza na Esheke ɗan'uwansa su ne, Ulam, da Yewush, da Elifelet.

40 'Ya'yan Ulam, maza, jarumawa ne sosai, 'yan baka, suna da 'ya'ya maza, da jikoki maza da yawa. Su ɗari da hamsin ne. Waɗannan duka mutanen Biliyaminu ne.

9

1 Haka kuwa aka lasafta Isra'ilawa bisa ga asalinsu. An rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila. Sai aka kai mutanen Yahuza zaman talala a Babila saboda rashin amincinsu ga Ubangiji.

2 Waɗanda suka fara zama a biranen mallakarsu, su ne Isra'ilawa da firistoci, da Lawiyawa, da kuma ma'aikatan Haikali.

3 Waɗansu mutanen Yahuza, da na Biliyaminu, da na Ifraimu, da na Manassa suka zauna a Urushalima.

4 Iyalin Yahuza guda ɗari shida da tasa'in suka zauna a Urushalima, shugabansu kuwa shi ne Utai ɗan Ammihud, jīkan Omri daga wajen Feresa. Waɗansu kakanninsu kuwa su ne Imri da Bani. Zuriyar Shela ɗan Yahuza suna da shugaba mai suna Asaya. Zuriyar Zera ɗan Yahuza kuwa, shugabansu Yuwel.

5

6

7 Ga zuriyar Biliyaminu a Urushalima bi da bi, da Sallai ɗan Meshullam, da Hodawiya, da Hassenuwa,

8 da kuma Ibneya ɗan Yeroham, da Ila ɗan Uzzi, wato jīkan Mikri, da Meshullam ɗan Shefatiya, da Reyuwel, da Ibnija.

9 Tare da danginsu a zamaninsu, sun kai ɗari tara da hamsin da shida ne. Duk waɗannan shugabannin gidajen kakanninsu ne.

10 Daga cikin firistoci masu zama a Urushalima su ne Yedaiya, da Yehoyarib, da Yakin,

11 da Azariya ɗan Hilkiya, shi ne jami'in Haikalin Ubangiji, kakanninsa sun haɗu da Shallum ɗan Zadok, da Merayot, da Ahitub,

12 da Adaya ɗan Yeroham, kakanninsa sun haɗu da Fashur, da Malkiya, da Ma'asai ɗan Adiyel, kakanninsa sun haɗu da Yazera, da Meshullam, da Meshillemot, da Immer.

13 Firistacin da suke shugabannin gidajen kakanninsu, sun kai mutum dubu da ɗari bakwai da sittin (1,760). Ƙwararru ne cikin hidimar Haikalin Ubangiji.

14 Lawiyawa masu zama a Urushalima kuma, su ne Shemaiya ɗan Hasshub, wanda kakanninsa suka haɗu da Azrikam da Hashabiya daga 'ya'yan Merari, maza,

15 da kuma Bakbakkar, da Heresh, da Galal, da Mattaniya ɗan Mika wanda kakanninsa su ne Zikri da Asaf,

16 da kuma Obadiya ɗan Shemaiya, kakanninsa su ne Galal da Yedutun, da Berikiya ɗan Asa, wato jīkan Elkana, wanda ya zauna a garin Netofa.

17 Masu tsaron Haikalin, su ne Shallum, da Akkub, da Talmon, da Ahiman, da 'yan'uwansu. Shallum shi ne shugaba.

18 Har zuwa yau, iyalinsu suke tsaron ƙofar sarki a wajen gabas. A dā su ne suke tsaron sauran ƙofofin zangon Lawiyawa.

19 Shallum ɗan Kore, wato jīkan Ebiyasaf, tare da 'yan'uwansa na zuriyar Kora, suke lura da masu tsaron ƙofofin alfarwa kamar dai yadda kakanninsu suka lura da zangon Ubangiji.

20 A dā Finehas ɗan Ele'azara shi ne shugabansu, Ubangiji kuwa yana tare da shi.

21 Zakariya ɗan Shallum yake tsaron ƙofar alfarwa ta sujada.

22 Dukan waɗanda aka zaɓa domin su zama masu tsaron ƙofofi, su ɗari biyu ne da goma sha biyu. An lasafta su bisa ga asalinsu da garuruwansu. Dawuda da Sama'ila annabi, su ne suka sa su a matsayinsu na riƙon amana.

23 Saboda haka su da 'ya'yansu maza suke tsaron ƙofofin Ubangiji, wato alfarwa ta sujada.

24 Matsaran ƙofofi suka tsaya a kusurwoyi huɗu, wato gabas da yamma, kudu da arewa.

25 'Yan'uwansu waɗanda suke a ƙauyuka kuwa, ya zamar musu wajibi su zo wurinsu kowane kwana bakwai, domin su karɓe su tsaron.

26 Su shugabanni huɗu na matsaran ƙofar Lawiyawa ne waɗanda suke da matsayi na riƙon amana, su ne masu lura da ɗakunan Haikalin Allah da dukiyarsa.

27 Sukan kwana suna tsaro kewaye da Haikalin Allah, gama hakkin yana kansu. Su ne sukan buɗe shi kowace safiya.

28 Waɗansunsu suna lura da kayayyakin aiki na cikin Haikali. Sukan ƙidaya su sa'ad da aka shigo da su, da sa'ad da aka fitar da su.

29 Aka sa waɗansu su zama masu lura da kayayyakin Haikalin, da kayayyakin aiki na cikin Wuri Mai Tsarki, da lallausan gari, da ruwan inabi, da mai, da turare, da kayan yaji.

30 Waɗansu 'ya'yan firistoci, maza, suke harhaɗa kayan yaji.

31 Mattitiya, ɗaya daga cikin Lawiyawa, ɗan farin Shallum na iyalin Kora, shi ne mai lura da toya waina.

32 Waɗansu 'yan'uwansu Kohatawa suke lura da gurasar ajiyewa. Sukan shirya ta kowace Asabar.

33 Waɗannan su ne mawaƙa, da shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa, waɗanda suka zauna a ɗakunan Haikali, ba su yin wani aiki dabam, gama dare da rana suke yin aikinsu.

34 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa a zamaninsu, wato waɗanda suka zauna a Urushalima.

35 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a ciki, sunan matarsa Ma'aka,

36 ɗan farinsa kuma shi ne Abdon. Sa'an nan ga Zur, da Kish, da Ba'al, da Ner, da Nadab,

37 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya, da Miklot,

38 mahaifin Shimeya. Zuriyarsu ne suka zauna a Urushalima daura da 'yan'uwansu.

39 Ner ya haifi Kish, Kish kuma ya haifi Saul, Saul ya haifi Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet.

40 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika.

41 'Ya'yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz.

42 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza,

43 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel.

44 Azel yana da 'ya'ya maza guda shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Isma'ilu, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.

10

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa, Isra'ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa.

2 Filistiyawa suka kama Saul da 'ya'yansa maza, suka kashe Jonatan da Yishwi, da Malkishuwa.

3 Yaƙin ya tsananta wa Saul, maharba suka rutsa Saul, suka yi masa rauni.

4 Sai Saul ya ce wa mai ɗaukar makamansa, “Zare takobinka, ka kashe ni, don kada marasa kaciyan nan su zo su yi mini ba'a.” Amma mai ɗaukar makamai nasa bai yarda ba, gama yana jin tsoro ƙwarai. Saboda haka sai Saul ya zare takobinsa ya fāɗi a kansa.

5 Sa'ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya faɗi a kan takobinsa ya mutu.

6 Ta haka Saul ya mutu, shi da 'ya'yansa maza guda uku tare da dukan gidansa.

7 Sa'ad da dukan Isra'ilawa waɗanda suke zaune a kwari suka ga sojojin sun gudu, Saul kuma da 'ya'yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa suka zo suka zauna a wurin.

8 Kashegari, sa'ad da Filistiyawa suka tafi su kwashe waɗanda aka kashe, sai suka tarar da Saul da 'ya'yansa maza matattu a Dutsen Gilbowa.

9 Suka kuwa tuɓe tufafinsa, suka datse kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka aiki manzanni ko'ina a ƙasar Filistiyawa don su ba gumakansu da jama'arsu wannan albishir.

10 Sai suka ajiye kayan yaƙin Saul a gidan gumakansu, suka kuma rataye kansa a gidan gunkin nan, wato Dagon.

11 Sa'ad da mutanen Yabesh-gileyad suka ji irin abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,

12 sai dukan ƙarfafan mutanensu suka tafi suka ɗauki gawar Saul, da gawawwakin 'ya'yansa, suka kawo a Yabesh suka binne ƙasusuwansu a ƙarƙashin itacen oak cikin Yabesh. Suka yi azumi har kwana bakwai.

13 Haka nan Saul ya mutu saboda laifin da ya yi wa Ubangiji, gama bai kiyaye maganar Ubangiji ba, saboda kuma ya nemi shawara wurin masu mabiya.

14 Amma bai nemi Ubangiji ba. Domin haka Ubangiji ya kashe shi, ya ɗauki sarautar, ya ba Dawuda ɗan Yesse.

11

1 Dukan Isra'ilawa kuwa suka taru wurin Dawuda a Hebron, suka ce masa, “Mu ɗaya ne da kai.

2 Ko dā can lokacin da Saul yake sarauta, kai ne kake yi wa Isra'ilawa jagora zuwa yaƙi da komowa. Ubangiji Allahnka kuwa ya ce maka, ‘Za ka yi kiwon jama'ata, wato Isra'ilawa, ka kuma shugabance su.’ ”

3 Sai dattawan Isra'ilawa suka zo wurin sarki Dawuda a Hebron. Dawuda kuwa ya yi alkawari da su a Hebron a gaban Ubangiji, ake kuwa naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila bisa ga faɗar Ubangiji ta bakin Sama'ila.

4 Sarki Dawuda kuwa, tare da dukan Isra'ilawa, suka tafi Urushalima, wato Yebus inda Yebusiyawa suke zaune.

5 Sai mazaunan Yebus, suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka Dawuda ya ci Sihiyona, gari mai kagara, wato birnin Dawuda ke nan.

6 Sai Dawuda ya ce, “Duk wanda ya ci Yebusiyawa da fari shi ne zai zama babban shugaban sojoji.” Yowab ɗan Zeruya ne ya fara tafiya, domin wannan aka maishe shi shugaba.

7 Sa'an nan Dawuda ya zauna a kagara, don haka aka kira birnin, birnin Dawuda.

8 Sai ya rutsa birnin da gini tun daga Millo. Yowab kuma ya gyaggyara sauran birnin.

9 Dawuda ya yi ta ƙasaita gaba gaba saboda Ubangiji Mai Runduna yana tare da shi.

10 Waɗannan su ne shugabanni, wato manyan jarumawan Dawuda waɗanda suka goyi bayansa sosai a mulkinsa, tare da dukan Isra'ilawa waɗanda suka naɗa shi sarki bisa ga maganar Ubangiji a kan Isra'ilawa.

11 Wannan shi ne labarin manyan jarumawan Dawuda. Yashobeyam ɗan Bahakmone shi ne shugaban jarumawa talatin. Ya karkashe mutum ɗari uku da māshinsa baki ɗaya.

12 Na biye da shi shi ne Ele'azara ɗan Dodo, Ba'ahohiye, wanda yake ɗaya daga cikin manyan jarumawan nan uku.

13 Yana tare da Dawuda a Efes-dammin sa'ad da Filistiyawa suka taru wuri ɗaya don su yi yaƙi. Akwai wata gonar sha'ir a wurin, sai jama'a suka gudu daga gaban Filistiyawa.

14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha'ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya cece su, ya ba su babbar nasara.

15 Wata rana sai uku daga cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara zuwa dutsen Dawuda, a kogon Adullam, sa'ad da rundunar sojojin Filistiyawa suka kafa sansani a kwarin Refayawa.

16 Dawuda yana cikin kagara, sojojin Filistiyawa kuwa suna a Baitalami.

17 Sai Dawuda ya yi marmarin gida, ya ce, “Dā ma wani ya kawo mini ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami in sha!”

18 Sai uku ɗin suka kutsa kai, suka shiga sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami, suka ɗauka, suka kawo wa Dawuda, Dawuda kuwa bai sha ba, amma ya kwarara ruwan a ƙasa domin sadaka ga Ubangiji.

19 Sa'an nan ya ce, “Allah ya sawwaƙe mini da zan yi wannan abu a gabansa, da zan sha jinin waɗannan da suka sadaukar da rayukansu, gama sai da suka yi kasai da ransu, sa'an nan suka ɗebo ruwan.” Saboda haka bai sha ruwan ba. Manyan jarumawan nan uku ne suka aikata waɗannan abubuwa.

20 Abishai ɗan'uwan Yowab kuwa shi ne shugaban jarumawa talatin ɗin. Ya girgiza mashinsa, ya kashe mutum ɗari uku. Ya yi suna a cikin jarumawan nan talatin.

21 Cikin jarumawa talatin ɗin, shi ya shahara har ya zama shugabansu. Amma duk da haka bai kai ga jarumawan nan uku ba.

22 Benaiya ɗan Yehoyada, ɗan wani jarumi ne daga Kabzeyel, ya yi manyan ayyuka, ya kashe jarumawa biyu na Mowabawa. Sai ya gangara ya kashe zaki a cikin rami a ranar da ake yin dusar ƙanƙara.

23 Sai kuma ya kashe wani dogon Bamasare mai tsayi kamu biyar. Bamasaren yana da māshi mai kama da dirkar masaƙa a hannunsa, amma sai ya gangaro wurinsa da kulki a hannu, ya ƙwace māshin daga hannun Bamasaren, ya kashe shi da shi.

24 Waɗannan abubuwa Benaiya ɗan Yehoyada ya yi su, ya kuwa yi suna kamar manyan jarumawan nan uku.

25 Ya yi suna a cikin jarumawa talatin ɗin, amma bai kai ga jarumawan nan uku ba. Sai Dawuda ya sa shi ya zama shugaban matsaransa.

26 Waɗannan su ne manyan jarumawan sojoji. Asahel ɗan'uwan Yowab Elhanan ɗan Dodo daga Baitalami Shamma daga Harod Helez daga Felet Aira ɗan Ikkesha daga Tekowa Abiyezer daga Anatot Sibbekai daga Husha Ilai daga Aho Maharai daga Netofa Heled ɗan Ba'ana daga Netofa Ittayi ɗan Ribai daga Gibeya ta Biliyaminu Benaiya na Firaton Hurai daga rafuffuka kusa da Ga'ash Abiyel daga Araba Azmawet daga Bahurim Eliyaba daga Shalim 'Ya'yan Yashen, maza, daga Gizon Jonatan ɗan Shimeya daga Harod Ahiyam ɗan Sharar daga Harod Elifelet ɗan Ahasbai Hefer daga Mekara Ahaija daga Felet Hezro daga Karmel Nayarai ɗan Ezbai Yowel ɗan'uwan Natan Mibhar ɗan Hagri Zelek daga Ammon Naharai daga Biyerot (Mai riƙe wa Yowab ɗan Zeruya makamai) Aira da Gareb daga Yattir Uriya Bahitte Zabad ɗan Alai Adina ɗan Shiza (Shi ne shugaba a kabilar Ra'ubainu, yana da ƙungiyarsa mai soja talatin tare da shi) Hanan ɗan Ma'aka Yoshafat daga Mitna Uzziya daga Ashtera Shama da Yehiyel 'ya'yan Hotam, maza, daga Arower Yediyel da Yoha 'ya'yan Shimri, maza, daga Tiz Eliyel daga Mahawa Yeribai, da Yoshawiya 'ya'yan Elna'am, maza Itma daga Mowab Eliyel, da Obida, da Yawasiyel daga Zoba,

12

1 Mutane da yawa suka haɗa kai da Dawuda lokacin da yake a Ziklag, sa'ad da yake a takure saboda Saul ɗan Kish. Su ma suna cikin manyan jarumawan da suka taimake shi yaƙi. Dukansu gwanayen sojoji ne, suna iya su harba kibiya, ko su yi jifa da majajjawa da hannun dama ko da na hagu.

2 Su daga kabilar Biliyaminu ne, dangin Saul.

3 Waɗannan su ne shugabannin sojoji, Ahiyezer, da Yowash, 'ya'yan Shemaiya, maza, daga Gibeya Yeziyel, da Felet, 'ya'yan Azmawet, maza Beraka, da Yehu daga Anatot Ismaya daga Gibeyon babban jarumi ne a cikin jarumawan nan talatin, yana daga cikin shugabannin jarumawa talatin ɗin Irmiya, da Yahaziyel Yohenan, da Yozabad daga Gedera Eluzai, da Yerimot, da Be'aliya Shemariya, da Shefatiya daga Harif Elkana, da Isshiya, da Azarel Yowezer, da Yashobeyam daga iyalin Kora Yowela, da Zabadiya 'ya'ya maza na Yeroham na Gedor

4

5

6

7

8 Waɗannan su ne sunayen shahararru, ƙwararrun mayaƙa daga kabilar Gad, waɗanda suka haɗa kai da sojojin Dawuda, sa'ad da yake a kagara a hamada. Su gwanayen yaƙi da garkuwa da mashi ne. Fuskokinsu kamar na zakoki, saurinsu kamar bareyi a kan dutse.

9 Ga yadda aka lasafta su bisa ga matsayinsu, da Ezer, da Obadiya, da Eliyab, da Mishmanna, da Irmiya, da Attai, da Eliyel, da Yohenan, da Elzabad, da Irmiya, da Makbannai.

10

11

12

13

14 Waɗannan daga kabilar Gad shugabannin sojoji ne, waɗansu na mutum dubu, sauransu kuma ƙananan shugabanni ne waɗanda suke shugabancin sojoji ɗari.

15 Su ne waɗanda suka haye Urdun a watan fari na shekara, sa'ad da Kogin Urdun ɗin ya yi ambaliya. Suka kori waɗanda suke zaune a kwaruruka, na wajen gabas da yamma da kogin.

16 Sa'an nan waɗansu daga cikin mazajen Biliyaminu da na Yahuza, suka zo wurin Dawuda a kagararsa.

17 Sai Dawuda ya fito don ya tarye su, ya ce musu, “Idan da salama kuka zo wurina don ku taimake ni, to, zuciyata za ta zama ɗaya da taku, amma idan kun zo ne don ku bashe ni ga maƙiyana, to, Allah na kakanninmu ya duba ya shara'anta, da yake ba ni da laifi.”

18 Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Amasa wanda daga baya ya zama shugaban talatin ɗin, sai ya ce, “Muna tare da kai, ya Dawuda ɗan Yesse! Allah ya ba ka nasara tare da waɗanda suke tare da kai! Allah yana wajenka!” Sa'an nan Dawuda ya marabce su, ya maishe su shugabanni a sojojinsa.

19 Waɗansu sojoji daga Manassa, suka tafi wurin Dawuda sa'ad da yake fita tare da Filistiyawa don su yi yaƙi da Saul. Amma Dawuda bai tafi tare da su ba, domin sarakunan Filistiyawa sun yi shawara, suka sallame shi, don kada ya juya musu gindin baka, ya nemi sulhu a wurin shugabansu Saul, da kawunansu.

20 Sa'ad da yake komawa Ziklag sai sojojin Manassa suka zo wurinsa, wato su Adana, da Yozabad, da Yediyayel, da Maikel, da Yozabad, da Elihu, da Zilletai. A sojojin kabilar Manassa, waɗannan shugabannin sojoji ne na dubu dubu.

21 Suka kuwa taimaki Dawuda sa'ad da mahara take tasar masa, gama dukansu jarumawa ne sosai, su kuma shugabannin sojoji ne.

22 Kowace rana mutane suna ta zuwa wurin Dawuda don su taimake shi, har suka zama babbar runduna.

23 Horarrun sojoji da yawa suka haɗa kai da sojojin Dawuda a Hebron domin su taimaki Dawuda da yaƙi, su mai da shi sarki maimakon Saul, kamar yadda Ubangiji ya alkawarta. Ga yadda yawansu yake.

24 Mutanen Yahuza waɗanda suke riƙe da garkuwoyi da māsu don yaƙi, mutum dubu shida da ɗari takwas (6,800).

25 Na kabilar Saminu jarumawa mayaƙa mutum dubu bakwai da ɗari (7,100).

26 Na kabilar Lawi akwai mutum dubu huɗu da ɗari shida (4,600).

27 Akwai kuma Yehoyada wanda shi ne shugaban gidan Haruna, yana da mutum dubu uku da ɗari bakwai (3,700).

28 Na dangin Zadok wanda yake jarumi, saurayi, akwai shugabannin sojoji ashirin da biyu.

29 Na kabilar Biliyaminu, wato kabilar Saul, akwai mutum dubu uku (3,000). (Har yanzu yawancin mutanen Biliyaminu ba su daina bin gidan Saul ba.)

30 Na kabilar Ifraimu akwai mutum dubu ashirin da ɗari takwas (20,800), jarumawa ne sosai, waɗanda suka shahara a danginsu.

31 Na rabin kabilar Manassa wajen yamma akwai mutum dubu goma sha takwas (18,000) waɗanda aka zaɓa domin su zo su naɗa Dawuda ya zama sarki.

32 Na kabilar Issaka akwai shugabanni ɗari biyu, waɗanda suka gane da halin da ake ciki, da abin da ya kamata Isra'ila ya yi. Su ne suke shugabancin 'yan'uwansu.

33 Na kabilar Zabaluna akwai mutum dubu hamsin (50,000) suna da kowane irin kayan yaƙi. Suka zo domin su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya.

34 Na kabilar Naftali akwai shugabannin sojoji dubu ɗaya (1,000) tare da sojoji dubu talatin da dubu bakwai (37,000) masu garkuwoyi da māsu.

35 Na kabilar Dan mutum dubu ashirin da takwas da ɗari shida (28,600).

36 Na kabilar Ashiru, sojoji dubu arba'in (40,000) suka fito da shirin yaƙi.

37 Kabilan gabashin Urdun, wato kabilar Ra'ubainu, da Gad, da rabin kabilar Manassa, su dubu ɗari da dubu ashirin ne (120,000), suna da kowane irin kayan yaƙi.

38 Duk waɗannan mayaƙa sun zo Hebron a shirye, da zuciya ɗaya don su naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila duka. Haka kuma dukan sauran Isra'ilawa suka goyi baya da zuciya ɗaya a naɗa Dawuda ya zama sarki.

39 Suka yi kwana uku tare da Dawuda, suka yi ta ci suna sha, gama 'yan garin sun shirya wata liyafa dominsu.

40 Waɗanda kuma suke kusa da su har zuwa Issaka, da Zabaluna da Naftali, sun kawo abinci a kan jakuna, da raƙuma, da alfadarai, da takarkarai. Suka kawo abinci mai yawa, wato gāri da kauɗar ɓaure da nonnan busassun 'ya'yan inabi, da ruwan inabi, da man zaitun. Suka kuma kawo shanu da tumaki domin yanka a ci. Duk an yi wannan domin a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra'ila.

13

1 Sa'an nan Dawuda ya yi shawara da shugabannin sojoji na dubu dubu da na ɗari ɗari, da kowane shugaba.

2 Ya kuma yi magana da dukan taron Isra'ilawa, ya ce, “Idan kun ga ya yi kyau, idan kuma nufin Ubangiji Allahnmu ne, to, bari mu aika a ko'ina wurin 'yan'uwanmu waɗanda aka rage a ƙasar Isra'ila, mu kuma aika wa firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a biranensu masu makiyaya domin su zo wurinmu.

3 Sa'an nan mu ɗauko akwatin alkawari na Allahnmu mu kawo shi wurinmu, gama mun ƙyale shi tun zamanin Saul.”

4 Jama'a kuwa suka amince da shawarar, suka yarda kuma a yi haka ɗin.

5 Haka fa, Dawuda ya tattara dukan Isra'ilawa wuri ɗaya, daga Shihor ta Masar, har zuwa mashigin Hamat domin a kawo akwatin alkawari na Allah daga Kiriyat-yeyarim.

6 Sai Dawuda tare da dukan Isra'ilawa, suka haura zuwa Ba'al, wato Kiriyat-yeyarim ta Yahuza, domin su ɗauko akwatin alkawarin Allah daga can, inda ake kira bisa sunan Ubangiji, wanda kuma yake zaune a wurin kerubobi.

7 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabon keken shanu daga gidan Abinadab. Uzza da Ahiyo suka kora keken shanun.

8 Sai Dawuda da dukan Isra'ilawa suka yi rawa da iyakar ƙarfinsu a gaban Allah, suna raira waƙoƙi suna kaɗa, garayu, da molaye, da ganguna, da kuge, suna busa ƙaho.

9 Sa'ad da suka kai masussukar Kidon, sai Uzza ya miƙa hannunsa don ya riƙe akwatin alkawarin saboda gargada.

10 Sai Ubangiji ya husata da Uzza, ya buge shi, ya mutu nan take a gaban Allah, saboda ya miƙa hannunsa ya kama akwatin alkawari.

11 Sai Dawuda ya ɓata ransa saboda da Ubangiji ya hukunta Uzza da fushi, sai ya sa wa wannan wuri suna Feresa-uzza, wato hukuncin Uzza.

12 Sa'an nan Dawuda ya ji tsoron Allah, ya ce, “Ƙaƙa zan kawo akwatin alkawarin Allah a gidana?”

13 Don haka Dawuda bai kai akwatin alkawarin zuwa cikin birninsa ba, amma ya raɓa da shi zuwa gidan Obed-edom wanda yake daga Gat.

14 Akwatin alkawarin Allah kuwa ya kasance a gidan Obed-edom har wata uku. Ubangiji kuwa ya sa wa iyalin Obed-edom da dukan abin da yake da shi albarka.

14

1 Sai Hiram Sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda, su kai masa itatuwan al'ul, da magina, da massassaƙa domin a gina masa fāda.

2 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya tabbatar masa da sarautar Isra'ila, mulkinsa kuwa ya ɗaukaka ƙwarai saboda jama'arsa, Isra'ila.

3 Dawuda kuwa ya ƙara auren waɗansu mata a Urushalima, suka haifi 'ya'ya mata da maza.

4 Ga sunayen 'ya'yan da aka haifa masa a Urushalima, Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu,

5 da Ibhar, da Elishuwa, da Elifelet,

6 da Noga, da Nefeg, da Yafiya,

7 da Elishama, da Eliyada, da Elifelet.

8 Sa'ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila duka, sai dukan Filistiyawa suka haura, suna neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya fita domin ya yi yaƙi da su.

9 Filistiyawa suka iso kwarin Refayawa suka fara fatali da shi.

10 Sai Dawuda ya roƙi Allah, ya ce, “In tafi in yi yaƙi da Filistiyawa? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji kuwa ya amsa masa, ya ce, “Ka haura, gama zan bashe su a hannunka.”

11 Sai suka haura zuwa Ba'al-ferazim, Dawuda kuwa ya ci su da yaƙi a wurin. Sai ya ce, “Allah ya raraki maƙiyana ta hannuna, kamar yadda ruwa yakan rarake ƙasa.” Don haka aka sa wa wurin suna Ba'al-ferazim.

12 Filistiyawa suka gudu suka bar gumakansu a wurin. Dawuda kuwa ya yi umarni, aka ƙone su duka.

13 Filistiyawa kuma suka sāke kawo yaƙi a kwarin.

14 Dawuda ya sāke yin roƙo ga Allah, Allah kuwa ya ce masa, “Kada ka hau zuwa wurinsu, ka kewaye ka ɓullo musu ta baya daura da itatuwan tsamiya.

15 Sa'ad da ka ji motsi kamar na tafiyar sojoji a bisa itatuwan tsamiya, sai ka fita ka yi yaƙi, gama Allah ya wuce ta gabanka don ya bugi sojojin Filistiyawa.”

16 Dawuda fa ya yi daidai yadda Ubangiji ya umarce shi. Suka bugi sojojin Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

17 Sunan Dawuda kuma ya kai ko'ina cikin dukan ƙasashe. Ubangiji kuwa ya sa dukan al'ummai su ji tsoron Dawuda.

15

1 Dawuda kuwa ya gina wa kansa gidaje a birninsa, ya kuma kafa alfarwa domin akwatin alkawari na Allah.

2 Sai Dawuda ya ce, “Kada wani ya ɗauki akwatin alkawari na Allah sai Lawiyawa kaɗai, gama su ne Ubangiji ya zaɓa domin su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su kuma yi masa hidima har abada.”

3 Saboda haka Dawuda ya tattara Isra'ilawa duka a Urushalima don a kawo akwatin alkawarin Ubangiji a wurinsa, inda aka riga aka shirya masa.

4 Dawuda kuma ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya, tare kuma da Lawiyawa.

5 Waɗanda aka tattaro ke nan, daga iyalin Kohat su ɗari da shirin ne. Uriyel shi ne shugabansu.

6 Daga iyalin Merari su ɗari biyu da ashirin, Asaya ne shugabansu.

7 Daga iyalin Gershon ɗari da talatin, Yowel ne shugabansu.

8 Daga iyalin Elizafan ɗari biyu, Shemaiya ne shugabansu.

9 Daga iyalin Hebron su tamanin, Eliyel ne shugabansu.

10 Daga iyalin Uzziyel ɗari da goma sha biyu, Amminadab ne shugabansu.

11 Sa'an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyata firistoci, da Lawiyawa, wato Uriyel, da Asaya, da Yowel, da Shemaiya, da Eliyel, da Amminadab,

12 ya ce musu, “Ku ne shugabanni na gidajen kakanninku, Lawiyawa. Sai ku tsarkake kanku da 'yan'uwanku domin ku iya kawo akwatin alkawarin Allah na Isra'ila a inda na shirya masa.

13 Gama Ubangiji Allahnmu ya fashe fushinsa a kanmu saboda ba ku ne kuka ɗauke shi a karo na farko ba, saboda kuma ba mu yi masa sujada kamar yadda aka umarta ba.”

14 Sa'an nan firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji Allah na Isra'ila.

15 Lawiyawa fa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah a bisa sandunansa a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.

16 Dawuda ya umarci shugabannin Lawiyawa su sa 'yan'uwansu mawaƙa su riƙa raira waƙa da murna, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, da molaye, da garayu, da kuge masu amon gaske.

17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berikiya daga cikin 'yan'uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kishi.

18 Daga cikin 'yan'uwansu, har yanzu aka zaɓi mataimakansu, wato Zakariya, da Ben, da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Unno, da Eliyab, da Benaiya, da Ma'aseya, da Mattitiya, da Elifelehu, da Mikneya, da Obed-edom, da Yehiyel, da masu tsaron ƙofofi.

19 Haka aka zaɓi mawaƙa, wato Heman, da Asaf, da Etan don su buga kuge na tagulla.

20 Su Zakariya, da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Unno, da Eliyab, da Ma'aseya, da Benaiya, su ne masu kaɗa molaye da murya a sama.

21 Su Mattitiya, da Elifelehu, da Mikneya, da Obed-edom, da Yehiyel, da Azaziya suke ja da garayu da murya ƙasa-ƙasa.

22 Kenaniya shugaban Lawiyawa shi ne yake bi da waƙoƙi domin shi gwani ne.

23 Berikiya da Elkana su ne masu tsaron ƙofa ta akwatin alkawari.

24 Sai Shebaniya, da Yehoshafat, da Netanel, da Amasai, da Zakariya, da Benaiya, da Eliyezer, firistoci, suka yi ta busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-edom da Yehiya su ne kuma masu tsaron ƙofar akwatin alkawari.

25 Haka Dawuda, da dattawan Isra'ilawa, da shugabannin dubu dubu, suka tafi da murna domin su ɗauko akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-edom.

26 Saboda Allah ya taimaki Lawiyawa waɗanda suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi hadaya da bijimai bakwai da raguna bakwai.

27 Dawuda yana saye da kyakkyawar taguwa ta lilin tare da Lawiyawa duka waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, da mawaƙa, da Kenaniya shugaban mawaƙan. Dawuda kuma ya sa falmaran ta lilin.

28 Da haka fa Isra'ilawa duka suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, suna ta sowa, suna ta busa ƙaho, suna kaɗa kuge da molaye, da garayu.

29 Sa'ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shigo birnin Dawuda, sai Mikal 'yar Saul ta leƙa ta taga, ta ga sarki Dawuda yana ta rawa, yana murna, sai ta ji ya saƙale mata a zuci.

16

1 Suka fa shigo da akwatin alkawarin Allah, suka ajiye shi a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa masa, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama a gaban Allah.

2 Da Dawuda ya gama miƙa hadayar ƙonawa da ta salama, sai ya sa wa jama'a albarka da sunan Ubangiji.

3 Ya kuma rarraba wa Isra'ilawa mata da maza, gurasa, da gunduwar nama, da kauɗar zabibi.

4 Ya kuma sa waɗansu Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka Ubangiji Allah na Isra'ila, su gode masa, su kuma yabe shi.

5 Asaf shi ne shugaba, na biye da shi su ne Zakariya da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Mattitiya, da Eliyab, da Benaiya, da Obed-edom, da Yehiyel, waɗanda za su kaɗa molaye da garayu. Asaf kuwa shi ne mai kaɗa kuge.

6 Benaiya da Yahaziyel firistoci, su ne za su riƙa busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah.

7 A wannan lokaci ne Dawuda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su riƙa raira waƙoƙin yabo ga Ubangiji.

8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!

9 Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi, Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!

10 Ku yi murna saboda mu nasa ne, Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

11 Ku je wurin Ubangiji neman taimako, Ku tsaya a gabansa koyaushe.

12 Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki, Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

13 Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu.

14 Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu, Umarnansa domin dukan duniya ne.

15 Zai cika alkawarinsa har abada, Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

16 Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim, Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

17 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila, Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,

18 “Zan ba ka ƙasar Kan'ana, Za ta zama mallakarka.”

19 Jama'ar Ubangiji kima ne, Baƙi ne kuwa a ƙasar.

20 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa, Daga wannan mulki zuwa wancan.

21 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba, Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

22 Ya ce, “Kada ku taɓa bayina, zaɓaɓɓu, Kada ku cuci annabawana!”

23 Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku dukan duniya, Ku yi shelar albishir na ceton da ya yi mana kowace rana.

24 Ku yi shelar ɗaukakarsa ga al'ummai, Da ayyukansa masu girma ga dukan mutane,

25 Ubangiji da girma yake, wajibi ne mu yabe shi, Dole mu yi tsoronsa fiye da dukan alloli.

26 Gama allolin dukan sauran al'umma gumaka ne, Amma Ubangiji shi ne ya halitta sammai.

27 Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi, Iko da farin ciki sun cika haikalinsa.

28 Ku yi yabon Ubangiji, ku dukan mutanen duniya, Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa!

29 Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja, Kuna kawo sadaka, kuna zuwa Haikalinsa. Ku rusuna a gaban Mai Tsarki da sahihiyar zuciya,

30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ku dukan duniya! Hakika duniya ta kahu sosai, ba za ta jijjigu ba.

31 Duniya da sararin sama, ku yi farin ciki! Ku faɗa wa al'ummai, Ubangiji shi ne sarki.

32 Ki yi ruri, ke teku, da dukan abin da yake cikinki, Ka yi farin ciki, kai saura da dukan abin da yake cikinka.

33 Itatuwa a jeji za su yi sowa domin murna Sa'ad da Ubangiji zai zo ya yi mulki a duniya.

34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce!

35 Ku ce masa, “Ka cece mu, ya Allah Mai Cetonmu, Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga al'ummai, Domin mu gode maka, Mu kuma yabi sunanka mai tsarki.”

36 Ku yabi Ubangiji Allah na Isra'ila! Ku yi ta yabonsa har abada abadin! Sa'an nan dukan jama'a suka ce, “Amin, Amin,” suka yabi Ubangiji.

37 Dawuda ya sa Asaf tare da 'yan'uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji domin a yi hidima kullayaumin a gaban akwatin alkawarin kamar yadda aka bukaci a yi kowace rana.

38 Akwai kuma masu tsaron ƙofofi, wato Obed-edom ɗan Yedutun tare da 'yan'uwansa, su sittin da takwas, da Hosa.

39 Sai ya bar Zadok firist da 'yan'uwansa firistoci a wurin zama na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon.

40 Kowace safiya da maraice suna miƙa hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a bisa bagaden ƙona hadaya, kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, waɗanda ya ba Isra'ilawa.

41 Tare da su kuma akwai Heman, da Yedutun, da sauran waɗanda aka zaɓa musamman domin su yi godiya ga Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa.

42 Heman da Yedutun suna lura da ƙaho, da kuge, da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin raira waƙoƙin yabo ga Allah. 'Ya'yan Yedutun, maza, su aka ba aikin tsaron ƙofa.

43 Sa'an nan dukan jama'a suka watse, kowa ya koma gidansa, Dawuda kuma ya koma gidansa, ya sa wa iyalinsa albarka.

17

1 Sa'ad da Dawuda yake zaune a fādarsa, sai ya ce, wa annabi Natan, “Ga shi, ni ina zaune a cikin gidan da aka yi da itacen al'ul, amma akwatin alkawarin Ubangiji yana cikin alfarwa.”

2 Natan ya amsa masa ya ce, “Ka yi duk abin da zuciyarka ta ɗauka, gama Allah yana tare da kai.”

3 Amma a wannan dare Ubangiji ya yi magana da Natan, ya ce,

4 “Ka tafi, ka faɗa wa bawana, Dawuda, cewa ni Ubangiji na ce, ‘Ba za ka gina mini ɗakin da zan zauna a ciki ba.

5 Gama tun ranar da na fito da Isra'ilawa ban taɓa zama a cikin ɗaki ba, amma daga alfarwa zuwa alfarwa, daga wannan mazauni kuma zuwa wancan.

6 A dukan wuraren da na tafi tare da Isra'ilawa, ban taɓa faɗa wa wani daga cikin hakiman Isra'ila, waɗanda na ba da umarni su yi kiwon jama'ata, cewa su gina mini ɗaki da itacen al'ul ba.’

7 “Saboda haka fa sai ka faɗa wa bawana Dawuda cewa, ‘Ni Ubangiji Mai Runduna, na ɗauko ka daga kiwon tumaki domin ka zama sarkin jama'ata Isra'ila.

8 Na kuwa kasance tare da kai a duk inda ka tafi, na kuma hallaka maƙiyanka a gabanka. Zan sa ka shahara kamar waɗanda suka shahara a duniya.

9 Zan zaɓo wa jama'ata, wato Isra'ila, wuri, zan dasa su, su zauna a wuri na kansu, don kada a sāke damunsu, kada kuma masu mugunta su ƙara lalata su kamar dā,

10 tun lokacin da na sa hakimai su shugabanci jama'ata Isra'ila. Zan rinjayi dukan maƙiyanka. Banda wannan kuma na yi alkawari zan ci dukan maƙiyanka, in mallakar da su ga zuriyarka.

11 Sa'ad da lokacinka ya yi da za ka mutu, zan ta da ɗaya daga cikin zuriyarka, ɗaya daga cikin 'ya'yanka maza, zan kafa mulkinsa.

12 Shi ne zai gina mini Haikali, zan kafa gadon sarautarsa har abada.

13 Ni zan zama uba a gare shi, shi kuwa ya zama ɗa a gare ni, ba zan kawar masa da madawwamiyar ƙaunata ba, kamar yadda na kawar da ita daga wanda ya riga ka sarauta.

14 Zan zauna da shi a gidana da mulkina har abada. Gadon sarautarsa kuwa zai kahu har abada.’ ”

15 Natan kuwa ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.

16 Sarki Dawuda kuwa ya shiga alfarwa, ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, mene kuma gidana da za ka yi mini haka?

17 Amma wannan ƙanƙanen abu ne a gare ka, ya Allah. Ka kuma yi alkawari, cewa za ka tsawaita kwanakin zuriyar bawanka, ka ɗauke ni kamar ni wani babban mutum ne, ya Ubangiji Allah.

18 Me kuma ni Dawuda zan ƙara ce maka, a kan girman da ka ba bawanka? Gama ka san bawanka.

19 Ya Ubangiji, saboda bawanka ne, da kuma bisa ga yardar ranka, ka aikata wannan babban al'amari, domin ka bayyana waɗannan manyan abubuwa.

20 Ya Ubangiji, ba wani kamarka, ba kuma wani Allah sai kai, bisa ga duk abin da muka ji da kunnuwanmu.

21 Wace al'umma ce take a duniyar nan kamar jama'arka, Isra'ila, wadda kai, Allah, ka je ka fanshe ta, ta zama jama'arka, domin ka yi suna ta wurin manyan abubuwa masu banmamaki, kamar yadda ka kori al'ummai a gaban jama'arka, wadda ka fansa daga Masar?

22 Gama ka mai da jama'ar Isra'ila ta zama taka har abada. Kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.

23 “Yanzu dai, ya Ubangiji, bari maganar da ka yi wa bawanka da gidansa ta tabbata har abada, ka kuma aikata yadda ka faɗa.

24 Bari sunanka ya kahu, ya ɗaukaka har abada, a riƙa cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna, shi ne Allah na Isra'ilawa.’ Gidan bawanka Dawuda kuma ya kahu a gabanka.

25 Gama kai, ya Allahna, ka riga ka bayyana wa bawanka, cewa za ka sa zuriyata su zama sarakuna, don haka ne, ni bawanka na sami ƙarfin halin yin wannan addu'a gare ka.

26 Yanzu dai ya Ubangiji, kai Allah ne, ka riga ka yi alkawarin wannan kyakkyawan abu gare ni, bawanka.

27 Ina roƙonka, ka sa wa gidan bawanka albarka, domin ya dawwama a gabanka, gama ya Ubangiji, abin da ka sa wa albarka, ya albarkatu ke nan har abada.”

18

1 Bayan haka kuma Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya mallake su, ya ƙwace Gat da garuruwanta daga hannunsu.

2 Ya kuma ci Mowab da yaƙi, Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji.

3 Dawuda kuma ya ci Hadadezer, Sarkin Zoba, da yaƙi a Hamat, sa'ad da ya tafi ya kafa mulkinsa a Kogin Yufiretis.

4 Sai Dawuda ya ƙwace karusai dubu (1,000), da mahayan dawakai dubu bakwai (7,000), da sojojin ƙasa dubu ashirin (20,000) daga gare shi. Dawuda kuma ya yanyanke agarar dawakan da suke jan karusai, amma ya bar waɗansu dawakai daga cikinsu waɗanda suka isa jan karusai ɗari.

5 Sa'ad da Suriyawa daga Dimashƙu suka zo don su taimaki Hadadezer Sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe mutum dubu ashirin da dubu biyu (22,000) daga cikin Suriyawan.

6 Sa'an nan Dawuda ya sa ƙungiyoyin sojoji a Suriya ta Dimashƙu, Suriyawa kuma suka zama bayin Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. Ubangiji kuwa ya taimaki Dawuda duk inda ya tafi.

7 Dawuda kuma ya ƙwato garkuwoyi na zinariya waɗanda barorin Hadadezer suke ɗauke da su, ya kawo su Urushalima.

8 Dawuda kuma ya kwaso tagulla mai yawan gaske daga Beta da Berotayi, biranen Hadadezer. Da su ne Sulemanu ya yi kwatarniya, da ginshiƙai, da kayayyakin Haikali.

9 Sa'ad da Toyi, Sarkin Hamat, ya ji an ce Dawuda ya riga ya ci nasara a kan sojojin Hadadezer, Sarkin Zoba,

10 sai ya aiki Adoniram ɗansa wurin sarki Dawuda, don ya gaishe shi, ya kuma yabe shi saboda ya yi yaƙi da Hadadezer, har ya ci shi, gama Hadadezer yakan yi yaƙi da Toyi. Adoniram kuwa ya kawo kayayyaki iri iri na zinariya, da na azurfa, da na tagulla.

11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan ga Ubangiji, tare da azurfa da zinariya waɗanda ya kwaso daga al'umman da ya ci, wato Edom, da Mowab, da mutanen Ammon, da na Filistiya, da na Amalek.

12 Abishai ɗan Zeruya kuma ya ci nasara a kan Edomawa, mutum dubu goma sha takwas (18,000) a Kwarin Gishiri.

13 Sai ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan Edomawa kuma suka zama bayin Dawuda. Ubangiji kuwa ya taimaki Dawuda duk inda ya tafi.

14 Da haka Dawuda ya yi mulki bisa dukan Isra'ila. Ya yi wa dukan jama'arsa adalci da gaskiya.

15 Yowab ɗan Zeruya shi ne shugaban sojoji, Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci.

16 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Seraiya kuwa shi ne magatakarda.

17 Benaiya ɗan Yehoyada shi ne shugaban Keretiyawa da Feletiyawa, wato matsara. 'Ya'yan Dawuda, maza, su ne manyan ma'aikata na kusa da shi.

19

1 Bayan haka kuma Nahash Sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa kuma ya gāji sarautarsa.

2 Sa'an nan Dawuda ya ce, “Zan nuna alheri ga Hanun ɗan Nahash, gama tsohonsa ya nuna mini alheri.” Don haka Dawuda ya aiki manzanni su yi wa Hanun ta'aziyyar rasuwar tsohonsa. Fādawan Dawuda suka zo ƙasar Ammon wurin Hanun, domin su yi masa ta'aziyya.

3 Amma hakiman Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama tsohonka ne da ya aiko manzanni su yi maka ta'aziyya? Fādawansa sun zo wurinka ne don su leƙi asirin ƙasar, su bincike ta, su ci ta da yaƙi.”

4 Hanun kuwa ya kama fādawan Dawuda, ya aske gyammansu, ya yanyanke rigunansu a tsaka daga wajen kwankwaso, sa'an nan ya sallame su.

5 Waɗansu mutane kuwa suka je suka faɗa wa Dawuda abin da ya sami mutanen. Sai ya aiko a tarye su, gama an ƙasƙanta mutanen nan da gaske. Sai sarki ya ce, “Ku zauna a Yariko, har lokacin da gyammanku suka tohu sa'an nan ku iso.”

6 Sa'ad da Ammonawa suka ga sun mai da kansu abin ƙi ga Dawuda, sai Hanun da Ammonawa suka aika da talanti dubu (1,000) na azurfa don su yi ijara da karusai da mahayan dawakai daga Mesofotamiya, da jihohin Ma'aka ta Suriya, da Zoba.

7 Suka yi ijarar karusai dubu talatin da dubu biyu (32,000), da Sarkin Ma'aka, tare da jama'arsa. Suka zo suka kafa sansani a gaban Medeba. Ammonawa kuwa suka tattaru daga biranensu don su yi yaƙi.

8 Da Dawuda ya ji labari, sai ya aiki Yowab tare da dukan sojoji, ƙarfafan mutane.

9 Sai Ammonawa suka fito suka jā dāga a ƙofar birninsu. Sarakunan da suka zo suka ware suka zauna a saura.

10 Da Yowab ya ga an kafa masa yaƙi gaba da baya, sai ya zaɓi waɗansu jarumawa na gaske a Isra'ila, ya sa su su kara da Suriyawa.

11 Sa'an nan ya sa sauran sojoji a hannun Abishai ɗan'uwansa. Suka jā dāgar yaƙi da Ammonawa.

12 Yowab ya ce wa Abishai, “Idan Suriyawa sun fi ƙarfina, to, sai ka taimake ni, amma idan Ammonawa sun fi ƙarfinka, to, sai in taimake ka.

13 Mu yi ƙarfin hali, mu yi jaruntaka saboda jama'armu da biranen Allahnmu. Bari Ubangiji ya yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”

14 Yowab da jama'ar da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Suriyawa, sai Suriyawa suka gudu daga gabansu.

15 Da Ammonawa suka ga Suriyawa sun gudu, su ma suka gudu daga gaban Abishai, ɗan'uwan Yowab, suka shiga birni. Sa'an nan Yowab ya komo Urushalima.

16 Da Suriyawa suka ga Isra'ilawa sun ci su da yaƙi sai suka aiki manzanni suka kira Suriyawa waɗanda suke hayin kogi. Shobak shugaban sojojin Hadadezer ne yake shugabantarsu.

17 Sa'ad da aka faɗa wa Dawuda, sai ya tattara Isra'ilawa duka ya haye Urdun, ya zo wurinsu, ya jā dāga don ya yi yaƙi da su. Aka fara gabza yaƙi,

18 sai Suriyawa suka gudu a gaban Isra'ilawa, Dawuda ya karkashe Suriyawa, mutum dubu bakwai (7,000) masu karusai, da sojojin ƙasa dubu arba'in (40,000). Ya kuma kashe Shobak shugaban sojojin.

19 Da barorin Hadadezer suka ga Isra'ilawa sun ci su da yaƙi, sai suka ƙulla zumunci da Dawuda, suka bauta masa. Saboda haka Suriyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.

20

1 Da bazara, lokacin da sarakuna sukan fita su yi yaƙi, sai Yowab ya tafi da sojoji suka lalatar da ƙasar Ammonawa. Suka tafi, suka kewaye Rabba da yaƙi. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima. Yowab ya bugi Rabba ya yi nasara da ita.

2 Sai Dawuda ya ciro kambi daga kan sarkinsu, sai ya iske nauyinsa talanti ɗaya na zinariya ne, akwai kuma duwatsu masu daraja a cikinsa. Dawuda ya sa kambin a kansa. Ya kwaso ganima da yawa a birnin.

3 Ya kuma fito da mutanen da suke ciki, ya yanyanka su da zartuna da makamai masu kaifi, da gatura. Haka Dawuda ya yi wa dukan biranen Ammonawa. Sa'an nan Dawuda da dukan jama'a suka koma Urushalima.

4 Bayan wannan kuma, sai yaƙi ya tashi a Gat tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa, sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar ƙattin nan. Aka ci Filistiyawa.

5 Yaƙi kuma ya sake tashi tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa, sai Elhanan ɗan Yayir, ya kashe Lahmi ɗan'uwan Goliyat daga Gat, wanda yake gorar mashinsa ta yi ya dirkar masaƙa.

6 Yaƙi ya sāke tashi a Gat, inda wani cindo, ƙaton mutum yake. Yana da yatsotsi ashirin da huɗu, wato a kowane hannu yana da yatsa shida, haka nan kuma a kowace ƙafarsa. Shi kuma daga zuriyar ƙattin nan ne.

7 Sa'ad da ya yi wa mutanen Isra'ila ba'a, sai Jonatan ɗan Shimeya, wato ɗan'uwan Dawuda, ya kashe shi.

8 Waɗannan uku ne Dawuda da jama'arsa suka kashe daga zuriyar ƙattin na Gat.

21

1 Shaiɗan ya tashi gaba da Isra'ila, sai ya iza Dawuda ya ƙidaya Isra'ilawa.

2 Dawuda fa ya ce wa Yowab da sauran shugabannin jama'a, “Ku tafi, ku ƙidaya jama'ar Isra'ila tun daga Biyer-sheba har zuwa Dan, ku kawo mini labari don in san yawansu.”

3 Amma Yowab ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya yawan jama'arsa har sau ɗari bisa kan yadda suke a yanzu! Ranka ya daɗe, ya sarki, ashe, dukkansu ba naka ba ne? Me zai sa shugabana ya so a yi haka? Me zai sa ya zama sanadin tuntuɓe ga mutanen Isra'ila?”

4 Duk da haka, sarki ya sa Yowab ya bi umarninsa. Sai Yowab ya tashi, ya bibiya ƙasar Isra'ila duka, sa'an nan ya komo Urushalima.

5 Yowab ya kawo wa Dawuda adadin yawan mutanen. Jimillar dukan Isra'ila zambar dubu ne da dubu ɗari (1,100,000) waɗanda za su iya yaƙi. Jimillar mutanen Yahuza kuwa dubu ɗari huɗu da dubu saba'in ne (470,000) waɗanda suka isa zuwa yaƙi.

6 Amma bai ƙidaya Lawiyawa da mutanen Biliyaminu ba, domin Yowab bai ji daɗin umarnin sarki ba.

7 Allah bai ji daɗin wannan al'amari ba, don haka sai ya bugi Isra'ila.

8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai saboda abin nan da na aikata. Amma ina roƙonka ka gafarta mini laifina, gama na yi aikin wauta ƙwarai da gaske.”

9 Sa'an nan Ubangiji ya yi magana da Gad, annabin Dawuda, ya ce,

10 “Je ka ka faɗa wa Dawuda, ka ce, ‘Ubangiji yana so ka zaɓi ɗaya daga cikin abu uku, wanda zai yi maka.’ ”

11 Gad kuwa ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ka zaɓa,

12 ko shekara uku na yunwa, ko kuwa ka sha ɗibga a hannun maƙiyanka har wata uku, maƙiyanka su yi ta fafararka, ko kwana uku na takobin Ubangiji, wato annoba ke nan da zai aukar wa ƙasar, mala'ikan Ubangiji zai yi ta hallakarwa ko'ina a ƙasar Isra'ila. Yanzu fa, sai ka yi tunani, ka ba ni amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”

13 Dawuda kuwa ya ce wa Gad, “Na shiga uku, gara in fāɗa a hannun Ubangiji, gama shi mai yawan jinƙai ne, kada ka bar ni in faɗa a hannun mutum.”

14 Saboda haka Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra'ila. Mutum dubu saba'in (70,000) na Isra'ila suka mutu.

15 Allah ya aiko mala'ikansa don ya hallaka Urushalima, amma sa'ad da yake gab da hallaka ta, sai Ubangiji ya gani, ya janye shirin annobar, ya ce wa mala'ikan hallakarwa, “Ya isa, janye hannunka.” Mala'ikan Ubangiji kuwa na tsaye kusa da masussukar Arauna Bayebuse.

16 Dawuda ya ɗaga idonsa, sai ya ga mala'ikan Ubangiji yana tsakanin sama da ƙasa, da takobinsa a zare a hannunsa a kan Urushalima. Sa'an nan Dawuda tare da dattawa suka fāɗi rubda ciki, suna saye da tufafin makoki.

17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ai, ni ne na ba da umarni a ƙidaya jama'ar. Hakika, ni na yi zunubi, na kuwa aikata mummunan abu, amma waɗannan talakawa fa, me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, ka bar hannunka ya yi gāba da ni da gidan tsohona, amma kada ka yi gāba da jama'arka, har da za ka aukar musu da annoba.”

18 Mala'ikan Ubangiji ya umarci Gad ya faɗa wa Dawuda ya haura, ya gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse.

19 Dawuda kuwa ya haura kamar yadda Gad ya faɗa masa da sunan Ubangiji.

20 Arauna yana cikin sussukar alkama, sai ya waiwaya ya ga mala'ika. 'Ya'yansa maza su huɗu kuwa, waɗanda suke tare da shi suka ɓuya.

21 Sa'ad da Dawuda ya tafi wurin Arauna, da Arauna ya ga Dawuda, sai ya fito daga masussukar ya tafi ya fāɗi rub da ciki a gaban Dawuda ya gaishe shi.

22 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ba ni wannan masussuka don in gina wa Ubangiji bagade. Ka sayar mini da masussukar a bakin cikakken kuɗinta, domin a kawar wa jama'a da annobar.”

23 Arauna ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa, na ba ka, sai ka yi abin da kake so da ita, ranka ya daɗe. Zan kuma ba da bijimai domin hadayu na ƙonawa, in ba da keken sussuka domin itacen wuta, in kuma ba da alkama don hadaya ta gari. Zan ba ka waɗannan duka.”

24 Amma sarki Dawuda ya ce wa Arauna, “A'a, zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai in ba Ubangiji ba, ba kuwa zan miƙa masa hadayu na ƙonawa da abin da ban biya ba.”

25 Sai Dawuda ya biya Arauna shekel ɗari shida na zinariya domin masussukar.

26 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama. Sai ya yi roƙo ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wutar da ta sauko daga sama a bisa bagaden hadayar ta ƙonawa.

27 Sa'an nan Ubangiji ya umarci mala'ikan, shi kuwa ya mai da takobinsa a kube.

28 Da Dawuda ya ga Ubangiji ya amsa masa a masussukar Arauna Bayebuse, sai ya miƙa hadaya a wurin.

29 Gama wurin zama na Ubangiji wanda Musa ya yi a jeji, da bagaden hadaya ta ƙonawa sun cikin masujada a Gibeyon.

30 Dawuda bai iya zuwa wurin don ya yi tambaya ga Allah ba, saboda yana jin tsoron takobin mala'ikan Ubangiji.

22

1 Sa'an nan sai Dawuda ya ce, “A nan Haikalin Ubangiji Allah zai kasance, da kuma bagaden ƙona hadaya domin Isra'ila.”

2 Dawuda kuwa ya umarta a tattaro dukan baƙin da suke a ƙasar Isra'ila. Ya sa waɗansu su farfasa duwatsu, su sassaƙe duwatsun domin ginin Haikalin Allah.

3 Dawuda kuma ya cika manyan ɗakunan ajiya da ƙarafa don yin ƙusoshi na ƙyamaren ƙofofi, da mahaɗai, ya kuma tara tagulla mai yawa wanda ta fi ƙarfin awo,

4 da katakan al'ul da ba a san adadinsu ba, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo wa Dawuda itacen al'ul mai ɗumbun yawa.

5 Dawuda kuwa ya ce, “Ɗana Sulemanu yaro ne, bai gogu da duniya ba. Ga shi, Haikalin da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, zai zama sananne mai daraja cikin dukan ƙasashe, saboda haka sai in tanada masa.” Domin haka Dawuda ya tara kayayyakin gini masu ɗumbun yawa kafin rasuwarsa.

6 Sai Dawuda ya kira Sulemanu ɗansa, ya yi masa wasiyyar gina Haikalin Ubangiji, Allah na Isra'ila.

7 Dawuda kuwa ya ce wa Sulemanu, “Ɗana, na ƙudura a zuciyata in gina Haikali saboda sunan Ubangiji Allah.

8 Amma Ubangiji ya ce mini, ‘Ka zubar da jini da yawa, ka yi manyan yaƙe-yaƙe, don haka ba za ka gina Haikali saboda sunana ba, gama a gabana ka zubar da jini mai yawa a duniya.

9 Za a haifa maka ɗa, zai zama mutumin salama. Zan kuwa ba shi zaman lafiya da abokan gāba da suke kewaye da shi, gama za a ce da shi Sulemanu, wato salama. Zan kawo wa Isra'ila salama, da natsuwa a zamaninsa.

10 Shi zai gina Haikali saboda sunana. Zai zama ɗana, ni kuwa zan zama uba a gare shi, zan kafa gadon sarautarsa a Isra'ila har abada.’

11 “To, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, domin ka yi nasara ka gina Haikalin Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya faɗa a kanka.

12 Ubangiji dai ya ba ka basira da haziƙanci domin sa'ad da ya sa ka ka lura da Isra'ila ka kiyaye dokokinsa.

13 Za ka arzuta idan ka kula ka kiyaye dokoki da ka'idodi da Ubangiji ya umarci Musa saboda Isra'ila. Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali. Kada ka ji tsoro, kada kuma ka karaya.

14 Da wahala mai yawa na yi tanadi domin Haikalin Ubangiji, zinariya wajen talanti dubu ɗari (100,000), da azurfa kuma wajen talanti zambar dubu (1,000,000), domin gina Haikalin Ubangiji. Bayan wannan akwai tagulla da ƙarfe masu tarin yawa. Na kuma tanada katakai da duwatsu. Kai kuma sai ka ƙara a kansu.

15 Kana da ma'aikata jingim, su masu fasa duwatsu, da magina, da masassaƙa, da gwanayen masu sana'o'i iri dabam dabam, masu yawan gaske.

16 Za su yi aiki da zinariya, da azurfa, da tagulla, da ƙarfe. Tashi, ka kama aiki, Ubangiji ya kasance tare da kai!”

17 Dawuda kuma ya umarci dukan shugabannin Isra'ila su taimaki ɗansa Sulemanu.

18 Ya ce, “Ubangiji Allahnku yana tare da ku, ya ba ku zaman lafiya a kowane sashi. Gama ya ba da mazaunan ƙasar a hannuna, an murƙushe ƙasar a gaban Ubangiji da jama'arsa.

19 Yanzu fa sai ku sa hankalinku da zuciyarku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku tashi, ku gina wa Ubangiji Allah tsattsarkan wuri domin a kawo akwatin alkawari na Ubangiji, da tsarkakakkun tasoshin Allah a cikin Haikalin da aka gina saboda sunan Ubangiji.”

23

1 Sa'ad da Dawuda ya tsufa, yana da shekaru da yawa, sai ya naɗa ɗansa Sulemanu ya zama Sarkin Isra'ila.

2 Dawuda kuwa ya tattara dukan shugabannin Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa.

3 Aka ƙidaya Lawiyawa maza tun daga mai shekara talatin har sama, jimillarsu dubu talatin da dubu takwas (38,000).

4 Sai Dawuda ya ce dubu ashirin da dubu huɗu (24,000) daga cikinsu za su yi hidimar Haikalin Ubangiji, dubu shida (6,000) kuma su zama manyan ma'aikata da alƙalai,

5 dubu huɗu (4,000) su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu (4,000) kuma za su zama masu raira yabbai ga Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda ya yi.

6 Dawuda kuwa ya kasa su kashi kashi bisa ga 'ya'yan Lawi maza, wato Gershon, da Kohat, da Merari.

7 'Ya'yan Gershon maza, su ne Libni da Shimai.

8 'Ya'yan Libni, maza, su ne Yehiyel, shi ne babba, da Zetam, da Yowel, su uku.

9 'Ya'yan Shimai, maza kuwa, su ne Shelomit, da Heziyel, da Haran, su uku. Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu, Libni.

10 'Ya'yan Shimai, maza, su ne Yahat, da Zaina, da Yewush, da Beriya. 'Ya'yan Shimai, maza, ke nan, su huɗu.

11 Yahat shi ne babba, Zaina shi ne na biyu, amma Yewush, da Beriya ba su da 'ya'ya da yawa, saboda haka ana lasafta su a haɗe gida ɗaya.

12 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel, su huɗu ke nan.

13 'Ya'yan Amram, maza, su ne Haruna, da Musa. Aka keɓe Haruna domin ya tsarkake abubuwa mafi tsarki, domin shi da 'ya'yansa za su ƙone turare a gaban Ubangiji, su yi masa hidima, su riƙa sa albarka da sunansa har abada.

14 Amma 'ya'yan Musa mutumin Allah, an lasafta su tare da kabilar Lawi.

15 'Ya'yan Musa, maza, ke nan, Gershom da Eliyezer.

16 Ɗan Gershom babba shi ne Shebuwel.

17 Ɗan Eliyezer shi ne Rehabiya, shugaba, shi Eliyezer ba shi da waɗansu 'ya'ya, amma Rehabiya yana da 'ya'ya da yawa.

18 Ɗan Izhara shi ne Shelomit, shugaba.

19 'Ya'yan Hebron, maza, su ne Yeriya, shi ne babba, da Amariya na biyu, da Yahaziyel na uku, da kuma Yekameyam na huɗu.

20 'Ya'yan Uzziyel, maza, su ne Mika, da Isshiya.

21 'Ya'yan Merari, su ne Mali da Mushi. 'Ya'yan Mali su ne Ele'azara da Kish.

22 Ele'azara kuwa ya rasu ba shi da 'ya'ya maza, sai 'yan mata kaɗai, sai 'yan'uwansu, 'ya'yan Kish, maza, suka aure su.

23 'Ya'yan Mushi, maza, su uku ne, wato Mali, da Eder, da Yerimot.

24 Waɗannan su ne 'ya'yan Lawi, maza, bisa ga gidajen kakanninsu, wato su ne shugabannin da aka rubuta sunayensu ɗaya ɗaya daga mai shekara ashirin da haihuwa zuwa sama. Su ne za su yi hidima a cikin Haikalin Ubangiji.

25 Gama Dawuda ya ce, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya hutar da jama'arsa, yana kuwa zama a Urushalima har abada.

26 Yanzu Lawiyawa ba za su riƙa ɗaukar alfarwar sujada tare da kayayyakin yin aiki a cikinta ba.”

27 Bisa ga maganar Dawuda ta ƙarshe aka ƙidaya 'ya'yan Lawiyawa, maza, daga mai shekara ashirin zuwa sama.

28 Aikinsu shi ne su taimaki 'ya'yan Haruna, maza, gudanar da aiki cikin Haikalin Ubangiji, wato lura da farfajiyoyi da ɗakuna, da tsabtace tsarkakan abubuwa, da yin taimako cikin kowace hidimar Haikalin Ubangiji.

29 Za su kuma taimaka wajen gurasar ajiyewa, da lallausan gari na hadaya ta gari, da waina marar yisti, da abin da akan toya, da abin da akan kwaɓa, da ma'aunan nauyi da na girma.

30 Za su kuma riƙa tsayawa kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Haka kuma za su riƙa yi da maraice,

31 da kuma lokacin miƙa wa Ubangiji hadayun ƙonawa a ranakun Asabar, da lokacin tsayawar amaryar wata, da lokacin ƙayyadaddun idodi, za su tsaya a gaban Ubangiji bisa ga yawansu da ake bukata.

32 Su ne za su riƙa lura da alfarwa ta sujada, da Wuri Mai Tsarki, za su kuma taimaki 'ya'yan Haruna, maza, 'yan'uwansu, da yin hidimar Haikalin Ubangiji.

24

1 Ga yadda 'ya'yan Haruna, maza, suka karkasu. 'Ya'yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.

2 Amma Nadab da Abihu sun riga mahaifinsu mutuwa, ba su kuma da 'ya'ya. Saboda haka Ele'azara da Itamar suka shiga aikin firistoci.

3 Sai Dawuda da Zadok daga zuriyar Ele'azara, da Ahimelek daga zuriyar Itamar suka karkasa su bisa ga ƙayyadaddun lokatansu na yin aiki.

4 Tun da yake akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Ele'azara fiye da zuriyar Itamar, sai suka karkasa su haka, shugabannin gidajen kakannin zuriyar Ele'azara mutum goma sha shida, na zuriyar Itamar kuwa su takwas, bisa ga gidajen kakanninsu.

5 Da haka aka karkasa su ta hanyar kuri'a gama akwai ma'aikatan Wuri Mai Tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Ele'azara da zuriyar Itamar.

6 Shemaiya, ɗan Netanel marubuci, Balawe, ya rubuta su a gaban sarki da shugabanni, da Zadok firist, da Ahimelek ɗan Abiyata, da shugabannin gidajen kakannin firistoci, da Lawiyawa. Aka ɗauki gida guda daga gidajen kakannin Ele'azara, aka kuma ɗauki ɗaya daga gidajen kakannin Itamar.

7 Ga yadda aka shirya ƙungiyoyin iyali ashirin da huɗu su sami aikinsu, 1) Yehoyarib, 2) Yedaiya, 3) Harim, 4) Seyorim, 5) Malkiya, 6) Mijamin, 7) Hakkoz, 8) Abaija, 9) Yeshuwa, 10) Shekaniya, 11) Eliyashib, 12) Yakim, 13) Huffa, 14) Yeshebeyab, 15) Bilga, 16) Immer, 17) Hezir, 18) Haffizzez, 19) Fetahiya, 20) Yehezkel, 21) Yakin, 22) Gamul, 23) Delaiya, 24) Ma'aziya.

8

9

10

11

12

13

14

15

16

17

18

19 Waɗannan suna da aikin da aka ba su na hidimar Haikalin Ubangiji bisa ga ka'idar da kakansu Haruna ya kafa musu, kamar yadda Ubangiji Allah na Isra'ila ya umarce shi.

20 Sauran 'ya'yan Lawi, maza, na wajen Amram, shi ne Shebuwel. Na wajen Shebuwel, shi ne Yedaiya.

21 Na wajen Rehabiya, shi ne Isshiya,

22 Na wajen Izhara, shi ne Shelomit, na wajen Shelomit, shi ne Yahat.

23 Na wajen Hebron, su ne Yeriya na fari, da Amariya, da Yahaziyel, da Yekameyam.

24 Na wajen Uzziyel, shi ne Mika, na wajen Mika, shi ne Shamir.

25 Ɗan'uwan Mika, shi ne Isshiya. Na wajen Isshiya, shi ne Zakariya.

26 Na wajen Merari, Mali da Mushi, da Yayaziya. Na wajen Yayaziya, shi ne Beno.

27 Na wajen Merari, wato na wajen Yayaziya, su ne Beno, da Shoham, da Zakkur, da Ibri.

28 Na wajen Mali, shi ne Ele'azara wanda ba shi da 'ya'ya maza.

29 Na wajen Kish, ɗan Kish, shi ne Yerameyel.

30 'Ya'yan Mushi, maza, su ne Mali, da Eder, da Yerimot. Waɗannan su ne 'ya'yan Lawiyawa, maza, bisa ga gidajen kakanninsu.

31 Su ma suka jefa kuri'a kamar yadda 'yan'uwansu, 'ya'yan Haruna, maza, suka yi a gaban sarki Dawuda, da Zadok, da Ahimelek, da shugabannin gidajen kakanni na firistoci da na Lawiyawa. Shugaban gidan kakanni ya jefa kuri'a daidai da ƙanensa.

25

1 Dawuda fa da shugabannin Lawiyawa suka zaɓi waɗansu daga cikin 'ya'yan Asaf, maza, da na Heman, da na Yedutun domin su raira waƙa da garayu, da molaye, da kuge. Ga waɗanda suka yi wannan hidima.

2 Daga cikin 'ya'yan Asaf, maza, Zakkur, da Yusufu, da Netaniya, da Asharela, Asaf mahaifinsu ne yake bi da su, shi ne kuma mawaƙin sarki.

3 Na wajen Yedutun, su ne 'ya'yan Yedutun, maza, wato Gedaliya, da Zeri, da Yeshaya, da Shimai, da Hashabiya, da Mattitiya, su shida ne. Mahaifinsu Yedutun shi ne yake bi da su, shi ne kuma mai raira waƙoƙi da garaya domin godiya da yabon Ubangiji.

4 Na wajen Heman, su ne 'ya'yan Heman, maza, wato Bukkiya, da Mattaniya, da Uzziyel, da Shebuwel, da Yerimot, da Hananiya, da Hanani, da Eliyata, da Giddalti, da Romamti-yezer, da Yoshbekasha, da Malloti, da Hotir, da Mahaziyot.

5 Allah ya ba Heman, wato annabin sarki, 'ya'ya maza su goma sha huɗu, da 'ya'ya mata su uku, kamar yadda ya yi alkawari, domin ya ba Heman iko.

6 Dukansu tsohonsu ne yake bi da su da raira waƙoƙi, da kaɗa kuge, da molaye da garayu, cikin Haikalin Ubangiji, domin yin sujada. Asaf, da Yedutun, da Heman suna ƙarƙashin umarnin sarki.

7 Jimillar horarrun mawaƙa don raira waƙa ga Ubangiji, su da 'yan'uwansu, duka waɗanda suke ƙwararru, su ɗari biyu da tamanin da takwas ne.

8 Sai suka jefa kuri'a domin su ba kowa aikin da zai yi, yaro da babba, malami da almajiri.

9 Waɗannan su ne shugabannin ƙungiyoyi ashirin da huɗu, na goma sha biyu biyu, bisa ga yadda aka tsara su ga aikin. 1) Yusufu daga iyalin Asaf, 2) Gedaliya, 3) Zakkur, 4) Zeri, 5) Netaniya, 6) Bukkiya, 7) Asharela, 8) Yeshaya, 9) Mattaniya, 10) Shimai, 11) Uzziyel, 12) Hashabiya, 13) Shebuwel, 14) Mattitiya, 15) Yeremot, 16) Hananiya, 17) Yoshbekasha, 18) Hanani, 19) Malloti, 20) Eliyata, 21) Hotir, 22) Giddalti, 23) Mahaziyot, 24) Romamtiyezer.

26

1 Ƙungiyoyin masu tsaron ƙofofi ke nan. Na wajen Kora shi ne Shallum ɗan Kore, daga cikin iyalin Ebiyasaf.

2 Shallum kuwa yana da 'ya'ya maza, su ne Zakariya, da Yediyayel, da Zabadiya, da Yatniyel,

3 da Elam, da Yehohanan, da Eliyehoyenai, su bakwai ke nan.

4 Obed-edom kuma Allah ya ba shi 'ya'ya maza, su ne Shemaiya, da Yehozabad, da Yowa, da Sakar, da Netanel,

5 da Ammiyel, da Issaka, da Fauletai, da su Allah ya sa masa albarka.

6 Ɗan farin Obed-edom, wato Shemaiya ya haifi 'ya'ya maza waɗanda suka yi shugabanci a gidan kakansu, gama su jarumawa ne.

7 'Ya'yan Shemaiya, su ne Otni, da Refayel, da Obida, da Elzabad, waɗanda 'yan'uwansu, Elihu, da Semakiya jarumawa ne.

8 Waɗannan duka iyalin Obed-edom ne. Su da 'ya'yansu maza da 'yan'uwansu suna da ƙarfi da gwaninta na yin aiki. Su sittin da biyu ne daga wajen Obed-edom.

9 Shallum yana da 'ya'ya maza da 'yan'uwa, su goma sha takwas jarumawa.

10 Hosa kuma na wajen 'ya'yan Merari, maza, yana da 'ya'ya maza, Shimri shi ne babba, ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, duk da haka mahaifinsa ya maishe shi babba.

11 Hilkiya shi ne na biyu, da Tebaliya na uku, da Zakariya na huɗu. Dukan 'ya'yan Hosa, maza, da 'yan'uwansa, su goma sha uku ne.

12 Aka rarraba masu tsaron Haikali ƙungiya ƙungiya, bisa ga iyali, aka raba musu ayyuka a Haikali kamar dai sauran Lawiyawa.

13 Sai suka jefa kuri'a bisa ga gidajen kakanninsu, ba a damu da yawan jama'a a iyali ba, a kan kowace ƙofar.

14 Kuri'a ta ƙofar gabas ta faɗo a kan Shallum. Sai aka jefa kuri'a don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma'ana, sai kuri'a ta ƙofar arewa ta faɗo a kansa.

15 Kuri'a ta ƙofar kudu ta faɗo a kan Obed-edom. Aka sa 'ya'yansa maza su lura da ɗakunan ajiya.

16 Kuri'a ta ƙofar yamma kusa da Ƙofar Shalleket, a kan hanyar da ta haura, ta faɗo a kan Shuffim da Hosa. Aka raba aikin tsaro bisa ga lokatan da aka tsara bi da bi.

17 A kowace rana Lawiyawa shida suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.

18 A ɗan ɗakin da take wajen yamma, akwai masu tsaro huɗu a hanyar, biyu kuma a ɗan ɗakin.

19 Waɗannan su ne ƙungiyoyin masu tsaron ƙofofi daga zuriyar Kora da ta Merari.

20 Sauran Lawiyawa, 'yan'uwansu kuwa, suke lura da baitulmalin Haikalin Allah, da ɗakin ajiyar kayan da aka keɓe ga Allah.

21 Libni daga cikin iyalin Gershon, shi ne kakan ƙungiyoyin iyali da dama, iyalin Yehiyel ne ɗaya daga cikinsu.

22 Biyu daga cikin wannan iyali, wato Zetam da Yowel, suke lura da baitulmalin Haikali da ɗakin ajiyar kaya.

23 Aka raba aiki kuma ga zuriyar Amram, da ta Izhara, da ta Hebron, da kuma ta Uzziyel.

24 Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami'in baitulmalin.

25 Ta wurin ɗan'uwan Gershom, wato Eliyezer ya sami dangantaka da Shelomit. Eliyezer shi ne mahaifin Rehabiya, wanda ya haifi Yeshaya, uban Yoram, da Zikri, da Shelomit.

26 Shi wannan Shelomit da 'yan'uwansa suke lura da kyautai waɗanda sarki Dawuda, da shugabannin, gidajen kakanni, da shugabannin dubu dubu, da na ɗari ɗari, da shugabannin sojoji suka keɓe ga Allah.

27 Daga cikin ganimar yaƙi suka keɓe wani sashi domin gyaran Haikalin Ubangiji.

28 Dukan kuma abin da Sama'ila annabi, da Saul ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruya, suka keɓe an sa su a hannun Shelomit da 'yan'uwansa.

29 Kenaniya da 'ya'yansa maza na wajen Izhara su ne aka danƙa wa al'amuran sasantawa na Isra'ilawa, wato sun zama shugabanni da alƙalai.

30 Hashabiya da 'yan'uwansu, su dubu da ɗari bakwai (1,700), gwanaye ne, daga zuriyar Hebron, su ne suke lura da Isra'ilawan yamma da Urdun a kan aikin Ubangiji da na sarki.

31 Yeriya shi ne shugaban zuriyar Hebron bisa ga asalinsu. A shekara ta arba'in ta sarautar Dawuda, sai aka bincika, aka tarar akwai ƙarfafan mutane, jarumawa a cikinsu, a Yazar ta Gileyad.

32 Sarki Dawuda ya sa shi, shi da 'yan'uwansu su dubu biyu da ɗari bakwai (2,700) gwanaye, waɗanda suke shugabancin gidajen kakanni, su lura da kabilar Ra'ubainu, da ta Gad, da rabin kabilar Manassa a kan dukan ayyukan Allah da na sarki.

27

1 Ga lissafin kawunan iyalin Isra'ilawa, da shugabannin dangi, da jama'a masu gudanar da ayyukan mulki. A kowane wata akan sauya aikin ƙungiyar mutum dubu ashirin da dubu huɗu (24,000), a ƙarƙashin shugaban aiki na wannan wata. Kowane wata akan sauya, wata ƙungiya ta kama aiki.

2 Waɗannan su ne shugabanni don kowane wata. Wata na 1, Yashobeyam, ɗan Zabdiyel. (Shi daga dangin Feresa na kabilar Yahuza ne.) Wata na 2, Dodai, ɗan Ahowa. (Miklot yake bi masa a shugabancin.) Wata na 3, Benaiya, ɗan Yehoyada firist. Shugaba ne daga cikin sanannun nan “talatin.” (Ɗansa Ammizzabad ya gāje shi a shugabancin ƙungiya.) Wata na 4, Asahel, ƙanen Yowab. (Ɗansa Zabadiya ya gāje shi.) Wata na 5, Shimeya, daga zuriyar Izhara. Wata na 6, Aira, ɗan Ikkesha, daga Tekowa. Wata na 7, Helez, mutumin Ifraimu, daga Felet. Wata na 8, Sibbekai, daga garin Husha. (Shi daga dangin Zera ne, na kabilar Yahuza.) Wata na 9, Abiyezer, daga Anatot na kabilar Biliyaminu. Wata na 10, Maharai, daga Netofa. (Shi ma daga dangin Zera ya fito.) Wata na 11, Benaiya, daga Firaton na kabilar Ifraimu. Wata na 12, Heled, daga Netofa. (Shi daga zuriyar Otniyel ne.)

3 Ga jerin sunayen masu mulkin kabilan Isra'ila. Ra'ubainu: Eliyezer ɗan Zikri, Saminu: Shefatiya ɗan Ma'aka, Lawi: Hashabiya ɗan Kemuwel, Haruna: Zadok, Yahuza: Eliyab ɗaya daga cikin 'yan'uwan sarki Dawuda, Issaka: Omri ɗan Maikel, Zabaluna: Ishmaiya ɗan Obadiya, Naftali: Yerimot ɗan Azriyel, Ifraimu: Hosheya ɗan Azaziya, Manassa ta Yamma: Yowel ɗan Fedaiya, Manassa ta Gabas: Iddo ɗan Zakariya, Biliyaminu: Yawasiyel ɗan Abner, Dan: Azarel ɗan Yeroham. Waɗannan su ne shugabannin kabilai.

4 Sarki Dawuda bai ƙidaya waɗanda shekarunsu suka kasa ashirin ba, gama Ubangiji ya yi alkawari zai sa mutanen Isra'ila su yi yawa kamar taurari a sararin sama.

5 Yowab ɗan Zeruya ne ya fara ƙidayar, amma bai gama ba. Allah ya hukunta wa Isra'ila saboda wannan ƙidaya, saboda haka ba za a taɓa samun cikakken adadi a lissafin da suke a ajiye na fādawan sarki Dawuda ba.

6 Ga lissafin masu sarrafa dukiyar sarki. Ɗakin ajiya na sarki: Azmawet ɗan Adiyel, Ƙaramin ɗakin ajiya: Jonatan ɗan Uzziya, Aikin gona: Ezri ɗan Kabilu, Kurangar Inabi: Shimai daga Rama, Ɗakin ajiyar Inabi: Zabdi daga Shefam, Itatuwan zaitun da na ɓaure (a gindin tsaunukan yamma): Ba'al-hanan daga Geder, Ajiyar man zaitun: Yowash, Garken shanu na filin Sharon: Shirtai daga Sharon, Garken shanu na cikin kwari: Shafat ɗan Adlai, Raƙuma: Obil Ba'isma'ile, Jakuna: Yedaiya daga Meronot, Tumaki: Yaziz Bahagire.

7 Dukan waɗannan su ne masu lura da dukiyar sarki Dawuda.

8 Jonatan, kawun Dawuda, shi ne mai ba da shawara, yana da ganewa, shi kuma magatakarda ne. Shi da Yehiyel ɗan Hakmoni su ne masu koya wa 'ya'yan sarki, maza.

9 Ahitofel shi abokin shawarar sarki ne. Hushai Ba'arkite kuwa shi ne abokin sarki.

10 Sai Yehoyada ɗan Benaiya, da Abiyata suka gāji matsayin Ahitofel. Yowab shi ne babban shugaban sojojin sarki.

28

1 Dawuda ya yi umarni a tara dukan shugabannin Isra'ila, da shugabannin kabilai, da shugabannin ƙungiyoyin da suke bauta wa sarki, da shugabannin dubu dubu, da na ɗari ɗari, da masu lura da dukan dukiya da dabbobin sarki, da na 'ya'yansa, da fādawa, da manyan sojoji, da jarumawa, a Urushalima.

2 Sarki Dawuda fa ya miƙe tsaye, ya ce, “Ku saurare ni, ku 'yan'uwana, da jama'ata. Na yi niyya a zuciyata in gina wa akwatin alkawari na Ubangiji wurin hutawa, da wurin zaman zatin Allah. Na riga na yi shiri domin ginin,

3 amma Allah bai yardar mini in yi da kaina ba, domin ni mayaƙi ne, na kuwa zubar da jini.

4 Duk da haka Ubangiji Allah na Isra'ila ya zaɓe ni da zuriyata daga cikin gidan mahaifina, in zama Sarkin Isra'ilawa har abada. Gama shi ya zaɓi Yahuza ya zama shugaba. Daga cikin gidan Yahuza kakana, da kuma daga cikin 'ya'yan mahaifina, maza, ya ji daɗina har ya naɗa ni sarkin dukan Isra'ila.

5 Daga cikin dukan 'ya'yana maza, (gama Ubangiji ya ba ni 'ya'ya maza da yawa), ya zaɓi ɗana Sulemanu ya hau gadon sarautar Isra'ila, abin mulkin Ubangiji.

6 “Ya ce mini, ‘Ɗanka Sulemanu ne zai gina Haikalina da shirayuna, gama na zaɓe shi ya zama ɗa a gare ni, ni kuwa in zama uba a gare shi.

7 Zan tabbatar da mulkinsa har abada idan ya bi umarnaina da ka'idodina da himma kamar yadda ake yi a yau.’

8 “Saboda haka a gaban dukan Isra'ila, wato taron jama'ar Ubangiji, da kuma gaban Allahnmu, sai ku kiyaye, ku bi dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki ƙasan nan mai kyau, ku kuma bar wa 'ya'yanku ita gādo har abada.

9 “Kai kuwa ɗana Sulemanu, sai ka san Allah na tsohonka, ka bauta masa da zuciya ɗaya, da kuma yardar rai, gama Ubangiji mai binciken dukan zukata ne, ya kuma san kowane irin nufi da tunani. Idan ka neme shi, za ka same shi, in kuwa ka rabu da shi, shi ma zai yi watsi da kai har abada.

10 Ka lura, gama Ubangiji ya zaɓe ka domin ka gina Haikali, wato Wuri Mai Tsarki. Ka yi ƙarfi, ka kama aiki.”

11 Sa'an nan Dawuda ya ba ɗansa Sulemanu tsarin shirayin Haikalin, da ɗakunansa, da ɗakunan ajiya, da benaye, da Wuri Mafi Tsarki, inda ake gafarta zunubi.

12 Ya kuma ba shi tsarin dukan abin da ya yi nufin yi, na filayen Haikalin Ubangiji da dukan ɗakuna na kewaye, da ɗakunan ajiya na Haikalin Allah, da ɗakunan ajiye kyautan da aka keɓe ga Ubangiji.

13 Ya kuma ba shi tsarin ƙungiyoyin firistoci da na Lawiyawa, da na dukan hidimar da za a yi a Haikalin Ubangiji, da aikin lura da kayayyakin aiki na cikin Haikalin Ubangiji.

14 Ya kuma faɗa wa Sulemanu yawan zinariya da za a yi kwanoni da ita don yin aiki, da yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita don yin aiki,

15 da yawan zinariya da za a yi alkukan fitilu, da kuma fitilun, da yawan zinariya da za a yi kowane alkuki da fitilunsa, da yawan azurfa da za a yi alkuki bisa ga yadda za a yi amfani da kowane alkuki,

16 da yawan zinariya da za a yi teburorin gurasar ajiyewa, da azurfar da za a yi teburorin azurfa,

17 da yawan zinariya tsantsa wadda za a yi cokula masu yatsotsi, da daruna, da finjalai, da kwanoni da ita, da yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita,

18 da yawan zinariya tsantsa wadda za a yi bagaden ƙona turare da ita. Ya kuma ba shi tsarin zinariya ta kerubobin da za su miƙe fikafikansu su rufe akwatin alkawari na Ubangiji.

19 Sarki Dawuda ya ce, “Dukan wannan rubutacce ne daga wurin Ubangiji zuwa gare ni domin in fahimci fasalin aikin filla filla.”

20 Sarki Dawuda kuma ya ce wa ɗansa Sulemanu, “Ka yi ƙarfin hali, ka dāge sosai, ka kama aikin, kada ka ji tsoro, kada kuwa ka karai, gama Ubangiji Allah, wato Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ba, ba kuwa zai rabu da kai ba, har ka gama dukan aikin Haikalin.

21 Ga dai ƙungiyoyin firistoci da na Lawiyawa, suna nan domin yin hidima a Haikalin Allah, ga kuma gwanaye na kowace irin sana'a suna tare da kai don yin kowane irin aiki. Shugabanni da dukan jama'a suna ƙarƙashinka duka.”

29

1 Sarki Dawuda fa ya yi magana da dukan taron, ya ce, “Ga shi, ɗana Sulemanu, wanda Allah ya zaɓa, shi dai saurayi ne tukuna, bai gogu da duniya ba tukuna, aikin kuwa babba ne, gama Haikali ba na mutum ba ne, amma na Ubangiji Allah ne.

2 A halin yanzu dai na riga na yi iyakacin ƙoƙarina, har na tanada waɗannan abubuwa saboda Haikalin Allahna, wato zinariya saboda kayayyakin zinariya, azurfa saboda kayayyakin azurfa, tagulla saboda kayayyakin tagulla, baƙin ƙarfe saboda kayayyakin baƙin ƙarfe, itace kuwa saboda kayayyakin itace, da duwatsu da yawa masu daraja, da masu launi iri iri.

3 Saboda kuma ƙaunar Haikalin Allahna da nake yi, shi ya sa na ba da zinariyata da azurfata domin Haikalin Allahna, banda wanda na riga na tanada saboda Haikali mai tsarki.

4 Na ba da zinariya tsantsa, talanti dubu uku (3,000), da azurfa tsantsa, talanti dubu bakwai (7,000), domin yin ado a bangon Haikalin,

5 da kuma dukan kayayyakin da masu sana'a za su yi. Yanzu fa ko akwai mai niyyar ba da sadaka ta yardar rai ga Ubangiji?”

6 Sa'an nan shugabannin gidajen kakanni, da shugabannin kabilai, da shugabanni na dubu dubu, da na ɗari ɗari, da masu lura da aikin sarki, suka bayar da yardar rai.

7 Sun ba da zinariya talanti dubu biyar (5,000), da darik dubu goma (10,000), da azurfa talanti dubu goma (10,000), da tagulla talanti goma sha takwas (18,000), da ƙarfe talanti dubu ɗari (100,000).

8 Dukan waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka bayar da su cikin taskar Haikalin Ubangiji, ta hannun Yehiyel Bagershone.

9 Sai jama'a suka yi murna da ganin yadda suka bayar hannu sake, gama sun kawo sadakokinsu a gaban Ubangiji da zuciya ɗaya, shi sarki Dawuda kuma ya yi murna ƙwarai.

10 Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanmu Yakubu, yabo ya tabbata gare ka har abada abadin!

11 Girma, da iko, da daraja, da nasara, da ɗaukaka duk naka ne, ya Ubangiji, gama dukan abin da yake cikin sammai da duniya naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji. Kai ne Maɗaukaki duka.

12 Dukan wadata da girma daga gare ka suke, kai kake mulki da dukan iko da ƙarfi. Kai ne kake da iko ka ba mutum iko da ƙarfi.

13 Yanzu ya Allahnmu, muna gode maka muna kuma yabon sunanka mai daraja.

14 “Amma wane ni ko kuma jama'ata, da za mu iya kawo sadaka mai yawa haka? Gama dukan kome daga gare ka yake. Daga cikin abin da muka karɓa daga wurinka muka ba ka.

15 Gama mu kamar baƙi ne, masu yawo a gabanka kamar kakanninmu. Kwanakinmu a duniya kamar inuwa ne, ba za mu tsere wa mutuwa ba.

16 Ya Ubangiji Allahnmu, duk wannan da muka kawo domin mu gina maka Haikali saboda sunanka mai tsarki, daga gare ka ne muka samu, duka naka ne.

17 Da yake na sani, ya Allahna, kakan gwada zuciya, kana ƙaunar gaskiya, bisa ga amincewar zuciyata, da yardar rai, na miƙa maka dukan waɗannan abubuwa. Ina murna da ganin jama'arka waɗanda suke nan a tattare, sun kawo maka sadakokinsu da yardar rai.

18 Ya Ubangiji, Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, kakanninmu, ka tabbatar da yardar rai ɗin nan a rayukan jama'arka, ka bi da zukatansu zuwa gare ka.

19 Ka kuma ba ɗana Sulemanu cikakkiyar zuciya, har da zai kiyaye umarnanka, da shaidunka, da dokokinka, domin ya aikata su duka, ya kuma gina Haikali wanda na riga na yi tanadi dominsa.”

20 Sa'an nan Dawuda ya ce wa taro duka, “Sai ku yabi Ubangiji Allahnku yanzu.” Taron jama'a kuwa suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu, suka rusuna har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada, suka kuma girmama sarki.

21 Kashegari sai suka miƙa wa Ubangiji hadayu, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji, bijimai dubu ɗaya (1,000), da raguna dubu ɗaya (1,000), da 'yan raguna dubu ɗaya (1,000), da hadayunsu na sha, da hadayu masu yawa domin Isra'ila duka.

22 Sai suka ci, suka sha, suka yi murna a gaban Ubangiji a wannan rana. Sai suka sake shelar naɗin Sulemanu ɗan Dawuda sarki, a karo na biyu, suka shafa masa man keɓewa domin ya zama mai mulki na Ubangiji, Zadok kuwa shi ne firist.

23 Sai Sulemanu ya zauna a kan gādon sarauta na Ubangiji maimakon tsohonsa Dawuda. Ya yi nasara a cikin sarautar, Isra'ilawa dukansu suka yi masa biyayya.

24 Dukan ma'aikatan hukuma kuwa, da manyan mutane, da kuma dukan 'ya'yan sarki Dawuda, suka yi alkawari za su yi wa sarki Sulemanu biyayya.

25 Ubangiji kuwa ya ɗaukaka Sulemanu ƙwarai da gaske a gaban dukan Isra'ilawa, ya ɗaukaka sarautarsa fiye da ta waɗanda suka riga shi sarauta a Isra'ila.

26 Dawuda ɗan Yesse ya yi mulki bisa dukan Isra'ila,

27 har shekara arba'in. Ya yi mulki a Hebron shekara bakwai sa'an nan ya yi mulki shekara talatin da uku a Urushalima.

28 Sa'an nan ya rasu da kyakkyawan tsufa, cike da shekaru, da arziki, da daraja. Ɗansa Sulemanu kuma ya gāji sarautarsa.

29 An fa rubuta ayyukan sarki Dawuda daga farko har ƙarshe a tarihin Sama'ila, annabi, da na annabi Natan, da na annabi Gad.

30 An rubuta labarin mulkinsa, da ikonsa, da al'amuran da suka same shi, da Isra'ilawa, da dukan mulkokin ƙasashe na kewaye.